• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Zamfara Ta Ƙudiri Aniyar Bunkasa Harkokin Ilimi A Jihar

by Leadership Hausa
1 year ago
in Labarai
0
Gwamnatin Zamfara Ta Ƙudiri Aniyar Bunkasa Harkokin Ilimi A Jihar
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamna Dauda Lawal na jihar Zamfara ya jaddada ƙudirin gwamnatin sa na ganin ta kafa tubali mai inganci a harkar ilimi don ’yan baya su samu ilimi mai inganci a Zamfara.

Gwamna Lawal ya bayyana haka ne a ranar Asabar ɗin da ta gabata yayin gasar wasanni na shekara ta 2024 karo na uku na makarantar Almufida International Academy da ke Gusau.

  • Hukumar Hisbah A Zamfara Ta Hana ‘Ƙauye Day’ Da Sauran Bukukuwan Aure Da Ba Su Cancanta Ba A Jihar
  • ‘Yan Bindiga: Gwamna Dauda Ya Kai Ziyarar Jaje A Zurmi Da Birnin Magaji

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar ta bayyana cewa mai makarantar ya bai wa Gwamna Lawal lambar yabo a matsayin Babban Kwamandan Abokantaka na Kwalejin (GCFC).

Ya ce, Gwamnan ya yaba da yadda ɗaliban suka nuna ƙwazo a lokutan wasanni daban-daban.

A yayin jawabin nasa, Gwamna Lawal ya nuna jin daɗin sa ga yadda makarantar ke gudanar da ayyukanta na ɗora ɗalibai kan kyawawan halaye.

Labarai Masu Nasaba

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

Ya kuma yaba wa ɗaliban bisa kyawawan wasannin motsa jiki, haɗin kai, da kuma ƙwarewar da suka nuna.

“Abin da na gani a nan ya burge ni, waɗannan halaye masu kyau suna nuna kyakkyawar makoma.

“Na zo ne a yau domin nuna goyon baya da nuna ƙwarin gwiwa wajen inganta fannin ilimi a jihar Zamfara. Idan dai za a iya tunawa, na kafa dokar ta-ɓaci a fannin ilimi da lafiya na jihar a wani shiri na gwamnati na.

“Shawarar mayar da martani ga ƙalubalen da harkar ilimi ta Zamfara ke fuskanta, mataki ne mai kyau na ganin ’yan baya sun samu ilimi mai inganci.

“Ilimi shi ne ƙashin bayan kowace al’umma, kuma Zamfara ba za ta iya yin watsi da shi ba.”

Gwamnan ya kuma zagaya, inda ya duba kayayyakin da kwalejin ta ke da su domin bunƙasa ƙwarewar ɗalibai.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: DaudaIlimiZamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Darusan Da Aka Koya A Gasar Kofin Afirka

Next Post

Zaben Shugaban Kasar Amurka 2024: Afirka Ba Ta Shirya Fuskantar Wa’adi Na Biyu Na Shugabancin Trump Ba

Related

Lassa Da Shawara Sun Kashe Mutum 183 A Jihohi 36 Da Abuja
Labarai

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

2 hours ago
Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?
Da ɗumi-ɗuminsa

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

3 hours ago
ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 
Labarai

ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

3 hours ago
‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi
Labarai

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

4 hours ago
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara
Manyan Labarai

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

6 hours ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

7 hours ago
Next Post
Zaben Shugaban Kasar Amurka 2024: Afirka Ba Ta Shirya Fuskantar Wa’adi Na Biyu Na Shugabancin Trump Ba

Zaben Shugaban Kasar Amurka 2024: Afirka Ba Ta Shirya Fuskantar Wa’adi Na Biyu Na Shugabancin Trump Ba

LABARAI MASU NASABA

Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

May 15, 2025
Lassa Da Shawara Sun Kashe Mutum 183 A Jihohi 36 Da Abuja

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

May 15, 2025
Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

May 15, 2025
ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

May 15, 2025
‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

May 15, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

May 15, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

May 15, 2025
UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.