• English
  • Business News
Wednesday, May 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Za Ta Zuba Jarin Dala Miliyan 617 A Fannin Fasahar Sadarwa

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
Gwamnatin Tarayya Za Ta Zuba Jarin Dala Miliyan 617 A Fannin Fasahar Sadarwa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A wani mataki na bunkasa harkokin samar da ayyukan yi ta hanyar kirkire-kirkire da fasaha, shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu a watan Nuwamban 2023 za ta kaddamar da zuba jarin dala miliyan 617.7 a bangaren fasahar sadarwar zamani da kirkire-kirkire ta cikin wani shiri (i-DICE) a takaice.

Domin cimma wannan nasarar, mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya bayar da umarni ga kwamitin aiwatarwa na i-DICE da ya tabbatar ya fara gudanar da harkokin gabansa a karshen watan Nuwamban wannan shekarar.

  • CMG Ya Gudanar Da Taron Bita Yayin Cika Shekara Daya Da Watsa Shirin Leaders Talk
  • Sojoji Sun Kashe Dan Bindiga, Sun Ceto Mutane 6, Sun Kwato Makamai A Kaduna

A cewar wata sanarwa da kakakin mataimakin shugaban kasan, Stanley Nkwocha, ya fitar, ya ce, Shettima ya bayyana hakan ne a lokacin da tawagar i-DICE suka ziyarceshi domin masa bayanin matakin da ake kai dangane da shirin a halin yanzu a fadar shugaban kasa da ke Abuja.

A wajen ganawar, Shettima na nanata muhimmimancin shirin gwamnatin tarayya na samar da ayyukan yi a bangaren fasahar sadarwar zamani, yana mai cewa, tabbas gwamnati za ta cimma alkawuran da ta dauka a wannan fannin.

A cewarsa, ya bukaci abokan jere a shirin i-DICE da su tabbatar da sun ririta kudaden da aka ware domin tafiyar da shirin, ya ce, dala miliyan 617.7 zai kawo gagarumin sauyi muddin aka tafiyar da shi ta hanyoyin da suka dace.

Labarai Masu Nasaba

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

“Idan aka yi nazarin kalubalen da kasar nan ke ciki da irin bukatar samar da ayyuka da matasanmu ke yi, akwai bukatar a hada karfi da karfe wajen shawo kan wannan matsalar, ina rokonku da ku bayar da hadin kai domin tabbatar da shirin ya fara aiki zuwa karshen watan Nuwamba.

“Ina fatan zan ke samun bayanin aikace-aikacenku na mako-mako da zarar aka fara shirin. Kuma muna son a hanzarta gudanar da ayyukan da zai shafi dukkanin bangarorin kasar nan.”

Sai ya ba su tabbacin goyon bayan gwamnatin tarayya a kowani lokaci domin cimma wannan nasarar na samar da ayyuka da ceto ‘yan kasa daga halin rashin aikin yi.
Tun da farko, ministan kudi, Wale Edun, ya shaida cewar shirin zai taimaka sosai wajen cimma alkawuran da gwamnatin Bola Tinubu ta yi wa ‘yan kasa na samar da ayyukan yi a bangaren kimiyyar fasahar sadarwa ga mutum miliyan 1.2.

“Tabbas dala miliyan 617 zai dauki tsawon lokaci na taimaka wa yunkurin shugaban kasa na samar da ayyukan yi da kyautata tattalin arziki musamman samar da dama ga matasa. Wani muhimman lamari a shirin shi ne kaso 50 mata ne za su amfana da wannan shirin,” ya shaida.

Shi kuma ministan sadarwa, kirkire-kirkire da tattalin arzikin zamani, Bosus Tijjani, cewa ya yi shirin wani babban damace ga kasar nan.
“Fasaha da samar da ayyukan yi na tattalin arzikin zamani na taimakawa sosai wajen kyautata tattalin arziki. A duniyance an amince kuma an shaidi yadda fasaha ke bada damar shawo kan matsaloli da daman gaske.”

Ya kara da cewa, ta cikin shirin za a bai wa al’ummar kasa na cikin gida damar fito da fasaharsu domin taimaka wa kasar kuma su ma za su samu kudaden tafiyar da harkokin rayuwarsu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: NCCNITDA
ShareTweetSendShare
Previous Post

Yakin Isra’ila Da Hamas: Tura Ta Kai Bango

Next Post

Minista Ya Nemi Google Ta Dakatar Da Yada Labarai Masu Barazana Ga Hadin Kan Nijeriya

Related

JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu
Manyan Labarai

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

16 minutes ago
A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka
Ra'ayi Riga

A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

1 hour ago
Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata
Labarai

Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata

3 hours ago
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya
Manyan Labarai

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

5 hours ago
‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 239, Sun Ƙwato Makamai Da Alburusai A Kogi
Labarai

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 239, Sun Ƙwato Makamai Da Alburusai A Kogi

7 hours ago
Dakarun Soji Sun Daƙile Wani Sabon Harin ISWAP A Dikwa
Labarai

Dakarun Soji Sun Daƙile Wani Sabon Harin ISWAP A Dikwa

8 hours ago
Next Post
Minista Ya Nemi Google Ta Dakatar Da Yada Labarai Masu Barazana Ga Hadin Kan Nijeriya

Minista Ya Nemi Google Ta Dakatar Da Yada Labarai Masu Barazana Ga Hadin Kan Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

May 14, 2025
Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata

Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata

May 14, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

May 14, 2025
Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

May 14, 2025
Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

May 14, 2025
Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin

Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin

May 14, 2025
‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 239, Sun Ƙwato Makamai Da Alburusai A Kogi

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 239, Sun Ƙwato Makamai Da Alburusai A Kogi

May 14, 2025
Dakarun Soji Sun Daƙile Wani Sabon Harin ISWAP A Dikwa

Dakarun Soji Sun Daƙile Wani Sabon Harin ISWAP A Dikwa

May 14, 2025
Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.