ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Tawagar Malaman Nijeriya Suka Tattauna Da Sojojin Juyin Mulkin Nijar

by Muhammad
3 years ago
Nijar

BBC ta rawaito yadda ziyarar Malaman Nijeriya ta kasance a Jamhoriyar Nijar kan wani tayin da suka yi na neman taka irin tasu rawar a dambarwar da ta ɓarke tsakanin Sojojin da suka yi juyin mulki a Nijar da kuma ECOWAS, Malaman addinin musulunci daga Nijeriya sun samu damar tattaunawa da shugabannin sojin Nijar.

Wani lamari na neman kaucewa zub da jini ya haɗe kan malaman Nijeriya da alokuta da dama suke yi wa juna kallon hadarin kaji.

  • Hanyoyin Da Suka Kamata ECOWAS Ta Bi Wajen Warware Rikicin Nijar
  • Yadda Malamai Suka Dirar Wa Batun Yaki Da Nijar

Ƙarƙashin jagorancin Sheikh Abdullahi Bala Lau, shugaban kungiyar Izallah ta Nijeriya, malaman sun tattauna da sojojin juyin mulki na tsawon sa’o’i uku.

ADVERTISEMENT

Sheik Bala Lau ya shaida cewa tun da fari sai da sojojin suka fara neman afuwa game da rashin sauraren tawagar tsohon shugaban Nijeriya Janar Abdulsalami Abubakar da Sarkin Musulmi da sauransu.

“katse wutar lantarki da hana shiga da abinci Nijar ya janyo zanga-zanga kuma matasa sun fito a ranar, gudun kada a yi musu rashin ɗa’a in sojojin shi ya sa ba su iya ba su damar tattaunawa da su ba, amma sun ce mu bayar da haƙuri a madadinsu,” kamar yadda Bala Lau ya shaida.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

Ta ɓangaren abin da suka cimma Malamain ya ce an samu ƙofar tattaunawar diflomasiyya, domin kuwa sojojin sun ce yanzu a shirye suke su tattauna da wakilan ECOWAS, a ko da yaushe.

“Tun daga yadda suka karɓe mu muka san cewa tafiyarmu ta yi nasara. Sun turo ministoci da Firaiministan ƙasar filin jirgin sama domin su zo su tare mu, sun kai mu kuma har fadar shugaban ƙasa da kansu.

“Mun tattauna kusan sa’a uku da su, mun tattauna kan abubuwa da dama. Mun isar da saƙo kuma mun yi nasiha domin a kiyaye zubar da jini, domin rikici idan an san farkonsa ba a san ƙarshensa ba.

“Mun ƙara nuna musu muhimmancin haɗin kai da ke tsakanin Nijeriya da Nijar, domin tarihi ne mai nisa,” in ji Sheik Bala Lau.

Ya ƙara da cewa sojojin NIjar sun yi farin ciki tare da murnar wannan ƙoƙari sun kuma nuna za su bayar da haɗin ƙai domin a samu a tattauna.

Bala Lau ya ce akwai wasu saƙonni masu yawa da za su isar ga Shugaban Najeriya da ECOWAS Bola Ahmed Tinubu waɗanda ba za su faɗu ba a waya.

Ko da aka tambaye shi game da lokacin da sojojin ke ganin ya dace a tattauna da su sai ya ce ” a ko ina aka kira su za su je kuma ko da yaushe”.

Cikin tawagar malaman akwai Sheik Bala Lau wanda ya jagoranci tawagar ya kuma gabatar da bayani.

Akwai Sheik Ƙaribullahi Nasiru Kabara da Sheik Ibrahim Dahiru Bauchi da Farfesa Khalid Sakataren ƙungiyar Jama’atu Nasril Islam da Farfesa Salisu Shehu da dai suransu.

Nijar
Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100
  • Muhammad
    ‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan
  • Muhammad
    Cikin Shekaru 28, Kudiri Ƙasa Da 10 Sanatocin Zamfara Ta Arewa Suka Gabatar A Majalisa – Shinkafi
  • Muhammad
    2027: NNPP Ta Yi Wa Korarrun Mambobinta Afuwa, Ta Yi Alƙawarin Basu Tikitin Kai-tsaye

MASU ALAKA

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan
Manyan Labarai

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

July 15, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026
‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Next Post
Mahangar Kungiyar Gaskiya Ta Fi Kwabo A Kan Sanata Kwankwaso Da Malam Aminu Kano

Mahangar Kungiyar Gaskiya Ta Fi Kwabo A Kan Sanata Kwankwaso Da Malam Aminu Kano

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026
‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

July 15, 2026
Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo

Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo

July 15, 2026
Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

July 15, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026
Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.