• English
  • Business News
Saturday, June 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Za Ta Zuba Jarin Dala Miliyan 617 A Fannin Fasahar Sadarwa

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
Gwamnatin Tarayya Za Ta Zuba Jarin Dala Miliyan 617 A Fannin Fasahar Sadarwa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A wani mataki na bunkasa harkokin samar da ayyukan yi ta hanyar kirkire-kirkire da fasaha, shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu a watan Nuwamban 2023 za ta kaddamar da zuba jarin dala miliyan 617.7 a bangaren fasahar sadarwar zamani da kirkire-kirkire ta cikin wani shiri (i-DICE) a takaice.

Domin cimma wannan nasarar, mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya bayar da umarni ga kwamitin aiwatarwa na i-DICE da ya tabbatar ya fara gudanar da harkokin gabansa a karshen watan Nuwamban wannan shekarar.

  • CMG Ya Gudanar Da Taron Bita Yayin Cika Shekara Daya Da Watsa Shirin Leaders Talk
  • Sojoji Sun Kashe Dan Bindiga, Sun Ceto Mutane 6, Sun Kwato Makamai A Kaduna

A cewar wata sanarwa da kakakin mataimakin shugaban kasan, Stanley Nkwocha, ya fitar, ya ce, Shettima ya bayyana hakan ne a lokacin da tawagar i-DICE suka ziyarceshi domin masa bayanin matakin da ake kai dangane da shirin a halin yanzu a fadar shugaban kasa da ke Abuja.

A wajen ganawar, Shettima na nanata muhimmimancin shirin gwamnatin tarayya na samar da ayyukan yi a bangaren fasahar sadarwar zamani, yana mai cewa, tabbas gwamnati za ta cimma alkawuran da ta dauka a wannan fannin.

A cewarsa, ya bukaci abokan jere a shirin i-DICE da su tabbatar da sun ririta kudaden da aka ware domin tafiyar da shirin, ya ce, dala miliyan 617.7 zai kawo gagarumin sauyi muddin aka tafiyar da shi ta hanyoyin da suka dace.

Labarai Masu Nasaba

Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

“Idan aka yi nazarin kalubalen da kasar nan ke ciki da irin bukatar samar da ayyuka da matasanmu ke yi, akwai bukatar a hada karfi da karfe wajen shawo kan wannan matsalar, ina rokonku da ku bayar da hadin kai domin tabbatar da shirin ya fara aiki zuwa karshen watan Nuwamba.

“Ina fatan zan ke samun bayanin aikace-aikacenku na mako-mako da zarar aka fara shirin. Kuma muna son a hanzarta gudanar da ayyukan da zai shafi dukkanin bangarorin kasar nan.”

Sai ya ba su tabbacin goyon bayan gwamnatin tarayya a kowani lokaci domin cimma wannan nasarar na samar da ayyuka da ceto ‘yan kasa daga halin rashin aikin yi.
Tun da farko, ministan kudi, Wale Edun, ya shaida cewar shirin zai taimaka sosai wajen cimma alkawuran da gwamnatin Bola Tinubu ta yi wa ‘yan kasa na samar da ayyukan yi a bangaren kimiyyar fasahar sadarwa ga mutum miliyan 1.2.

“Tabbas dala miliyan 617 zai dauki tsawon lokaci na taimaka wa yunkurin shugaban kasa na samar da ayyukan yi da kyautata tattalin arziki musamman samar da dama ga matasa. Wani muhimman lamari a shirin shi ne kaso 50 mata ne za su amfana da wannan shirin,” ya shaida.

Shi kuma ministan sadarwa, kirkire-kirkire da tattalin arzikin zamani, Bosus Tijjani, cewa ya yi shirin wani babban damace ga kasar nan.
“Fasaha da samar da ayyukan yi na tattalin arzikin zamani na taimakawa sosai wajen kyautata tattalin arziki. A duniyance an amince kuma an shaidi yadda fasaha ke bada damar shawo kan matsaloli da daman gaske.”

Ya kara da cewa, ta cikin shirin za a bai wa al’ummar kasa na cikin gida damar fito da fasaharsu domin taimaka wa kasar kuma su ma za su samu kudaden tafiyar da harkokin rayuwarsu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: NCCNITDA
ShareTweetSendShare
Previous Post

Yakin Isra’ila Da Hamas: Tura Ta Kai Bango

Next Post

Minista Ya Nemi Google Ta Dakatar Da Yada Labarai Masu Barazana Ga Hadin Kan Nijeriya

Related

Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu
Manyan Labarai

Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

1 hour ago
Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe
Manyan Labarai

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

2 hours ago
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa
Manyan Labarai

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

3 hours ago
Za a Binne Ɗantata A Madina, Za Ai Yi Sallar Ga’ibi A Kano
Labarai

Za a Binne Ɗantata A Madina, Za Ai Yi Sallar Ga’ibi A Kano

3 hours ago
Ƙungiyar Lauyoyi Musulmi Reshen Kaduna Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Matafiya A Filato
Labarai

Ƙungiyar Lauyoyi Musulmi Reshen Kaduna Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Matafiya A Filato

7 hours ago
Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu
Manyan Labarai

Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu

8 hours ago
Next Post
Minista Ya Nemi Google Ta Dakatar Da Yada Labarai Masu Barazana Ga Hadin Kan Nijeriya

Minista Ya Nemi Google Ta Dakatar Da Yada Labarai Masu Barazana Ga Hadin Kan Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Mata Ku Kula Da Masu Tallan Maganin Hana Kishiya

Mata Ku Kula Da Masu Tallan Maganin Hana Kishiya

June 28, 2025
Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

June 28, 2025
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

Ƙoƙarin Ƙungiyoyin Afrika A Gasar Kofin Duniya

June 28, 2025
Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

June 28, 2025
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

June 28, 2025
Za a Binne Ɗantata A Madina, Za Ai Yi Sallar Ga’ibi A Kano

Za a Binne Ɗantata A Madina, Za Ai Yi Sallar Ga’ibi A Kano

June 28, 2025
Me Ya Sa Syria Ta Bari Ana Amfani Da Sararin Samaniyarta Wajen Kai Wa Iran Hari?

Me Ya Sa Syria Ta Bari Ana Amfani Da Sararin Samaniyarta Wajen Kai Wa Iran Hari?

June 28, 2025
Wace Nahiya Ce Ta Fi Iya Ƙwallon Ƙafa Tsakanin Turai Da Kudancin Amurka?

Wace Nahiya Ce Ta Fi Iya Ƙwallon Ƙafa Tsakanin Turai Da Kudancin Amurka?

June 28, 2025
Ƙasashen Afrika 10 Da Suka Fi Girman Kasafin Kudi A 2025

Ƙasashen Afrika 10 Da Suka Fi Girman Kasafin Kudi A 2025

June 28, 2025
Ƙungiyar Lauyoyi Musulmi Reshen Kaduna Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Matafiya A Filato

Ƙungiyar Lauyoyi Musulmi Reshen Kaduna Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Matafiya A Filato

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.