ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, June 8, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Za Ta Zuba Jarin Dala Miliyan 617 A Fannin Fasahar Sadarwa

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Gwamnatin tarayya

A wani mataki na bunkasa harkokin samar da ayyukan yi ta hanyar kirkire-kirkire da fasaha, shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu a watan Nuwamban 2023 za ta kaddamar da zuba jarin dala miliyan 617.7 a bangaren fasahar sadarwar zamani da kirkire-kirkire ta cikin wani shiri (i-DICE) a takaice.

Domin cimma wannan nasarar, mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya bayar da umarni ga kwamitin aiwatarwa na i-DICE da ya tabbatar ya fara gudanar da harkokin gabansa a karshen watan Nuwamban wannan shekarar.

  • CMG Ya Gudanar Da Taron Bita Yayin Cika Shekara Daya Da Watsa Shirin Leaders Talk
  • Sojoji Sun Kashe Dan Bindiga, Sun Ceto Mutane 6, Sun Kwato Makamai A Kaduna

A cewar wata sanarwa da kakakin mataimakin shugaban kasan, Stanley Nkwocha, ya fitar, ya ce, Shettima ya bayyana hakan ne a lokacin da tawagar i-DICE suka ziyarceshi domin masa bayanin matakin da ake kai dangane da shirin a halin yanzu a fadar shugaban kasa da ke Abuja.

ADVERTISEMENT

A wajen ganawar, Shettima na nanata muhimmimancin shirin gwamnatin tarayya na samar da ayyukan yi a bangaren fasahar sadarwar zamani, yana mai cewa, tabbas gwamnati za ta cimma alkawuran da ta dauka a wannan fannin.

A cewarsa, ya bukaci abokan jere a shirin i-DICE da su tabbatar da sun ririta kudaden da aka ware domin tafiyar da shirin, ya ce, dala miliyan 617.7 zai kawo gagarumin sauyi muddin aka tafiyar da shi ta hanyoyin da suka dace.

LABARAI MASU NASABA

Yayin Da Dangote Ya Bayyana A Tattaunawar Neman Aiki…

Gwamnatin Tarayya Zata Biya Naira Biliyan 700 Ga Ƴan Kwangila 1,240 Da Aka Tantance

“Idan aka yi nazarin kalubalen da kasar nan ke ciki da irin bukatar samar da ayyuka da matasanmu ke yi, akwai bukatar a hada karfi da karfe wajen shawo kan wannan matsalar, ina rokonku da ku bayar da hadin kai domin tabbatar da shirin ya fara aiki zuwa karshen watan Nuwamba.

“Ina fatan zan ke samun bayanin aikace-aikacenku na mako-mako da zarar aka fara shirin. Kuma muna son a hanzarta gudanar da ayyukan da zai shafi dukkanin bangarorin kasar nan.”

Sai ya ba su tabbacin goyon bayan gwamnatin tarayya a kowani lokaci domin cimma wannan nasarar na samar da ayyuka da ceto ‘yan kasa daga halin rashin aikin yi.
Tun da farko, ministan kudi, Wale Edun, ya shaida cewar shirin zai taimaka sosai wajen cimma alkawuran da gwamnatin Bola Tinubu ta yi wa ‘yan kasa na samar da ayyukan yi a bangaren kimiyyar fasahar sadarwa ga mutum miliyan 1.2.

“Tabbas dala miliyan 617 zai dauki tsawon lokaci na taimaka wa yunkurin shugaban kasa na samar da ayyukan yi da kyautata tattalin arziki musamman samar da dama ga matasa. Wani muhimman lamari a shirin shi ne kaso 50 mata ne za su amfana da wannan shirin,” ya shaida.

Shi kuma ministan sadarwa, kirkire-kirkire da tattalin arzikin zamani, Bosus Tijjani, cewa ya yi shirin wani babban damace ga kasar nan.
“Fasaha da samar da ayyukan yi na tattalin arzikin zamani na taimakawa sosai wajen kyautata tattalin arziki. A duniyance an amince kuma an shaidi yadda fasaha ke bada damar shawo kan matsaloli da daman gaske.”

Ya kara da cewa, ta cikin shirin za a bai wa al’ummar kasa na cikin gida damar fito da fasaharsu domin taimaka wa kasar kuma su ma za su samu kudaden tafiyar da harkokin rayuwarsu.

Gwamnatin tarayya
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Jami’an Tsaro Sun Cafke Masu Garkuwa Da Mutane 4, Sun Ceto Uwa Da Ɗanta A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Zaɓen Fidda Gwani Na Gwamna: Ba Za Mu Lamunci Kaƙaba Mana Ɗan Takara A Bauchi Ba – Mambobin APC

MASU ALAKA

Yayin Da Dangote Ya Bayyana A Tattaunawar Neman Aiki…
Labarai

Yayin Da Dangote Ya Bayyana A Tattaunawar Neman Aiki…

June 8, 2026
Gwamnatin Tarayya Zata Biya Naira Biliyan 700 Ga Ƴan Kwangila 1,240 Da Aka Tantance
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Zata Biya Naira Biliyan 700 Ga Ƴan Kwangila 1,240 Da Aka Tantance

June 8, 2026
Ɗiyar Obasanjo Ta Fice Daga APC Bayan Gaza Samun Tikitin Takarar Gwamna
Manyan Labarai

Ɗiyar Obasanjo Ta Fice Daga APC Bayan Gaza Samun Tikitin Takarar Gwamna

June 8, 2026
Next Post
Minista Ya Nemi Google Ta Dakatar Da Yada Labarai Masu Barazana Ga Hadin Kan Nijeriya

Minista Ya Nemi Google Ta Dakatar Da Yada Labarai Masu Barazana Ga Hadin Kan Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

A Ƙarshe Jamilu Gwamna Ya Samu Babbar Dama Ta Yin Takara

A Ƙarshe Jamilu Gwamna Ya Samu Babbar Dama Ta Yin Takara

June 8, 2026
Yayin Da Dangote Ya Bayyana A Tattaunawar Neman Aiki…

Yayin Da Dangote Ya Bayyana A Tattaunawar Neman Aiki…

June 8, 2026
Morocco Na Fargabar Rashin Ƴan Wasa 2 Gabanin Karawa Da Brazil

Morocco Na Fargabar Rashin Ƴan Wasa 2 Gabanin Karawa Da Brazil

June 8, 2026
Gwamnatin Tarayya Zata Biya Naira Biliyan 700 Ga Ƴan Kwangila 1,240 Da Aka Tantance

Gwamnatin Tarayya Zata Biya Naira Biliyan 700 Ga Ƴan Kwangila 1,240 Da Aka Tantance

June 8, 2026
Ɗiyar Obasanjo Ta Fice Daga APC Bayan Gaza Samun Tikitin Takarar Gwamna

Ɗiyar Obasanjo Ta Fice Daga APC Bayan Gaza Samun Tikitin Takarar Gwamna

June 8, 2026
Kwamitin Majalisa Ya Kwato Naira Miliyan 521.76 Na VAT Daga CBN

Kwamitin Majalisa Ya Kwato Naira Miliyan 521.76 Na VAT Daga CBN

June 8, 2026
Sabon Rikici Ya Kunno Kai A NDC, An Buƙaci INEC Ta Soke Rijistarta

Sabon Rikici Ya Kunno Kai A NDC, An Buƙaci INEC Ta Soke Rijistarta

June 8, 2026
Shugabannin NDC Na Arewa Maso Yamma Sun Zargi Kwankwaso Da Ƙoƙarin Babakere

Shugabannin NDC Na Arewa Maso Yamma Sun Zargi Kwankwaso Da Ƙoƙarin Babakere

June 8, 2026
An Ceto Mutane 360 Daga Hannun Boko Haram, Wasu Na Can Riƙe Wurinsu

An Ceto Mutane 360 Daga Hannun Boko Haram, Wasu Na Can Riƙe Wurinsu

June 8, 2026
Sojoji Sun Kama Mutane 5 Masu Kai Wa Ƴan Bindiga Bayanai A Neja

Sojoji Sun Kama Mutane 5 Masu Kai Wa Ƴan Bindiga Bayanai A Neja

June 7, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.