Gwamnatin Tarayya ta bayyana cewa tana aiki tare da Ƙungiyar Lauyoyi ta Nijeriya (NBA) domin ƙirƙirar shirye-shiryen tallafawa fursunoni bayan sun kammala zaman kurkuku da kuma bayar da taimakon shari’a kyauta ga waɗanda ke jiran gurfanarwa.
Ministan Cikin Gida, Dr. Olubunmi Tunji-Ojo, ne ya bayyana hakan a ranar Alhamis bayan ziyarar bazata da ya kai Gidan Gyaran Hali da ke Kuje a Abuja.
- Kafafen Sada Zumunta Na Zamani Suna Taimakawa Wajen Ta’azzara Matsalar Tsaro A Arewa – Yari
- Shugaba Tinubu Ya Yi Wa Maryam Sanda Afuwa Bayan Shafe Shekaru 6 A Gidan Yari
Ya ce wannan ziyara da ya kai tare da Shugaban ƙungiyar lauyoyi (NBA), Afam Josiah Osigwe (SAN), na da nufin duba halin da ake ciki a gidan gyaran halin da kuma gano hanyoyin inganta tsarin gyaran halin da yin adalci.
Tunji-Ojo ya bayyana cewa haɗin gwuiwar da ke tsakanin ma’aikatarsa da NBA na cikin shirin gwamnatin Shugaba Bola Tinubu na “Renewed Hope”, wanda ke son inganta tsarin gyaran hali da rage cunkoson gidajen yari. Ya ƙara da cewa wannan shiri zai taimaka wajen shirya fursunoni su koma cikin al’umma cikin sauƙi tare da rage yiwuwar sake aikata laifi.
Ya ƙara da cewa ma’aikatar cikin gida za ta ci gaba da jagoranci ta hanyar aikatawa, inda ya jaddada muhimmancin ƙirƙirar hanyoyin da za su inganta walwalar fursunoni da jami’ar gidan yari. “Ta wannan hanyar, za mu rage cunkoso a gidajen gyaran hali da kuma taimaka wa fursunoni su koma cikin al’umma cikin nasara,” in ji shi.