Gwamnatin tarayya ta rattaba hannu kan wata yarjejeniya ta Yuro miliyan 20 da gwamnatin Jamus a bangaren inganta harkokin sabon tsarin makamashi a kasar da kuma inganta ci gaban makamashin da ake sabuntawa.
A cewar wata sanarwa da ma’aikatar kasafin kudi da tsare-tsaren tattalin arziki ta fitar a ranar Alhamis, an gudanar da yarjejeniyar ne a karkashin shirin bankin raya kasa na KfW da kuma asusun kalubalen kasuwanci na Afirka.
- Gwamnatin Tarayya Ta Gurfanar Da Natasha A Kotu Kan Zargin Ɓata Sunan Akpabio Da Yahaya Bello
- Tinubu Ya Kai Ziyara Benuwe Sakamakon Kisan Kiyashi Da Aka Yi Wa Jama’a
A cewar sanarwar, “Gwamnatin tarayyar Nijeriya ta sanya hannu kan wata yarjejeniyar aiki akan Yuro miliyan 20 tare da gwamnatin Jamus kan batun samar da makamashi don tallafawa ci gaban yanayi a Nijeriya.
“Za a sauƙaƙe hakan ne ta hanyar Bankin Raya kasa na KfW da Asusun Kalubalan Kasuwancin Afirka.”
An gudanar da bikin sanya hannun ne a ofishin ministan kasafin kudi da tsare-tsaren tattalin arziki, Abubakar Bagudu, wanda ya wakilci Nijeriya.
Sakatare na farko kuma shugaban hadin gwiwar raya kasa a ofishin jakadancin Jamus a Nijeriya, Dr Karin Jansen, da wakilin bankin raya kasa na KfW, Gerald Keuhnemund, duk sun halarci rattaba hannun.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp