ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, July 19, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Za Ta Zuba Jarin Dala Miliyan 617 A Fannin Fasahar Sadarwa

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Gwamnatin tarayya

A wani mataki na bunkasa harkokin samar da ayyukan yi ta hanyar kirkire-kirkire da fasaha, shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu a watan Nuwamban 2023 za ta kaddamar da zuba jarin dala miliyan 617.7 a bangaren fasahar sadarwar zamani da kirkire-kirkire ta cikin wani shiri (i-DICE) a takaice.

Domin cimma wannan nasarar, mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya bayar da umarni ga kwamitin aiwatarwa na i-DICE da ya tabbatar ya fara gudanar da harkokin gabansa a karshen watan Nuwamban wannan shekarar.

  • CMG Ya Gudanar Da Taron Bita Yayin Cika Shekara Daya Da Watsa Shirin Leaders Talk
  • Sojoji Sun Kashe Dan Bindiga, Sun Ceto Mutane 6, Sun Kwato Makamai A Kaduna

A cewar wata sanarwa da kakakin mataimakin shugaban kasan, Stanley Nkwocha, ya fitar, ya ce, Shettima ya bayyana hakan ne a lokacin da tawagar i-DICE suka ziyarceshi domin masa bayanin matakin da ake kai dangane da shirin a halin yanzu a fadar shugaban kasa da ke Abuja.

ADVERTISEMENT

A wajen ganawar, Shettima na nanata muhimmimancin shirin gwamnatin tarayya na samar da ayyukan yi a bangaren fasahar sadarwar zamani, yana mai cewa, tabbas gwamnati za ta cimma alkawuran da ta dauka a wannan fannin.

A cewarsa, ya bukaci abokan jere a shirin i-DICE da su tabbatar da sun ririta kudaden da aka ware domin tafiyar da shirin, ya ce, dala miliyan 617.7 zai kawo gagarumin sauyi muddin aka tafiyar da shi ta hanyoyin da suka dace.

LABARAI MASU NASABA

Shugaba Tinubu Zai Yi Jawabi Ga Shugabannin Duniya A Taron MDD Karo Na 81

Damawa Da Mata A Siyasa: Kujerun Majalisun Tarayya Na Iya Ƙaruwa Zuwa 121, da Kuma 397 A 2027

“Idan aka yi nazarin kalubalen da kasar nan ke ciki da irin bukatar samar da ayyuka da matasanmu ke yi, akwai bukatar a hada karfi da karfe wajen shawo kan wannan matsalar, ina rokonku da ku bayar da hadin kai domin tabbatar da shirin ya fara aiki zuwa karshen watan Nuwamba.

“Ina fatan zan ke samun bayanin aikace-aikacenku na mako-mako da zarar aka fara shirin. Kuma muna son a hanzarta gudanar da ayyukan da zai shafi dukkanin bangarorin kasar nan.”

Sai ya ba su tabbacin goyon bayan gwamnatin tarayya a kowani lokaci domin cimma wannan nasarar na samar da ayyuka da ceto ‘yan kasa daga halin rashin aikin yi.
Tun da farko, ministan kudi, Wale Edun, ya shaida cewar shirin zai taimaka sosai wajen cimma alkawuran da gwamnatin Bola Tinubu ta yi wa ‘yan kasa na samar da ayyukan yi a bangaren kimiyyar fasahar sadarwa ga mutum miliyan 1.2.

“Tabbas dala miliyan 617 zai dauki tsawon lokaci na taimaka wa yunkurin shugaban kasa na samar da ayyukan yi da kyautata tattalin arziki musamman samar da dama ga matasa. Wani muhimman lamari a shirin shi ne kaso 50 mata ne za su amfana da wannan shirin,” ya shaida.

Shi kuma ministan sadarwa, kirkire-kirkire da tattalin arzikin zamani, Bosus Tijjani, cewa ya yi shirin wani babban damace ga kasar nan.
“Fasaha da samar da ayyukan yi na tattalin arzikin zamani na taimakawa sosai wajen kyautata tattalin arziki. A duniyance an amince kuma an shaidi yadda fasaha ke bada damar shawo kan matsaloli da daman gaske.”

Ya kara da cewa, ta cikin shirin za a bai wa al’ummar kasa na cikin gida damar fito da fasaharsu domin taimaka wa kasar kuma su ma za su samu kudaden tafiyar da harkokin rayuwarsu.

Gwamnatin tarayya
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ATBU Ta Janye Filin Ginin Masallaci Da Ta Bai wa TIMSAN, Ta Amince Kowa Ya Yi Addininsa Yadda Ya Fahimta
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu

MASU ALAKA

Shugaba Tinubu Zai Yi Jawabi Ga Shugabannin Duniya A Taron MDD Karo Na 81
Labarai

Shugaba Tinubu Zai Yi Jawabi Ga Shugabannin Duniya A Taron MDD Karo Na 81

July 19, 2026
majalisar kasa
Manyan Labarai

Damawa Da Mata A Siyasa: Kujerun Majalisun Tarayya Na Iya Ƙaruwa Zuwa 121, da Kuma 397 A 2027

July 19, 2026
Kofin Duniya
Wasanni

Abubuwa Uku Da Ya Kamata Kusani Akan Kofin Duniya

July 19, 2026
Next Post
Minista Ya Nemi Google Ta Dakatar Da Yada Labarai Masu Barazana Ga Hadin Kan Nijeriya

Minista Ya Nemi Google Ta Dakatar Da Yada Labarai Masu Barazana Ga Hadin Kan Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Shugaba Tinubu Zai Yi Jawabi Ga Shugabannin Duniya A Taron MDD Karo Na 81

Shugaba Tinubu Zai Yi Jawabi Ga Shugabannin Duniya A Taron MDD Karo Na 81

July 19, 2026
majalisar kasa

Damawa Da Mata A Siyasa: Kujerun Majalisun Tarayya Na Iya Ƙaruwa Zuwa 121, da Kuma 397 A 2027

July 19, 2026
Kofin Duniya

Abubuwa Uku Da Ya Kamata Kusani Akan Kofin Duniya

July 19, 2026
Gwamnatin tarayya

Abubuwa Shida Da Ya Kamata Mace Ta Sani Kafin Ta Yi Aure

July 19, 2026
An Kaddamar Da “Bikin Fasahar AI Na Sin Na 2026” A Shanghai

An Kaddamar Da “Bikin Fasahar AI Na Sin Na 2026” A Shanghai

July 18, 2026
Fim Ko Gaske:Yaushe Masu Kallon Fina-finai Za Su Daina Daukar Fim A Matsayin Gaske

Fim Ko Gaske:Yaushe Masu Kallon Fina-finai Za Su Daina Daukar Fim A Matsayin Gaske

July 18, 2026
Sin Ta Nuna Matukar Adawa Da Matakin Burtaniya Na Mallake Kamfanin Karafa Na British Steel

Sin Ta Nuna Matukar Adawa Da Matakin Burtaniya Na Mallake Kamfanin Karafa Na British Steel

July 18, 2026
Tasirin AI (Artificial Intelligence) A Harkokin Al’umma Na Yau Da Kullum

Tasirin AI (Artificial Intelligence) A Harkokin Al’umma Na Yau Da Kullum

July 18, 2026
Xavi Ya Ce A Shirye Yake Ya Karɓi Ragamar Horar Da Tawagar Ƙasa

Xavi Ya Ce A Shirye Yake Ya Karɓi Ragamar Horar Da Tawagar Ƙasa

July 18, 2026
Masanin Kimiyya Na Sin Ya Lashe Kyautar UNESCO-Russia Mendeleev A Fannin Tushen Kimiyya

Masanin Kimiyya Na Sin Ya Lashe Kyautar UNESCO-Russia Mendeleev A Fannin Tushen Kimiyya

July 18, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.