• English
  • Business News
Sunday, October 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Fatali Da Zargin Da Obi Ya Yi Mata Kan Karin Kasafin Kuɗi

by Sulaiman
2 years ago
Tinubu

Ministan Yaɗa Labarai Da Wayar Da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya ce karin kasafin kuɗi na shekarar 2023 da Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya rattaba wa hannu a ranar Laraba, 8 ga Nuwamba, 2023 ba a yi shi cikin rashin tunani da hangen nesa ba, an yi shi ne bisa la’akari da halin matsin tattalin arziki wanda Nijeriya ta ke fuskanta a yanzu. 

 

A wata takarda ga manema labarai da ya rattaba wa hannu a ranar Alhamis, hadimin ministan na musamman a ɓangaren yaɗa labarai, Malam Rabi’u Ibrahim, ya ruwaito cewa ministan ya yi kira ga ɗan takarar zama shugaban ƙasa na Jam’iyyar Labour a zaɓen 2023 da ya samu lokaci ya zauna ya karanta kundin karin kasafin kuɗin na naira tiriliyan 2.17 a tsanake domin ya fahimce shi da kyau, zai ga ya ƙunshi tanadin kuɗin da aka yi wa muhimman ayyuka irin su tsaro, aikin gona, wadata ƙasa da abinci, ayyuka da gidaje, ƙarin albashi ga ma’aikata, shirin bada rance ga ɗalibai, da hanyoyin sauƙaƙa wa talaka halin da ya ke ciki, da sauran su, waɗanda an yi su ne don a ƙarfafa ginshiƙin tattalin arzikin ƙasar tare da inganta halin zamantakewa a tsakanin ‘yan Nijeriya.

  • Tinubu Ya Rattaba Hannu A Kan Karin Kasafin Kudi Na Naira tiriliyan 2.17 Na Shekarar 2023.
  • Ka Nemi Sana’a Siyasa Ba Taka Ba Ce,Tinubu Ga Peter Obi

Ya ce: “Ɗimbin tanade-tanaden da ke cikin ɗorin kasafin kuɗin ya nuna babban burin Shugaba Tinubu da yadda ya ke matuƙar son ya tallafa wa ayyukan da gwamnati ta sa a gaba, ya tunkari matsalar tsaro gaba-gaɗi, kuma ya gaggauta haɓaka hanyoyin da za a bi a magance matsalolin ƙasar waɗanda cire tallafin mai ya haifar.

Idris ya yi kira ga ‘yan siyasar adawa da su kasance masu sani kuma adalai wajen bayyana ra’ayin su mabambanta, sannan su kauce wa yi wa gaskiya jirwaye don kurum su cimma burin siyasa.

LABARAI MASU NASABA

Nafisa Abdullahi Aminu: Yarinyar Da Ta Ɗaukaka Darajar Nijeriya A Idon Duniya

Gwarzon Banki Na Shekarar 2025 Bankin Providus

Ya yi bayanin cewa an yi ɗorin kasafin kuɗin ne bayan tattaunawa tare da tuntuɓar masu ruwa da tsaki da su ka dace waɗanda su ka bada tabbacin cewa kasafin ya yi daidai da buƙata da muradun jama’ar Nijeriya.

Idris ya nanata cewa kamar yadda Shugaba Tinubu ya ke da son ganin an bi dukkan ƙa’idoji wajen sarrafa kuɗin gwamnati, to sai da aka yi nazari a tsanake kan kowane lissafi a kasafin kuɗin don tabbatar da cewa an kashe kuɗaɗen jama’a a yadda ya kamata.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Labarai

Nafisa Abdullahi Aminu: Yarinyar Da Ta Ɗaukaka Darajar Nijeriya A Idon Duniya

October 25, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji
Manyan Labarai

Gwarzon Banki Na Shekarar 2025 Bankin Providus

October 25, 2025
Gwarzuwar Hukumar Da Ta Kawo Sauyi A Kula Da Muhalli A 2025 Hukumar NASENI
Manyan Labarai

Gwarzuwar Hukumar Da Ta Kawo Sauyi A Kula Da Muhalli A 2025 Hukumar NASENI

October 25, 2025
Next Post
Mutuwar farad-daya

Yawaitar Mutuwar Farad-daya A Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

October 25, 2025

Nafisa Abdullahi Aminu: Yarinyar Da Ta Ɗaukaka Darajar Nijeriya A Idon Duniya

October 25, 2025
Sin Da Amurka Sun Fara Tattaunawa Kan Tattalin arziki Da Cinikayya A Kuala Lumpur

Sin Da Amurka Sun Fara Tattaunawa Kan Tattalin arziki Da Cinikayya A Kuala Lumpur

October 25, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwarzon Banki Na Shekarar 2025 Bankin Providus

October 25, 2025
Firaministan Sin Ya Isa Singapore Don Ziyarar Aiki

Firaministan Sin Ya Isa Singapore Don Ziyarar Aiki

October 25, 2025
Gwarzuwar Hukumar Da Ta Kawo Sauyi A Kula Da Muhalli A 2025 Hukumar NASENI

Gwarzuwar Hukumar Da Ta Kawo Sauyi A Kula Da Muhalli A 2025 Hukumar NASENI

October 25, 2025
An Gudanar Da Taron Cika Shekaru 80 Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan Da Dawo Da Shi Kasar Sin A Beijing

An Gudanar Da Taron Cika Shekaru 80 Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan Da Dawo Da Shi Kasar Sin A Beijing

October 25, 2025

Daɓid Adeyemi

October 25, 2025
Wakilin Sin: Shawarar GGI Ta Nuna Yadda Za A Jagoranci Bunkasa Makomar MDD

Wakilin Sin: Shawarar GGI Ta Nuna Yadda Za A Jagoranci Bunkasa Makomar MDD

October 25, 2025
Gwarzuwar Ma’aikaciyar Jinya Ta Shekarar 2025: Misis Mabel Ijeoma Duaka

Gwarzuwar Ma’aikaciyar Jinya Ta Shekarar 2025: Misis Mabel Ijeoma Duaka

October 25, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.