Gwamnatin tarayya ta ce tsare-tsaren da sauye-sauyenta sun yi nisa kan harkokin karyar da farashin kayayyakin abinci da zimmar tabbatar da wadatar kasa da abinci, sauki da rahusa kuma al’ummar kasar na samu ta kowani bangare.
Ministan albarkatun noma da wadata kasa da abinci, Sanata Abubakar Kyari, shi ne ya shaida hakan a hirarsa da ‘yan jarida a Maiduguri.
- Matsin Rayuwa: ‘Yan Nijeriya Sun Rage Zuwa Kasashen Waje
- Ƴansanda Sun Kama Shahararren Ɗan Damfarar Yanar Gizo A Bauchi
Kyari ya bayyana himmar da gwamnati ke ci gaba da yi a bangaren noma domin ta dakile matsalar karancin abinci ne da kuma farfado da tattalin arziki.
Ya ce ma’aikatarsa ta yi amfani da dabaru daban-daban domin tunkarar kalubale kamar rashin tsaro, ambaliya, da dogaro da shigo da kayayyaki, musamman a wuraren da ke da matukar muhimmanci kamar noman alkama da shinkafa.
“A wani bangare na kokarin rage sama da tan miliyan shida na alkama da ake shigowa da su duk shekara, mun kaddamar da shirin noman alkama na kasa,” in ji Kyari.
Ya ce Jihar Kurus Ribas ita ce ta farko a yankin kudu da ta shiga a dama da ita a harkar noman alkama, lamarin da ke nuni da gayar nasara wajen samar da abinci a kowani sassa na kasar nan.
Kyari ya kara da cewa shirin rabar da takin zamani ya taimaka wajen bunkasa samar da shinkafa zuwa tan 58,000, lamarin da ya bai wa gwamnatin tarayya sanya tallafi a bangaren rabar da shinkafa ga jihohin da ambaliyar ruwa ta shafa.
Ministan ya ce akwai bukatar kare masu amfani da kuma kayan da ake nomawa, “kaso 80 cikin 100 na abincinmu manoman cikin gida ne suka samar da su.”
A daidai gabar da ake hasashen adadin ‘yan Nijeriya zai kai miliyan 400 a nan da shekarar 2050, Kyari ya ce gwamnati ta dukufa wajen kyautata harkar noma da kuma samar wa matasa ayyukan yi a matsayin mataki mai dogon zango na samar da wadatar abincin.
Ya ce gwamnati na kuma kokarin gyara kadarorin da kasar ke da su kamar su taraktoci, da sauran muhimman kayan aiki domin kara bunkasa samar da abinci.
Ya kuma ce Nijeriya ta yi hadin gwiwa da kasar Belarus don samar da ayyukan hadaka da nufin kara yawan kayan da ake fitarwa.
Ministan ya yi gargadin cewa a guji amfani da injinan noma da gwamnati ta samar ba ta hanyoyin da suka dace ba, inda ya bukaci manoma da su yi amfani da irin wadannan kayan aikin yadda ya kamata.
Ministan ya ce warare uku na ajiyar kaya wato silo ne kawai suke aiki a halin yanzu, inda ya sha alwashin cewa za a maida hankali wajen gyara sauran.
Kyari ya ce “Ma’aikatar noma da dawata kasa da abinci za ta hada kai da masu ruwa da tsaki don tabbatar da an yi amfani da wadannan muhimman wuraren ajiyar kaya.”
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp