• English
  • Business News
Friday, October 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Rabon Hatsi Tan 42,000

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
Hatsi

Gwamnatin tarayya ta kaddamar da rabon hatsin har tan 42,000 gabanin fara bukukuwan karamar sallah.

Ministan yada labarai Mohammed Idris ya bayyana cewa rabon hatsin tan 42,000 yana daga cikin wani bangare na shirye-shiryen gwamnatin tarayya na rage radadin kuncin rayuwa da na tattalin arziki ga daukacin ‘yan Nijeriya.

  • Sin: An Fitar Da Tsarin Tallafin Kudade Domin Bunkasa Ci Gaba Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba
  • Liu Yuxi Ya Halarci Taron Tattaunawa Kan Wayewar Kan Sin Da Afirka Karo Na Uku

A cikin wata sanarwa da mataimakin daraktan yada labaran ministan, Suleiman Haruna ya fitar, ya ce ministan ya bayyana hakan ne a wurin kaddamar da rabon kayan abinci ga mabukata a daukacin kasar nan.

Kaddamar da rabon dai ya gudana ne saura kwanaki uku ga bikin karamar sallah, a wani yunkuri na gwamnatin tarayya na rage hauhawar farashin kayayyakin abinci a kasar nan baki daya.

Ministan ya ce Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu ya damu matuka da yadda kayayyakin abinci suka yi tashin gwauron zabi a Nijeriya, wanda hakan ta sa ya amince da bayar da umurnin raba tan 42,000 na hatsi, wadanda suka hada da gero, dawa, masara da kuma shinkafa tan 60,000.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Kano Ta Kai Ƙarar Ganduje Da Wasu Kotu Kan Zargin Almundahanar N4.4bn

Dantawaye Ya Karɓi Ragamar Aiki A Matsayin Sabon Kwamishinan Ƴansandan Abuja

Ya ce shirin gwamnatin tarayya karkashin shugaban kasa za ta sake fasalin manufofinta na rage radadin kuncin rayuwa, wanda ba da jumawa za a shawo kan lamarin.

“Gwamnati tana kara kira ga ‘yan Nijeriya su kara ci gaba da hakuri da wannan kuncin rayuwa, mun dauki matakai da za su fitar da ku daga wannan mummunan yanayi. Ba zai gaza jaddada muku cewa wannan yanayin ba zai taba tabbata ba za mu kawo karshensa.”

Ya ce a yanzu haka an samu ragin shigowa da man fetur da kashi 50 duk wata, sannan an samu karuwar darajar naira wanda duk suna cikin shirin sake bunkasa ayyukan ci gaban al’ummar Nijeriya.

“A ‘yan kwanakin da suka gabata, gwamnatin tarayya ta kaddamar da wani shiri a bangaren wutar lantarki da nufin bunkasa fannin domin ‘yan Nijeriya su sami ishasshen lantarki.

“Abu mai muhimmanci ga wannan tsarin dai shi ne, Gwamnatin Tinubu ta bayar da kashi 85 na tallafin lantarki ga ‘yan Nijeriya wanda yakan ya tabbatar da kasancewarta gwamnatin dimokuradiyya mai goyon bayan al’umma tare da kara kahi 15 kacal na kudaden wutar lantarkin ga masu yawan samun wutan.

“Ina kira gare ku da ku ci gaba da goyon bayan Gwamnatin Tinubu a daidai lokacin da take aiwatar da tsare-tsareta domin sake fasalin tattalin arzikin kasa,” in ji shi.

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka
Manyan Labarai

Gwamnatin Kano Ta Kai Ƙarar Ganduje Da Wasu Kotu Kan Zargin Almundahanar N4.4bn

October 17, 2025
Dantawaye Ya Karɓi Ragamar Aiki A Matsayin Sabon Kwamishinan Ƴansandan Abuja
Manyan Labarai

Dantawaye Ya Karɓi Ragamar Aiki A Matsayin Sabon Kwamishinan Ƴansandan Abuja

October 17, 2025
Ƙungiyar NNYLF Ta Gargaɗi Atiku Da Sowore Kan Cinna Wutar Rikici A Nijeriya
Labarai

Ƙungiyar NNYLF Ta Gargaɗi Atiku Da Sowore Kan Cinna Wutar Rikici A Nijeriya

October 17, 2025
Next Post
Babu Wani Shiri Na Kwaso ‘Yan Nijeriya Daga Falasdin Ko Isra’ila –Gwamnatin Tarayya

Jiga-jigan APC Da Ke Tsammanin Samun Mukamin Siyasa A Gwamnatin Tinubu Sun Shiga Rudani

LABARAI MASU NASABA

Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka

Gwamnatin Kano Ta Kai Ƙarar Ganduje Da Wasu Kotu Kan Zargin Almundahanar N4.4bn

October 17, 2025
Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

October 17, 2025
Ma’aikatar Kasuwanci Ta Kasar Sin: Sin Za Ta Kyautata Matakan Takaita Fitar Da Ma’adanan Farin Karfe Na Rare Earth

Ma’aikatar Kasuwanci Ta Kasar Sin: Sin Za Ta Kyautata Matakan Takaita Fitar Da Ma’adanan Farin Karfe Na Rare Earth

October 17, 2025
A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho

Zan Tabbatar Ana Tafiyar Da Ayyuka A Tashoshin Jiragen Ruwa A Afrika Ta Yamma —Dantsoho

October 17, 2025
Dantawaye Ya Karɓi Ragamar Aiki A Matsayin Sabon Kwamishinan Ƴansandan Abuja

Dantawaye Ya Karɓi Ragamar Aiki A Matsayin Sabon Kwamishinan Ƴansandan Abuja

October 17, 2025
peter

2027: Peter Obi Ya Shiga Rudani Kan Jam’iyyar Da Zai Tsaya Takara

October 17, 2025
Ƙungiyar NNYLF Ta Gargaɗi Atiku Da Sowore Kan Cinna Wutar Rikici A Nijeriya

Ƙungiyar NNYLF Ta Gargaɗi Atiku Da Sowore Kan Cinna Wutar Rikici A Nijeriya

October 17, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Dalilin Karyewar Farashin Kayan Abinci

Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Dalilin Karyewar Farashin Kayan Abinci

October 17, 2025
Tinubu

Batun Yin Afuwa Ga ‘Yan Yankin Ogoni Huɗu

October 17, 2025
Shettima

‘Yan Nijeriya Na Dab Da Fita Daga Halin Kuncin Talauci – Shettima 

October 17, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.