• English
  • Business News
Monday, October 20, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Shirin Bunkasa Kiwon Kifi

by Abubakar Abba
3 weeks ago
Kifi

Gwamnatin tarayya ta yi hadaka da Hukumar Kula da Abinci da Ayyukan Noma ta Majalisar Dinkin Duniya (FAO), ta hanyar kaddamar da shirin da za a kashe kimanin Naira miliyan 200, domin kara habaka kiwon kifi a fadin wannan kasa.

Manufar kaddamar da shirin ita ce, domin samar da wadataccen kifi a fadin Nijeriya baki-daya.

  • Ana Fatan Majalisar Wakilan Amurka Za Ta Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Raya Hadin Gwiwar Sin Da Amurka
  • Nazari Kan Littafin Baba Zube Na 5 (Gwamnati)

Darakta a sashen kula da kiwon kifi a Ma’aikatar Bunkasa Tattalin Arzikin Kasa na Teku, Wellington Omoragbon, a jawabinsa a wajen kaddamar da shirin a yankin Eriwe da ke Jihar Ogun ya sanar da cewa, an kaddamar da shirin a karkashin aikin kiwon kifi na ‘FISH4ACP’.

Omoragbon, wanda Darakta na biyu a ma’aikatar ya wakilce shi a wajen taron ya bayyana cewa, manufar shirin ita ce, domin a kara samar da kudade a fannin da kumakokarin ci gaba da gudanar da kiwon na kifi a wannan kasa.

Kazalika, ya yaba wa Hukumar ta FAO da kuma sauran abokan hadaka, bisa tallafa wa kasar nan, musamman ta fuskar kara habaka harkokin kiwon kifin.

LABARAI MASU NASABA

Sharhi Kan Noman Agwaluma A Nijeriya

Gwamnatin Jihar Taraba Ta Ayyana Yi Wa Kasuwannin Sayar Da Dabbobi 9 Garanbawul

Ya kara da cewa, duba da irin dimbin Kogunan da ake da su a wannan kasa, idan aka yi amfani da su yadda ya kamata, za a iya bunkasa fannin na kamun kifi a Nijeriya.

Omoragbon ya ci gaba da cewa, kalubalen da ake ci gaba da fuskanta a halin yanzu shi ne, na karancin kudade da kuma ci gaba da samun hauhawar farashin abincin da ake ciyar da kifin, wanda wannnan babban kalubale ne da masu sana’ar ke ci gaba da fuskanta a kasar.

“Muna sane da cewa, babban kalubalen da masu sana’ar a kasar nan ke ci gaba da fuskanta shi ne, karancin kudade tare da kuma ci gaba da samun hauhawar farashin abincin kifin, amma za mu iya kokarinmu, domin ganin mun samar wa da masu kiwon dauki, musamman domin a cike gibin da ake da shi a fannin,” a cewar Omoragbon.

hi kuwa a nasa jawabin, wakilin hukumar ta FAO a kasar nan da kuma yankin Afirka ta yamma, Koffy Kokako, kira ya yi da a dauki matakan da suka dace, domin kawo karshen shigo da kifi kimanin tan miliyan biyu da ake yi daga kasashen waje zuwa cikin wannan kasa.

Ya bayyana cewa, tarayyar turai da sauran abokan hadaka; sun zuba kudaden ne, domin masu kiwon kifi a kasar, su samu damar samun kudaden da za su yi kiwon kifin tare kuma da kara bunkasa kiwon kifin a kasar.

Haka nan, ya kara da cewa, a kashi na farko na aikin masu kiwon kifi guda 40 ne aka bai wa daga Naira miliyan 2.5 zuwa Naira miliyan biyar, wanda jimillar kudin suka kai kimanin Naira miliyan 200.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sharhi Kan Noman Agwaluma A Nijeriya
Noma Da Kiwo

Sharhi Kan Noman Agwaluma A Nijeriya

October 18, 2025
‘Yansanda Sun Cafke Ɓarayi 13 Tare Da Ƙwato Shanu 27 A Kaduna
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Jihar Taraba Ta Ayyana Yi Wa Kasuwannin Sayar Da Dabbobi 9 Garanbawul

October 18, 2025
Dalilin Bankin AfDB Na Yin Hadaka Da WFP Da IFPRI
Noma Da Kiwo

Dalilin Bankin AfDB Na Yin Hadaka Da WFP Da IFPRI

October 18, 2025
Next Post
Tinubu Zai Gana Da Manyan Ƴan Kasuwa, Zai Ƙaddamar Da Muhimman Aiyuka A Legas

Tinubu Zai Gana Da Manyan Ƴan Kasuwa, Zai Ƙaddamar Da Muhimman Aiyuka A Legas

LABARAI MASU NASABA

Kano Derby: Barau FC Ta Doke Kano Pillars A Karon Farko A Tarihin Gamuwarsu

Kano Derby: Barau FC Ta Doke Kano Pillars A Karon Farko A Tarihin Gamuwarsu

October 19, 2025
Binciken CGTN: An Fitar Da Sakamakon Jin Ra’ayin Jama’a Dangane Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Kolin JKS Na 20

Binciken CGTN: An Fitar Da Sakamakon Jin Ra’ayin Jama’a Dangane Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Kolin JKS Na 20

October 19, 2025
Arewa Ta Samu Kashi 56% Na Muƙaman Gwamnatin Tinubu — Shugaban FCC

Arewa Ta Samu Kashi 56% Na Muƙaman Gwamnatin Tinubu — Shugaban FCC

October 19, 2025
Xi Jinping Ya Mika Sakon Taya Cheng Li-wun Murnar Zama Shugabar Jam’iyyar KMT Ta Kasar Sin

Xi Jinping Ya Mika Sakon Taya Cheng Li-wun Murnar Zama Shugabar Jam’iyyar KMT Ta Kasar Sin

October 19, 2025
Ɗan Jarida Ibrahim Ɗan’uwa Rano Ya Shaƙi Iskar Ƴanci Bayan Tsare Shi

Ɗan Jarida Ibrahim Ɗan’uwa Rano Ya Shaƙi Iskar Ƴanci Bayan Tsare Shi

October 19, 2025
Tie Ning Ta Halarci Bikin Bude Taron Karawa Juna Sani Na ‘Yan Majalisun Dokokin Kasashen Afirka

Tie Ning Ta Halarci Bikin Bude Taron Karawa Juna Sani Na ‘Yan Majalisun Dokokin Kasashen Afirka

October 19, 2025
Ƴansanda Sun Kama Ɗan Jarida A Kano Bisa Zargin Ɓata Suna

Ƴansanda Sun Kama Ɗan Jarida A Kano Bisa Zargin Ɓata Suna

October 19, 2025
Amfanin Yawan Shan Ruwa Da Kuma Illolin Rashin Yawan Sha

Amfanin Yawan Shan Ruwa Da Kuma Illolin Rashin Yawan Sha

October 19, 2025
Xinjiang Ta Janyo Karin Jari A Rubu’i Uku Na Farkon Shekarar Nan

Xinjiang Ta Janyo Karin Jari A Rubu’i Uku Na Farkon Shekarar Nan

October 19, 2025
Yadda Shagwaɓa Kananan Yara Da Kudi Ke Shafar Tarbiyyarsu

Yadda Shagwaɓa Kananan Yara Da Kudi Ke Shafar Tarbiyyarsu

October 19, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.