• English
  • Business News
Saturday, November 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Ta Shirya Don Fara Rigakafin Kansar Mahaifa

by Idris Aliyu Daudawa
2 years ago
Mahaifa

Hukumar lafiya ta duniya ta kiyasta cewar ana iya maganin kansar mahaifa idan har aka samun yi ma kashi 90 na ‘yan mata allurar rigakafi ta kwayar cuta mai suna Human Papillo Birus.

Gwamanatin tarayya ta kammala shirye- shiryen da suka kamata domin gabatar da allurar da zata ceci rayuwar mata matasa wajen yi masu allurar rigakafin kansar mahaifa allurar rigakafi mai suna Human Papillomabirus (HPB)  wadda zata kare  ‘yan mata daga kamuwa da cutar kansar mahaifa  da sauaran cututtuka masu ala ka da ita.

  • Tinubu Ya Kori Shugaban Hukumar NASENI Bayan Wata 3 Da Nadinsa
  • GORON JUMA’A

Darektan hukumar kula da lafiya matakin farko Dakta Faisal Shuaib, shi ya bayyana hakan ranar Litinin a Abuja lokacin  da aka yi taro da Shugabannin addini kan halin da hukumar take ciki.

Mista Shuaib ya ce gwamnatin zata fara yin allurar ne ranar 25 ga watan Satumba ga ‘yan mata masu shekara 9 zuwa 15.

Ya  ce kansar mahaifa tana shafar iyayenmu,’yan’uwanmu, ‘ya’yanmu mata  da suke kamuwa da cutar  ta hanyar kwara HPB”.

LABARAI MASU NASABA

Trump Ya Ayyana Nijeriya A Matsayin Ƙasar Da Rayuwar Kiristoci Ke Cikin Hatsari

An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano

“Ranar 25 ga watan Satumba wannan shekara za mu fara yi ma ‘ya’yanmu mata masu shekara 9 zuwa 15 allurar rigakafin kamuwa da kansar mahaifa.”

Kwayar Cutar HPB Da Kansar Mahaifa

Kansar mahaifa wata nau’in cutar kansa ce da take girma cikin mahaifar mace, ita ceta hudu da aka fi sani  a tsakanin mata a duniya.Masana sun ce a shekarar 2008 kadau cutar kansar mahaifa ta yi sanadiyar mutuwar kamar yadda aka kiyasta mutuwar mata 311,000 a fadin duniya.

Binciken da Lancet suka yi ya nuna cewar fiye da mata milyan 44 na iya kamuwa da cutar kansar mahaifa tsakanin shekarar 2020 da 2069.

Hakanan ma ta yi gargadin cewa ana iya samun karuwara mutuwa daga kansar mahaifa ada abin zai iya kaiwa kashi 50 nan da  shekara ta  2040, bugu dakari mata da yawa al’amarin zai shafar iyalansu da  al’umma.

Duk da  yake ba a san abinda yake sa ana kamuwa da cutar kansar mahaifa ba sai dai 14 daga cikin 100 na kwayar cutar mai suna Human Papillomabirus (HPB) an gano cewa sune musabbabin kamuwa da a kalla kashi 99 na wadanda suka kamu da cutar kansa.

Hukumar lafiya ta duniya ta ce nau’oin kwayar cuta ta,HPB 16 da 18  sune musabbabin a kalla kashi 70 na nau’oin kansar da kuma kafin kamuwa da ita cutar.

Akwai ma sheda da ta hada kwayar cuta HPB da nau’oin kansa na dubura,wani sashe na farji, farji, azzakari, da oropharynd.

“Allural rigakafin kwayar cutar HPB tace wani cigaban daya shafi al’amarin kula da lafiyar al’umma.Wani abu ne mai nuna hadin kanmu wajen kare mutuncin rayuwa kjamar yadda Shu’aib ya jaddada”.

Gidunmawar Shugabannin Addini

Mista Shuaib ya ce yana da yana da kyau a samiu wayar da kan al’umma ko ina suke hakan ta sa gudunmawar Shugabannin ta taso.

Sune ke da damar sadar da sako mai muhimmanci wanda zai yi tasiri kan al’umma da kawar da shakku, su bada kwarin gwiwa na amincewa da sakon da ake son isarwa zuwa gare su,su yarda da tsarin da zamani ya zo da shi ta hanyar gwamnati.

“Ya ce kalamansu suna da matukar tasiri ga al’umma su amince har ga zuciyar su saboda mutuntawa da girmamawar da suke yi masu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa
Manyan Labarai

Trump Ya Ayyana Nijeriya A Matsayin Ƙasar Da Rayuwar Kiristoci Ke Cikin Hatsari

October 31, 2025
Yadda Waliyin Amarya Ya Sace Sadaki A Kano
Manyan Labarai

An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano

October 31, 2025
Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 
Labarai

Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 

October 31, 2025
Next Post
Likitoci A Kogi Sun Shirya Shiga Yajin Aikin Sai Baba Ta Gani

Likitoci A Kogi Sun Shirya Shiga Yajin Aikin Sai Baba Ta Gani

LABARAI MASU NASABA

CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

October 31, 2025
Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa

Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa

October 31, 2025
Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace

Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace

October 31, 2025
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa

Trump Ya Ayyana Nijeriya A Matsayin Ƙasar Da Rayuwar Kiristoci Ke Cikin Hatsari

October 31, 2025
Yadda Waliyin Amarya Ya Sace Sadaki A Kano

An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano

October 31, 2025
Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

October 31, 2025
Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 

Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 

October 31, 2025
Ya Kamata Sin Da Amurka Su Zama Kawayen Juna Ba Abokan Gaba Ba

Ya Kamata Sin Da Amurka Su Zama Kawayen Juna Ba Abokan Gaba Ba

October 31, 2025
Zaben 2027 Zai Kasance Ne Tsakanin Mulkin Tinubu Da Zabin Ƴan Nijeriya —Atiku Abubakar

Zaben 2027 Zai Kasance Ne Tsakanin Mulkin Tinubu Da Zabin Ƴan Nijeriya —Atiku Abubakar

October 31, 2025
Makarantar Kogi Poly Ta Bankaɗo Masu Ƙirƙirar Takardun Kammala Karatu na Bogi

Makarantar Kogi Poly Ta Bankaɗo Masu Ƙirƙirar Takardun Kammala Karatu na Bogi

October 31, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.