• English
  • Business News
Monday, July 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Zamfara Ta Ƙudiri Aniyar Bunkasa Harkokin Ilimi A Jihar

by Leadership Hausa
1 year ago
in Labarai
0
Gwamnatin Zamfara Ta Ƙudiri Aniyar Bunkasa Harkokin Ilimi A Jihar
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamna Dauda Lawal na jihar Zamfara ya jaddada ƙudirin gwamnatin sa na ganin ta kafa tubali mai inganci a harkar ilimi don ’yan baya su samu ilimi mai inganci a Zamfara.

Gwamna Lawal ya bayyana haka ne a ranar Asabar ɗin da ta gabata yayin gasar wasanni na shekara ta 2024 karo na uku na makarantar Almufida International Academy da ke Gusau.

  • Hukumar Hisbah A Zamfara Ta Hana ‘Ƙauye Day’ Da Sauran Bukukuwan Aure Da Ba Su Cancanta Ba A Jihar
  • ‘Yan Bindiga: Gwamna Dauda Ya Kai Ziyarar Jaje A Zurmi Da Birnin Magaji

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar ta bayyana cewa mai makarantar ya bai wa Gwamna Lawal lambar yabo a matsayin Babban Kwamandan Abokantaka na Kwalejin (GCFC).

Ya ce, Gwamnan ya yaba da yadda ɗaliban suka nuna ƙwazo a lokutan wasanni daban-daban.

A yayin jawabin nasa, Gwamna Lawal ya nuna jin daɗin sa ga yadda makarantar ke gudanar da ayyukanta na ɗora ɗalibai kan kyawawan halaye.

Labarai Masu Nasaba

Harin Sojojin Sama Ya Hallaka Manyan Shugabannin ISWAP A Borno

Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Jimamin Rasuwar Babban Ɗan Jarida Leon Usigbe

Ya kuma yaba wa ɗaliban bisa kyawawan wasannin motsa jiki, haɗin kai, da kuma ƙwarewar da suka nuna.

“Abin da na gani a nan ya burge ni, waɗannan halaye masu kyau suna nuna kyakkyawar makoma.

“Na zo ne a yau domin nuna goyon baya da nuna ƙwarin gwiwa wajen inganta fannin ilimi a jihar Zamfara. Idan dai za a iya tunawa, na kafa dokar ta-ɓaci a fannin ilimi da lafiya na jihar a wani shiri na gwamnati na.

“Shawarar mayar da martani ga ƙalubalen da harkar ilimi ta Zamfara ke fuskanta, mataki ne mai kyau na ganin ’yan baya sun samu ilimi mai inganci.

“Ilimi shi ne ƙashin bayan kowace al’umma, kuma Zamfara ba za ta iya yin watsi da shi ba.”

Gwamnan ya kuma zagaya, inda ya duba kayayyakin da kwalejin ta ke da su domin bunƙasa ƙwarewar ɗalibai.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: DaudaIlimiZamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Darusan Da Aka Koya A Gasar Kofin Afirka

Next Post

Zaben Shugaban Kasar Amurka 2024: Afirka Ba Ta Shirya Fuskantar Wa’adi Na Biyu Na Shugabancin Trump Ba

Related

Harin Sojojin Sama Ya Hallaka Manyan Shugabannin ISWAP A Borno
Manyan Labarai

Harin Sojojin Sama Ya Hallaka Manyan Shugabannin ISWAP A Borno

23 minutes ago
Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Jimamin Rasuwar Babban Ɗan Jarida Leon Usigbe
Labarai

Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Jimamin Rasuwar Babban Ɗan Jarida Leon Usigbe

31 minutes ago
Ƴansanda Sun Cafke Barayin Motoci 3 A Kano
Labarai

Ƴansanda Sun Cafke Barayin Motoci 3 A Kano

1 hour ago
Tinubu Ya Ƙaddamar Da Shirin Bai Wa Malaman Manyan Makarantun Nijeriya Rancen Miliyan 10
Labarai

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Shirin Bai Wa Malaman Manyan Makarantun Nijeriya Rancen Miliyan 10

2 hours ago
An Kwashe Duk Dabbobin Tsohon Akanta-Janar
Labarai

An Kwashe Duk Dabbobin Tsohon Akanta-Janar

3 hours ago
Gwamnatin Kano Ta Kafa Kwamitin Bincike Kan Belin Dillalin Kwaya
Labarai

Gwamnatin Kano Ta Kafa Kwamitin Bincike Kan Belin Dillalin Kwaya

5 hours ago
Next Post
Zaben Shugaban Kasar Amurka 2024: Afirka Ba Ta Shirya Fuskantar Wa’adi Na Biyu Na Shugabancin Trump Ba

Zaben Shugaban Kasar Amurka 2024: Afirka Ba Ta Shirya Fuskantar Wa’adi Na Biyu Na Shugabancin Trump Ba

LABARAI MASU NASABA

Harin Sojojin Sama Ya Hallaka Manyan Shugabannin ISWAP A Borno

Harin Sojojin Sama Ya Hallaka Manyan Shugabannin ISWAP A Borno

July 28, 2025
Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Jimamin Rasuwar Babban Ɗan Jarida Leon Usigbe

Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Jimamin Rasuwar Babban Ɗan Jarida Leon Usigbe

July 28, 2025
Ƴansanda Sun Cafke Barayin Motoci 3 A Kano

Ƴansanda Sun Cafke Barayin Motoci 3 A Kano

July 28, 2025
Tinubu Ya Ƙaddamar Da Shirin Bai Wa Malaman Manyan Makarantun Nijeriya Rancen Miliyan 10

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Shirin Bai Wa Malaman Manyan Makarantun Nijeriya Rancen Miliyan 10

July 28, 2025
An Kwashe Duk Dabbobin Tsohon Akanta-Janar

An Kwashe Duk Dabbobin Tsohon Akanta-Janar

July 28, 2025
Gwamnatin Kano Ta Kafa Kwamitin Bincike Kan Belin Dillalin Kwaya

Gwamnatin Kano Ta Kafa Kwamitin Bincike Kan Belin Dillalin Kwaya

July 28, 2025
Mazauna Sokoto Sun Yi Murna Bayan Nasarar Kashe Fitattun ‘Yan Bindiga 3 A Jihar

Mazauna Sokoto Sun Yi Murna Bayan Nasarar Kashe Fitattun ‘Yan Bindiga 3 A Jihar

July 27, 2025
Zhao Leji Ya Kai Ziyarar Sada Zumunta A Kyrgyzstan

Zhao Leji Ya Kai Ziyarar Sada Zumunta A Kyrgyzstan

July 27, 2025
Gwamnan Bauchi Ya Sulhunta Rikicin Manoma Da Makiyaya A Darazo

Gwamnan Bauchi Ya Sulhunta Rikicin Manoma Da Makiyaya A Darazo

July 27, 2025
Sin Ta Samu Ci Gaban Aikin Jigilar Kaya A Rabin Farko Na Bana

Sin Ta Samu Ci Gaban Aikin Jigilar Kaya A Rabin Farko Na Bana

July 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.