ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 22, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Minista Ya Nemi Google Ta Dakatar Da Yada Labarai Masu Barazana Ga Hadin Kan Nijeriya

by Sulaiman
3 years ago
Google

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya roƙi kamfanin taskace bayanai a intanet (Google), da ya daƙile bazuwar dukkan saƙwannin da ka iya zama haɗari da barazana ga ɗorewar dunƙulalliyar al’umma a ƙasa ɗaya.

Ministan ya yi wannan kira ne a lokacin da ya karɓi baƙuncin tawagar manyan jami’an Google na Afrika ta Yamma, bisa jagorancin daraktansu, Mista Olumide Balogun.

  • CMG Ya Kaddamar Da Bikin Baje Kolin “Hanyar Samun Wayewar Kai” A London
  • ‘Yan Nijeriya Za Su Iya Tara Min Kudi Don Yi Wa Tinubu Waka Saboda Kaunarsa -Mawaki Rarara

Tawagar ta kai masa ziyara ne a ranar Alhamis, a Abuja.

ADVERTISEMENT

Ya ce: “Akwai matuƙar muhimmanci a ga cewa an tantance tasiri da kuma illolin manhajojin yaɗa bayanai ta intanet. Ina ganin ku ne aikin hana yaɗuwar abu mai illa ya fi wajaba a kan ku.

“Gwamnati ba ta da aniya ko tunanin ƙaƙaba wa ‘yancin faɗar albarkacin baki ko ‘yan jarida takunkumi. Shugaban Ƙasa ba mai so ya ga ana tauye ‘yancin faɗar albarkacin baki ba ne.

LABARAI MASU NASABA

Yayin Da Na’ura Ta Fara Tunani: Bil’adama Ne Kadai Zai Iya Tunkarar Lamarinta

Kabiru Gaya Ya Amince Zai Sauya Sheƙa Zuwa APC

“To sai dai kuma, idan har aka ce bayani mai haɗari ne, zai iya zama babbar matsala kenan a gare mu. Zai tarwatsa haɗin kanmu tare da haifar mana da ruɗu a cikin ƙasa.

“Mun san cewa isar da saƙwannin bayanai ta intanet na da muhimmanci sosai wajen ɗorewar ƙasa har ta tsaya da diddiginta a matsayin ƙasa. Don haka akwai buƙatar samun ‘yancin bayyana ra’ayi a kafar da kowa zai ji ba a tauye masa haƙƙi ko ‘yanci ba.

“Saboda haka, muddin aka samu fahimta ta hanyar isar da sakonnin bayanai a cikin jama’a, to za a rage ɗarɗar da ambaliyar labarai na bogi. A kula, ‘yanci ya na tafiya ne tare da sanin ƙa’idoji da ya kamata.”

Minista ya ƙara da cewa, Google na da gagarumin haƙƙi na ganin cewa haƙƙin da aka bai wa mutane su na watsa bayanai a kafafen sada zumunta bai zama musabbabin haifar da hargitsi ga ‘yan Nijeriya ba.

Da ya ke nasa jawabin tun da farko, Mista Balogun ya shaida wa ministan cewa, cikin shekaru uku da su ka gabata zuwa yanzu kamfanin ya horas da ‘yan jarida 3,500 a Nijeriya.

Ya ce an horas da su ne dabarun amfani da hanyoyin fasahar zamani wajen tantance sahihan labarai, da tace labaran bogi da sauran su.

Google
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Babban Jami’in Diflomasiyyar Sin Ya Jaddada Matsayar Dangantakar Kasar Da Turai Ta Hadin Gwiwa
  • Sulaiman
    Kasar Sin: Yunkurin Japan Na Kalubalantar Odar Kasa Da Kasa Bayan Yakin Duniya Na Biyu A Bayyana Yake Kasa
  • Sulaiman
    Kasar Sin Ta Nuna Matukar Rashin Amincewarta Ga Jakadan Philippines Kan Tsokanar Fada A Ren’ai Jiao
  • Sulaiman
    An Rufe Babban Taron AI Na Duniya Na 2026

MASU ALAKA

Yayin Da Na’ura Ta Fara Tunani: Bil’adama Ne Kadai Zai Iya Tunkarar Lamarinta
Labarai

Yayin Da Na’ura Ta Fara Tunani: Bil’adama Ne Kadai Zai Iya Tunkarar Lamarinta

July 21, 2026
Kabiru Gaya Ya Amince Zai Sauya Sheƙa Zuwa APC
Labarai

Kabiru Gaya Ya Amince Zai Sauya Sheƙa Zuwa APC

July 21, 2026
‘Yansanda Sun Kama Mutane 2 Kan Zargin Satar Shanu A Bauchi, Sun Ƙwato Bijimi 3
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kama Mutane 2 Kan Zargin Satar Shanu A Bauchi, Sun Ƙwato Bijimi 3

July 21, 2026
Next Post
Jiragen NAF Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Da Lalata Baburansu 40 Da Bindigu 6 A Borno

Jiragen NAF Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Da Lalata Baburansu 40 Da Bindigu 6 A Borno

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin: Yunkurin Japan Na Kalubalantar Odar Kasa Da Kasa Bayan Yakin Duniya Na Biyu A Bayyana Yake Kasa

Kasar Sin: Yunkurin Japan Na Kalubalantar Odar Kasa Da Kasa Bayan Yakin Duniya Na Biyu A Bayyana Yake Kasa

July 21, 2026
Babban Jami’in Diflomasiyyar Sin Ya Jaddada Matsayar Dangantakar Kasar Da Turai Ta Hadin Gwiwa

Babban Jami’in Diflomasiyyar Sin Ya Jaddada Matsayar Dangantakar Kasar Da Turai Ta Hadin Gwiwa

July 21, 2026
Yayin Da Na’ura Ta Fara Tunani: Bil’adama Ne Kadai Zai Iya Tunkarar Lamarinta

Yayin Da Na’ura Ta Fara Tunani: Bil’adama Ne Kadai Zai Iya Tunkarar Lamarinta

July 21, 2026
Kasar Sin Ta Nuna Matukar Rashin Amincewarta Ga Jakadan Philippines Kan Tsokanar Fada A Ren’ai Jiao

Kasar Sin Ta Nuna Matukar Rashin Amincewarta Ga Jakadan Philippines Kan Tsokanar Fada A Ren’ai Jiao

July 21, 2026
An Rufe Babban Taron AI Na Duniya Na 2026

An Rufe Babban Taron AI Na Duniya Na 2026

July 21, 2026
Kabiru Gaya Ya Amince Zai Sauya Sheƙa Zuwa APC

Kabiru Gaya Ya Amince Zai Sauya Sheƙa Zuwa APC

July 21, 2026
‘Yansanda Sun Kama Mutane 2 Kan Zargin Satar Shanu A Bauchi, Sun Ƙwato Bijimi 3

‘Yansanda Sun Kama Mutane 2 Kan Zargin Satar Shanu A Bauchi, Sun Ƙwato Bijimi 3

July 21, 2026
Li Qiang Ya Taya Andy Burnham Murnar Zama Sabon Firaministan Birtaniya

Li Qiang Ya Taya Andy Burnham Murnar Zama Sabon Firaministan Birtaniya

July 21, 2026
Kasar Sin Ta Gabatar Da Matakan Bunkasa Bangaren Bayar Da Hidimomi A Cikin Gida

Kasar Sin Ta Gabatar Da Matakan Bunkasa Bangaren Bayar Da Hidimomi A Cikin Gida

July 21, 2026
Nasarawa Na Sa Ran Samun Dala Miliyan 10 Daga Lithium Kafin Karshen Shekara – Gwamna Sule

Nasarawa Na Sa Ran Samun Dala Miliyan 10 Daga Lithium Kafin Karshen Shekara – Gwamna Sule

July 21, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.