ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, December 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Ta Sha Alwashin Kama Waɗanda Suka Kashe Masallata A Malumfashi 

by Sulaiman
4 months ago
Tarayya

Gwamnatin Tarayya ta sha alwashin cafke da kuma hukunta masu hannu a kisan da aka yi wa wasu masallata a Ƙaramar Hukumar Malumfashi ta Jihar Katsina.

 

A cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Juma’a, Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya bayyana wannan hari a matsayin “hari ne na rashin imani da ta’addanci,” tare da jaddada cewa ba zai wuce ba tare da hukunci ba.

ADVERTISEMENT
  • Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe
  • Manyan Jami’an JKS Sun Ziyarci Jami’ai Da Mazauna Birnin Lhasa

Ministan ya ce jami’an tsaro suna kan bin sawun ‘yan ta’addan, tare da tabbatar da cewa “ba za a bar wata kafa ba sai an kama su, kuma an hukunta su yadda ya dace.”

 

LABARAI MASU NASABA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Ya ƙara da cewa: “Gwamnati tana tabbatar wa da ‘yan Nijeriya cewa adalci zai kasance cikin gaggawa kuma mai ƙarfi, kuma ba za a taɓa bari irin waɗannan ayyukan ta’addancin su samu gindin zama a ƙasar nan ba.”

 

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya miƙa ta’aziyya ga iyalan mamatan, al’ummar Malumfashi da kuma Gwamnatin Jihar Katsina.

 

Idris ya ce: “Damuwa da ɓakin cikin su namu ne, kuma gwamnati tana tare da su a wannan lokaci mai duhu. Allah Maɗaukaki ya jiƙan waɗanda suka rasu, ya kuma bai wa waɗanda suka rage ƙarfin zuciya da juriyar ɗaukar wannan babban rashi.”

 

Ministan ya kuma jaddada nasarorin da ake samu kwanan nan a yaƙi da ta’addanci, inda ya bayyana cewa Cibiyar Yaƙi da Ta’addanci ta Ƙasa (NCTC) ta cafke manyan shugabannin ƙungiyar ta’addanci ciki har da Mahmud al-Nigeri na ƙungiyar Mahmuda, da mataimakin sa Abu Abba, da kuma Mahmud Muhammad Usman (Abu Bara’a) na ƙungiyar Ansaru – waɗanda dukkan su suna cikin jerin masu laifi da ake nema a duniya.

 

Ya ce: “Wannan kama manyan shugabannin ya nuna irin nasarorin da ake samu a cikin ayyukan yaƙi da ta’addanci a ƙasar nan, bisa umarnin Shugaban Ƙasa Tinubu, wanda ya bayyana a sarari cewa ayyukan ta’addanci da ke barazana ga Nijeriya da ‘yan ƙasa nan ba da jimawa ba za su zama tarihi.”

 

Ya bayyana cewa Gwamnatin Tarayya ba za ta taɓa barin wanda ya zubar da jinin jama’a ya samu mafaka a Nijeriya ba.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja
Manyan Labarai

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta
Manyan Labarai

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka
Ra'ayi Riga

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Next Post
Hotuna: Shettima Ya Wakilci Shugaba Tinubu Wajen Jana’izar Sarkin Zuru

Hotuna: Shettima Ya Wakilci Shugaba Tinubu Wajen Jana'izar Sarkin Zuru

LABARAI MASU NASABA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

December 21, 2025
Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

December 21, 2025
Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

December 21, 2025
Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

December 21, 2025
An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.