ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, June 22, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

by Abubakar Abba
10 months ago
Dabino

Gwamnatin Tarayya ta bayyana cewa, tana sa ran samun sama da Naira biliyan 300 a duk shekara a fannin noman Dabino.

Ta ayyana wannan kudiri nata ne, biyo bayan rabar da Irin Dabino na kimanin Naira miliyan biyar da ta yi, domin shuka shi a 2025.

  • Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama
  • Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

Darakta Janar na Hukumar Kula da Al’amuran da suka shafi Itatuwan Shukawa ta Kasa (NAGGW), Alhaji Saleh Abubakar, ya bayyana hakan yayin kaddamar da wani aikin shuke-shuke da hukumar ta gudanar a kauyen Maimalari da ke Karamar Hukumar Yusufari ta Jihar Yobe.

ADVERTISEMENT

A cewarsa, gwamnatin tarayya ta kaddamar rabar da Irin Dabinon ne, miliyan biyar wanda take sa ran za a samar da Dabinon da ya kai kilo miliyan 500.

“Yana da matukar muhimmanci a sani cewa, wannan Iri na Dabino, kimanin miliyan biyar hukumar ta ce ta samar,” in ji shi.

LABARAI MASU NASABA

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

Ya ce, za a rabar da Irin Dabinon ne a sauran jihohi sha daya da aka fi yin nomansa, musamman domin a kara habaka nomansa a wadannan jihohi.

“Kowane Irin Dabino daya a kasuwa, zai iya samar da akalla kilo 100 da kudinsa ya kai kimanin Naira miliyan daya, wanda kuma a duk shekara kowannensa za a iya yin nomansa sau biyu,” kamar yadda ya bayyana.

“Mun kiyasata cewa, manomansa da za su noma shi, zai samar wa da gwamnatin tarayya Naira 300, wanda hakan zai kuma kara bunkasa tattalin arzikin kasar”.

Darakta Janar na Hukumar ta NAGGW ya bayyana cewa, manufar shirin ita ce, domin a kara karfafa bangaren tattalin arzikin kasar da kuma ci gaba da bayar da gudunmawar da bangaren ke yi na samar da sama da Naira biliyan 300 a sauran jihohin sha daya da ake nomansa.

Ya bayyana cewa, noman na Dabinon zai taimaka wajen habaka fannin ayyukan tattalin arzikin kasar da kuma kara kare fannin daga matsalolin sauyin yanayi da ke shafar fannin a jihar ta Yobe da kuma sauran jihohi sha daya da ake yin nomansa.

Daraka Janar ya kara da cewa, gangamin na shuka Itatuwan na daya daga cikin ayyukan hukumar na bikin hukumar na cika shekaru goma da kafuwa.

Dabino
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

MASU ALAKA

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

June 20, 2026
Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
Noma Da Kiwo

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

June 20, 2026
Kungiyar Manoman Citta Ta Kasa Ta Yaba Wa Gwamnatin Tarayya Kan Tallafin Da Take Ba Su
Noma Da Kiwo

Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

June 19, 2026
Next Post
Minista Ya Buƙaci Kafafen Yaɗa Labarai Da Su Guji Tallata ’Yan Ta’adda Da ’Yan Bindiga

Gwamnatin Tarayya Ta Sha Alwashin Kama Waɗanda Suka Kashe Masallata A Malumfashi 

LABARAI MASU NASABA

Fisatattun Matasa Sun Ƙone Wata Mata Ƙurmus Kan Jita-Jitar Satar Yara A Kaduna

Fisatattun Matasa Sun Ƙone Wata Mata Ƙurmus Kan Jita-Jitar Satar Yara A Kaduna

June 22, 2026

Mutane 842 Ne Suka Rasa Ransu, Aka Yi Garkuwa Da Sama Da 270 A Watan Mayu – Rahoto

June 21, 2026
PRP Ta Zargi Kwankwaso Da Saye Fom Ɗin Takarar  Jamiyyar

PRP Ta Zargi Kwankwaso Da Saye Fom Ɗin Takarar Jamiyyar

June 21, 2026
An Ƙaddamar Da Dakarun Tsaron Daji 2,187 A Bauchi

An Ƙaddamar Da Dakarun Tsaron Daji 2,187 A Bauchi

June 21, 2026
An Sanar Da Wadanda Suka Lashe Golden Goblet Na Bikin Fina-Finen Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28

An Sanar Da Wadanda Suka Lashe Golden Goblet Na Bikin Fina-Finen Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28

June 21, 2026
Cibiyar CBA Ta Kenya Za Ta Yi Hadin Gwiwa Da Wata Cibiyar Sin Wajen Bunkasa Noma Da Cinikayyar Lemar Kwadi

Cibiyar CBA Ta Kenya Za Ta Yi Hadin Gwiwa Da Wata Cibiyar Sin Wajen Bunkasa Noma Da Cinikayyar Lemar Kwadi

June 21, 2026
Wasu Abubuwa Da Ke Sa Maza Hana Mata Fita Unguwa (Uwargida)

Nasiha Ga Uwargida Kan Zafin Kishi (1)

June 21, 2026
Kasar Sin Ta Karbi Bakuncin Taron Daidaita Batun Kare Hakkin Dan Adam

Kasar Sin Ta Karbi Bakuncin Taron Daidaita Batun Kare Hakkin Dan Adam

June 21, 2026
Wakilin Sin Ya Yi Jawabi A Taron Majalissar UNHRC

Wakilin Sin Ya Yi Jawabi A Taron Majalissar UNHRC

June 21, 2026
Ƴan Ta’adda Sun Ƙone Shingen Bincike Na NSCDC, Sun Sace Wani Mutum A Kebbi

Ƴan Ta’adda Sun Ƙone Shingen Bincike Na NSCDC, Sun Sace Wani Mutum A Kebbi

June 21, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.