ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Ta Amince Da Karin Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyon 2.1

by Sulaiman
3 years ago
Gwamnatin tarayya

Gwamnatin tarayya ta amince da karin kasafin kudin da ya kai Naira tiriliyan 2.1.

Ministan Kasafin Kudi da tsare-tsaren Tattalin Arziki, Atiku Bagudu ne ya bayyana hakan ga manema labarai a fadar shugaban kasa a ranar Litinin bayan kammala taron majalisar zartarwa ta tarayya da shugaba Bola Tinubu ya jagoranta a fadar shugaban kasa.

  • Shirin Blue Circle Na Kasar Sin Ya Samu Lambar Yabo Ta Kare Muhalli Daga MDD
  • Ku Bayar Da Yaranku A Yi Musu Allurar Ragafin HPV Domin Ba Ta Illa Ko Kadan -Mansura Isa

Bagudu ya bayyana cewa, “Mun gabatar da wani karin kasafin kudi inda majalisar ta amince da karin Naira tiriliyan 2 da biliyan 176 da miliyan 791, da dubu 286 cikin kasafin kudin da aka gabatar.”

ADVERTISEMENT

A cewarsa, karin kasafin kudin an yi shi ne don magance matsalolin da suka kunno kai, ciki har da ware biliyan 605 don harkokin tsaro domin ci gaba da samun nasarar da aka samu a baya.

Bagudu ya ce, an ware biliyan 300 domin gyaran gadoji, gine-gine sannan kuma an ware biliyan 200 don harkokin noma.

LABARAI MASU NASABA

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Ya kara da cewa, an samar da karin biliyan 210 don biyan karin albashi da gwamnatin ta cimma matsaya kan tattaunawarta da kungiyoyin kwadago, wanda za a fara biya daga watan Satumba zuwa Disamba 2023.

 

Bagudu ya bayyana cewa, an ware biliyan 400 domin biyan kudaden musayar kudi, inda ya nuna cewa gwamnatin tarayya ta samu dala biliyan 800 daga bankin duniya na tsawon watanni biyu, kamar yadda shugaban kasa ya amince da a sanya a cikin kasafin kudin.

Ministan ya bayyana cewa, an amince da kudi har biliyan 100 don tallafawa babban birnin tarayya Abuja, domin gudanar da ayyuka na gaggawa yayin da aka ware biliyan 18 ga hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) domin gudanar da zabe a Bayelsa da kuma Jihar Imo.

Ya ce, an ware karin biliyan 5.5 domin gudanar da ayyukan kaddamar da rancen kudi ga dalibai, kuma an ware biliyan 800 domin shirye-shiryen kafa sabuwar ma’aikata.

Yarjejeniyar da aka cimma da kungiyoyin kwadago na karin albashi har na tsawon watanni shida na nan daram bata canja ba.

Gwamnatin tarayya
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya
  • Sulaiman
    Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari
  • Sulaiman
    Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana
  • Sulaiman
    Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

MASU ALAKA

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF
Rahotonni

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin
Rahotonni

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026
Labarai

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
Next Post
Karairayewar Darajar Naira: CBN Ya Ce Ba Shi Da Laifi, Ya Nemi A Kori Ƙarar Falana A Kotu

Karairayewar Darajar Naira: CBN Ya Ce Ba Shi Da Laifi, Ya Nemi A Kori Ƙarar Falana A Kotu

LABARAI MASU NASABA

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

June 13, 2026
Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.