• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tinubu Na Ƙoƙarin Gyara Kurakuran Baya, Ba Jawo Wahala Ba – Minista

by Sulaiman
9 months ago
in Labarai
0
Gwamnatin Tinubu Na Ƙoƙarin Gyara Kurakuran Baya, Ba Jawo Wahala Ba – Minista
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya ce, babban abin da gwamnatin Tinubu ta fi mayar da hankali a kai ba shi ne ta ɗora wa ‘yan Nijeriya wahala ba, sai dai ta gyara munanan tsare-tsare da matakan da ba su dace ba waɗanda a tarihi suka kawo cikas ga ci gaban Nijeriya.

 

A wata sanarwa da Mataimakin Ministan na Musamman kan Harkokin Yaɗa Labarai, Rabi’u Ibrahim, ya fitar,  Ministan ya bayyana haka ne a Abuja a ranar Laraba yayin da yake ganawa da jami’an diflomasiyya a Ma’aikatar Harkokin Wajen Ƙasar dangane da zanga-zangar da aka yi a faɗin ƙasar.

  • Gwamnan Gombe Ya Bayar Da Umurnin Raba Kayan Abinci Don Rage Raɗaɗin Kuncin Rayuwa
  • Gwamnatin Filato Ta Sassauta Dokar Hana Fita A Jihar

Ya jaddada ƙudirin Shugaba Tinubu na aiwatar da gyare-gyare da nufin samar da ci gaba mai ɗorewa da kuma inganta rayuwa ga ɗaukacin ‘yan ƙasa, yana mai cewa, ƙalubalen da ake fuskanta a yanzu na wucin-gadi ne.

 

Labarai Masu Nasaba

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Ministan ya ce, “Yana da muhimmanci mu fara da wannan bayanin cewa, Shugaba Tinubu bai zo ofis don ya jawo wahalhalu ko kuma wahalar da ’yan Nijeriya ba. Ya zo ne don warware matsalolin baya; tare da yunƙurin gyara da yawa daga cikin tsare-tsaren da ba su da kyau da kuma matakan da ba su dace ba da suka kawo mana koma-baya a matsayin mu na ƙasa shekaru da yawa.

Tinubu

“Shugaban Ƙasa ya hau karagar mulki ne a ɗaya daga cikin lokuta mafi ƙalubale a tarihin Nijeriya, inda ƙasar ke kashe kashi 97 na dukkan kuɗaɗen shigarta wajen biyan basussuka; tare da yawaitar talauci, hauhawar rashin aikin yi, lalacewar ababen more rayuwa, da rashin tsaro. Yayin da take fuskantar waɗannan abubuwa masu ban tsoro, gwamnati ta ɗauki ƙwararan matakai tare da aiwatar da gyare-gyaren da aka daɗe ba a yi ba domin ceto tattalin arziƙin ƙasar daga durƙushewa.”

 

Ministan ya bayyana cewa kawar da tallafin man fetur ya zama dole don karkatar da kuɗaɗen zuwa sassa masu muhimmanci kamar kiwon lafiya, ilimi, ababen more rayuwa, da tsaro, wanda ke tasiri kai tsaye ga jin daɗin ’yan ƙasa da ci gaban ƙasa.

 

Ya amince da cewa ana shan raɗaɗin sauyin da ke tattare da wannan matakin kuma ya yi nuni da cewa Gwamnatin Tarayya ta tsara shirye-shiryen shiga tsakani don magance waɗannan ƙalubale.

 

“Mun dage sosai kan tabbatar da cewa an aiwatar da waɗannan ayyukan domin kawo sassauci ga ‘yan Nijeriya,” inji Idris.

 

Yayin da yake magana kan zanga-zangar da aka gudanar a faɗin ƙasar nan, ministan ya ce gwamnati na mutunta ‘yancin yin taro cikin lumana da ‘yancin faɗin albarkacin baki, waɗanda su ne ginshiƙin dukkan al’ummomin dimokiraɗiyya, amma ya jaddada cewa abin da ya fara a matsayin zanga-zangar lumana a wasu jihohi da kuma Babban Birnin Tarayya shi ne ba da jimawa ba wasu da suka kutsa kai cikin zanga-zangar suka karɓe ragamar tare da shirya tarzomar da ta lalata rayuka da dukiyoyi.

 

“An samu rahotannin ƙone-ƙone, ɓarna, sace-sace, da kuma arangama da jami’an tsaro a garuruwa da dama. Abin takaici, waɗannan al’amura sun yi sanadin asarar rayukan da ba su ji ba ba su gani ba da kuma asarar dukiya mai yawa,” inji shi.

 

Idris ya tabbatar wa da jami’an diflomasiyya cewa Gwamnatin Tarayya ta fara gudanar da bincike kan tashe-tashen hankulan da aka yi a lokacin zanga-zangar domin a gano tare da gurfanar da duk masu hannu a cikin lamarin.

 

Ya ce: “Mun himmatu wajen hana sake aukuwar irin wannan mummunan lamari a nan gaba.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AlmundahanaRashin TsaroTabarbarewar Tattalin ArzikiTsadar Rayuwa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Shugaban Timor-Leste Ya Yaba Kayayyaki Kirar Kasar Sin

Next Post

Jami’in Kenya: Taron Dandalin FOCAC Zai Zurfafa Dangantakar Sin Da Kenya

Related

UTME
Manyan Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

5 hours ago
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista
Labarai

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

5 hours ago
gaza
Labarai

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

7 hours ago
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa
Labarai

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

9 hours ago
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja
Labarai

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

10 hours ago
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu
Manyan Labarai

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

11 hours ago
Next Post
Jami’in Kenya: Taron Dandalin FOCAC Zai Zurfafa Dangantakar Sin Da Kenya

Jami’in Kenya: Taron Dandalin FOCAC Zai Zurfafa Dangantakar Sin Da Kenya

LABARAI MASU NASABA

UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.