• English
  • Business News
Friday, May 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Zamfara Ta Kaddamar Da Gangamin Kula Da Lafiya Kyauta

by Hussein Yero
2 years ago
in Labarai
0
Gwamnatin Zamfara Ta Kaddamar Da Gangamin Kula Da Lafiya Kyauta
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin Jihar Zamfara ta ƙaddamar da babban gangamin duba marasa lafiya kyauta, wanda zai magance wasu cututtuka da suke addabar al’umma.

Sashe na farko na wannan shiri an fara shi ne da haɗin gwiwa da ofishin matar gwamnan jihar, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, wanda zai taimakawa mutanen da ke fama da cutar yanar ido (cataract), cutar gwaiwa (groin swellings), cutar yoyon fitsari (VVF) da kuma ilimin yadda za su kiwata lafiyarsu.

  • Yadda Tawagar Malaman Nijeriya Suka Tattauna Da Sojojin Juyin Mulkin Nijar

 

Wata sanarwa da mai magana da yawun Gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar a ranar Lahadi, ta ce wannan gangami na kula da kiwon lafiya kyauta an fara shi ne ranar Juma’ar da ta gabata, inda aka samu nasarar yi wa mutum 81 aikin ido, da kuma yi wa mutum 49 aikin cutar gwaiwa.

Ya ƙara da cewa, wannan babban gangami na kiwon lafiya an tsara duk wata zai yi aiki ga masu cutar gwaiwa mutum 1, 000, za a kuma yi wa mata 200 masu fama da yoyon fitsairi aiki, haka nan za a yi aiki ga mutum 1, 000 masu fama da ciwon ido.

Labarai Masu Nasaba

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

Sanarwar ta ce: “Gwamnatin Zamfara ta kafa kwamiti ne na ƙwararru waɗanda suka yi bincike suka tsamo nau’ikan cututtukan da ke addabar mutane.

“Binciken kwamitin ne ya tabbatar da cewa, mutane sun fi buƙatar aiki kyauta a cututtuka irinsu yanar ido, cutar gwaiwa, cutar yoyon fitsari da ilimin yadda za su kiwata lafiyarsu.

“Wannan shi ne karo na farko a Jihar Zamfara da gwamnati take yin gangami don kula da kiwon lafiyar jama’a masu fama da manyan cututtuka.

“Wannan gangami ya bayar da dama ga dukkanin ‘yan jiha daga kauyuka da birane don su amfana.

“Wannan yana daga cikin ƙoƙarin gwamnatin Dauda Lawal na tabbatar da yi wa sashen kiwon lafiya garanbawul. Kuma wannan gangami na bayar da tallafin ana bada shi ne ga dukkanin jama’ar da ke ƙananan hukumomi 14.

“Ana yin wannan gangami ne a babban asibitin Gusau, babban asibitin Sarki Fahad, da kuma Asibitin Kwararru na Yariman Bakura.” In ji shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: gwamnatiKiwon LafiyaZamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Yi Wa Uwar Da Ta Kashe ‘Ya’yanta Daurin Rai Da Rai A Amurka

Next Post

Tottenham Na Neman Gift Orban Na Gent Domin Maye Gurbin Kane

Related

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta
Ra'ayi Riga

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

2 hours ago
Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci
Labarai

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

4 hours ago
Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma
Noma Da Kiwo

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

5 hours ago
Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje
Labarai

Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

6 hours ago
GORON JUMA’A 09/05/2025
Labarai

GORON JUMA’A 09/05/2025

7 hours ago
AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 
Labarai

AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

8 hours ago
Next Post
Tottenham Na Neman Gift Orban Na Gent Domin Maye Gurbin Kane

Tottenham Na Neman Gift Orban Na Gent Domin Maye Gurbin Kane

LABARAI MASU NASABA

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

May 9, 2025
Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

May 9, 2025
Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

May 9, 2025
Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

May 9, 2025
Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

May 9, 2025
GORON JUMA’A 09/05/2025

GORON JUMA’A 09/05/2025

May 9, 2025
Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

May 9, 2025
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

May 9, 2025
AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

May 9, 2025
Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

May 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.