Gwamnatin Tarayya ta amince ta karbo bashi daga kasar waje na dala biliyan 2.2 don bunkasa tattalin arzikin Nijeriya.
Ministan Kudi, Wale Edun ne, ya bayyana haka bayan taron majalisar zartarwa.
- CHINA HI-TECH FAIR:Za A Kaddamar Da Fasahohi, Kayayyaki, Da Sakamako Sabbi Fiye Da 4300
- Ya Kamata Rungumar Hadin Gwiwa Da Yin Komai A Bude Su Zamo Ginshikan Ci Gaban Yankin Asiya Da Pacifik A Nan Gaba
Bayan taron majalisar zartarwa da shugaban kasa, Bola Tinubu ya jagoranta, Edun ya bayyana cewa kudaden za su fito daga Eurobond ($1.7 biliyan) da Sukuk bond ($500 miliyan), sai kuma a jira amincewar Majalisar Dokoki.
Bashin zai kasance a 2024 kuma wani bangare ne na gyare-gyare domin inganta tattalin arziki da janyo masu zuba hannun jari.
Edun ya kuma bayyana sabon asusun zuba jari na gida na Naira biliyan 250 da aka kafa don samar da lamunin gidaje masu rahusa.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp