• English
  • Business News
Saturday, August 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Ta Karbi Rukunin Farko Na Taraktoci Dubu Biyu Daga Belarus

by Abubakar Abba and Sulaiman
5 months ago
in Noma Da Kiwo
0
Aikin Gona
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ana sa ran fannin aikin noma na zamani, zai kara habaka a Nijeriya, biyo bayan isowar Taraktocin noma 2,000 rukunin farko daga Kasar Belarus.

Idan za a iya tunawa, Shugaba Bola Ahmed Tinubu, tuni ya amince da sayo Taraktocin noman 2, 000 daga Kasar Belarus.

  • Ba Gwamna Bala Ne Ya Soke Hawan Daushe Ba – Masarautar Bauchi Ta Bayyana Gaskiya
  • Fashin Baki Kan Kasafin Kudin 2025 Na Naira Tiriliyan 54.99

Ministan Aikin Gona da Samar da Wadacacen Abinci, Sanata Abubakar Kyari ne ya bayyana haka.

Kyari ya sanar da hakan ne, a yayin da ya kai ziyarar gani da ido ta bazata, domin ganin Taraktocin noman guda 2, 000 da suka fara isowa cikin kasar.

“Mun ji dadi da fara karbar wannan rukuni na farko na wadannan Taraktocin noman 2, 000, wanda hakan ya nuna cewa; mun karbi kasshi 30 cikin 100 na kayan”, a cewar Kyari.

Labarai Masu Nasaba

Nazari Kan Dalilin Da Ya Sa Kajin Gidan Gona Ke Samar Da Ƙananan Ƙwai 

Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya

“Wadannan Taraktocin noma 2, 000, za a tura su don fara yin noman daminar 2025 da su, wadanda kuma za a iya horas da matasa a kananan hukumomin kasar 774, har ila yau, muna da wadatattun kayan gyaransu da za a iya yin aikin da su har tsawon shekara hudu”, in ji shi.

A yayin da Kyarin ya kai ziyarar aiki domin duba Taraktocin, ya nuna jin dadinsa kan ci gaban da ake samu na hadakar da gwamnatin tarayya ta yi da kasar ta Belarus, musamman domin samar da kayan aikin noma na zamani.

Kasashen biyu, sun kulla wannan yajejeniyar ce a watan Satumbar 2024.

“A yanzu da nake magana da ku, sama da kwantena 200 da suka yi dakon Tarakatocin da kayan gyaransu, sun iso Jihar Legas, inda ya kara da cewa, a karkashin wannan shiri; an turo Taraktoci 2,000 wadanda kowacce daya ke dauke da kayan gyaranta 9,072”, in ji Kyari.

Ministan ya kara da cewa, samar da wadannan Taraktoc, na daya daga cikin alkawuran yakin neman zabe da Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu ya yi, musamman duba da cewa; gwamnatin ta mayar da hankali wajen farfado da fannin aikin noma na wannan kasa.

 

Tsarin Rabar Da Taraktocin:

Gwamnatin tarayya, ta shirya tsari uku na rabar da wadannan kayayyaki, wadanda suka hada da; sayarwa kai tsaye ga daidaikun mutane, sayar wa da kungiyoyi da wadanda za su karbi haya.

Ana sa ran Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu ne, zai kaddamar da wadannan Taraktoci kafin a fara noman kakar bana da su.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Wakilin Musamman Na Xi Ya Halarci Bikin Rantsar Da Shugabar Namibiya

Next Post

Fadin Yankin Da Ke Fama Da Zaizayar Kasa Na Kasar Sin Ya Ragu A 2024 

Related

Nazari Kan Dalilin Da Ya Sa Kajin Gidan Gona Ke Samar Da Ƙananan Ƙwai 
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Dalilin Da Ya Sa Kajin Gidan Gona Ke Samar Da Ƙananan Ƙwai 

6 days ago
Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya
Noma Da Kiwo

Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya

6 days ago
Nijeriya Na Asarar Tiriliyan 3.2 Sanadiyyar Watsi Da Noma A Gandun Daji
Noma Da Kiwo

Nijeriya Na Asarar Tiriliyan 3.2 Sanadiyyar Watsi Da Noma A Gandun Daji

1 week ago
Manoma Sun Caccaki Tinubu Kan Ƙarfafa Shigo Da Shinkafa Da Masara Daga Ƙasashen Waje
Noma Da Kiwo

Manoma Sun Caccaki Tinubu Kan Ƙarfafa Shigo Da Shinkafa Da Masara Daga Ƙasashen Waje

2 weeks ago
Manyan Ƙalubale Takwas Da Ke Shafar Farashin Tumatir
Noma Da Kiwo

Manyan Ƙalubale Takwas Da Ke Shafar Farashin Tumatir

2 weeks ago
Sin Ta Gaggauta Aikin Gyara Da Kyautata Ababen Aikin Gona
Noma Da Kiwo

Asusun NADF, OCP Da Gwamnatin Katsina Sun Kaddamar Da Noman Hekta 50

3 weeks ago
Next Post
Fadin Yankin Da Ke Fama Da Zaizayar Kasa Na Kasar Sin Ya Ragu A 2024 

Fadin Yankin Da Ke Fama Da Zaizayar Kasa Na Kasar Sin Ya Ragu A 2024 

LABARAI MASU NASABA

Wang Yi: Ya Kamata A Mutunta Tarihi Domin Magance Sake Yin Kuskure

Wang Yi: Ya Kamata A Mutunta Tarihi Domin Magance Sake Yin Kuskure

August 15, 2025
An Samu Rarrabuwar Kawuna A Jam’iyyar ADC Kan Shugabancin David Mark

An Samu Rarrabuwar Kawuna A Jam’iyyar ADC Kan Shugabancin David Mark

August 15, 2025
Ya Kamata A Yi Wa Japan Jinyar Cutar “Mantuwar Tarihi”

Ya Kamata A Yi Wa Japan Jinyar Cutar “Mantuwar Tarihi”

August 15, 2025
Muhimman Batutuwan Da Za Mu Yi La’akari Da Su Kafin Amincewa Da Bukatun Kirkirar Sabbin Jihohi — Majalisar Dattawa

Muhimman Batutuwan Da Za Mu Yi La’akari Da Su Kafin Amincewa Da Bukatun Kirkirar Sabbin Jihohi — Majalisar Dattawa

August 15, 2025
CMG Ya Kaddamar Da Bikin Mu’amalar Al’adu Da Jama’a A Hedkwatar MDD

CMG Ya Kaddamar Da Bikin Mu’amalar Al’adu Da Jama’a A Hedkwatar MDD

August 15, 2025
Gwamna Sani Ya Ba Da Umarnin Gudanar Da Bincike Kan Kashe Wani Matashi A Barnawa

Gwamna Sani Ya Ba Da Umarnin Gudanar Da Bincike Kan Kashe Wani Matashi A Barnawa

August 15, 2025
Rawar Da Dakta Bello Matawalle Ke Takawa Wajen Inganta Harkokin Tsaro A Nijeriya

Rawar Da Dakta Bello Matawalle Ke Takawa Wajen Inganta Harkokin Tsaro A Nijeriya

August 15, 2025
Gasar Wasannin Mutum Mutumin Inji Ta Duniya Ta 2025 Na Gabatar Da Sabbin Fasahohin Zamani

Gasar Wasannin Mutum Mutumin Inji Ta Duniya Ta 2025 Na Gabatar Da Sabbin Fasahohin Zamani

August 15, 2025
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP

Babu Dalilin Da Zai Sa ‘Yan Nijeriya Su Yi Talauci – Tinubu

August 15, 2025
Tattalin Arzikin Sin Ya Bunkasa Yadda Ya Kamata A Watan Yuli

Tattalin Arzikin Sin Ya Bunkasa Yadda Ya Kamata A Watan Yuli

August 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.