• English
  • Business News
Saturday, September 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Ta Amince Da Karin Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyon 2.1

by Sulaiman
2 years ago
in Labarai
0
Gwamnatin tarayya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin tarayya ta amince da karin kasafin kudin da ya kai Naira tiriliyan 2.1.

Ministan Kasafin Kudi da tsare-tsaren Tattalin Arziki, Atiku Bagudu ne ya bayyana hakan ga manema labarai a fadar shugaban kasa a ranar Litinin bayan kammala taron majalisar zartarwa ta tarayya da shugaba Bola Tinubu ya jagoranta a fadar shugaban kasa.

  • Shirin Blue Circle Na Kasar Sin Ya Samu Lambar Yabo Ta Kare Muhalli Daga MDD
  • Ku Bayar Da Yaranku A Yi Musu Allurar Ragafin HPV Domin Ba Ta Illa Ko Kadan -Mansura Isa

Bagudu ya bayyana cewa, “Mun gabatar da wani karin kasafin kudi inda majalisar ta amince da karin Naira tiriliyan 2 da biliyan 176 da miliyan 791, da dubu 286 cikin kasafin kudin da aka gabatar.”

A cewarsa, karin kasafin kudin an yi shi ne don magance matsalolin da suka kunno kai, ciki har da ware biliyan 605 don harkokin tsaro domin ci gaba da samun nasarar da aka samu a baya.

Bagudu ya ce, an ware biliyan 300 domin gyaran gadoji, gine-gine sannan kuma an ware biliyan 200 don harkokin noma.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki

Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

Ya kara da cewa, an samar da karin biliyan 210 don biyan karin albashi da gwamnatin ta cimma matsaya kan tattaunawarta da kungiyoyin kwadago, wanda za a fara biya daga watan Satumba zuwa Disamba 2023.

 

Bagudu ya bayyana cewa, an ware biliyan 400 domin biyan kudaden musayar kudi, inda ya nuna cewa gwamnatin tarayya ta samu dala biliyan 800 daga bankin duniya na tsawon watanni biyu, kamar yadda shugaban kasa ya amince da a sanya a cikin kasafin kudin.

Ministan ya bayyana cewa, an amince da kudi har biliyan 100 don tallafawa babban birnin tarayya Abuja, domin gudanar da ayyuka na gaggawa yayin da aka ware biliyan 18 ga hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) domin gudanar da zabe a Bayelsa da kuma Jihar Imo.

Ya ce, an ware karin biliyan 5.5 domin gudanar da ayyukan kaddamar da rancen kudi ga dalibai, kuma an ware biliyan 800 domin shirye-shiryen kafa sabuwar ma’aikata.

Yarjejeniyar da aka cimma da kungiyoyin kwadago na karin albashi har na tsawon watanni shida na nan daram bata canja ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Gwamnatin TinubuKasafin Kudin 2023Rancen kudin karatu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Shirin Blue Circle Na Kasar Sin Ya Samu Lambar Yabo Ta Kare Muhalli Daga MDD

Next Post

Karairayewar Darajar Naira: CBN Ya Ce Ba Shi Da Laifi, Ya Nemi A Kori Ƙarar Falana A Kotu

Related

Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki

38 minutes ago
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina
Manyan Labarai

Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

3 hours ago
Gwamnatin Tarayya Za Ta Inganta Muhimman Abubuwan More Rayuwa Don Ci Gaban Ƙasa
Labarai

Gwamnatin Tarayya Za Ta Inganta Muhimman Abubuwan More Rayuwa Don Ci Gaban Ƙasa

4 hours ago
Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutum Uku A Zariya
Labarai

Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutum Uku A Zariya

5 hours ago
Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido
Labarai

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido Ba

6 hours ago
Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya
Labarai

Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

17 hours ago
Next Post
Karairayewar Darajar Naira: CBN Ya Ce Ba Shi Da Laifi, Ya Nemi A Kori Ƙarar Falana A Kotu

Karairayewar Darajar Naira: CBN Ya Ce Ba Shi Da Laifi, Ya Nemi A Kori Ƙarar Falana A Kotu

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki

Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki

September 13, 2025
PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya

PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya

September 13, 2025
Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

September 13, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

September 13, 2025
Gwamnatin Tarayya Za Ta Inganta Muhimman Abubuwan More Rayuwa Don Ci Gaban Ƙasa

Gwamnatin Tarayya Za Ta Inganta Muhimman Abubuwan More Rayuwa Don Ci Gaban Ƙasa

September 13, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutum Uku A Zariya

Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutum Uku A Zariya

September 13, 2025
Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido Ba

September 13, 2025
Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

September 12, 2025
Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

September 12, 2025
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

September 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.