ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Zamfara Ta Kaddamar Da Gangamin Kula Da Lafiya Kyauta

by Hussein Yero
3 years ago
Zamfara

Gwamnatin Jihar Zamfara ta ƙaddamar da babban gangamin duba marasa lafiya kyauta, wanda zai magance wasu cututtuka da suke addabar al’umma.

Sashe na farko na wannan shiri an fara shi ne da haɗin gwiwa da ofishin matar gwamnan jihar, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, wanda zai taimakawa mutanen da ke fama da cutar yanar ido (cataract), cutar gwaiwa (groin swellings), cutar yoyon fitsari (VVF) da kuma ilimin yadda za su kiwata lafiyarsu.

  • Yadda Tawagar Malaman Nijeriya Suka Tattauna Da Sojojin Juyin Mulkin Nijar

 

ADVERTISEMENT

Wata sanarwa da mai magana da yawun Gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar a ranar Lahadi, ta ce wannan gangami na kula da kiwon lafiya kyauta an fara shi ne ranar Juma’ar da ta gabata, inda aka samu nasarar yi wa mutum 81 aikin ido, da kuma yi wa mutum 49 aikin cutar gwaiwa.

Ya ƙara da cewa, wannan babban gangami na kiwon lafiya an tsara duk wata zai yi aiki ga masu cutar gwaiwa mutum 1, 000, za a kuma yi wa mata 200 masu fama da yoyon fitsairi aiki, haka nan za a yi aiki ga mutum 1, 000 masu fama da ciwon ido.

LABARAI MASU NASABA

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

Sanarwar ta ce: “Gwamnatin Zamfara ta kafa kwamiti ne na ƙwararru waɗanda suka yi bincike suka tsamo nau’ikan cututtukan da ke addabar mutane.

“Binciken kwamitin ne ya tabbatar da cewa, mutane sun fi buƙatar aiki kyauta a cututtuka irinsu yanar ido, cutar gwaiwa, cutar yoyon fitsari da ilimin yadda za su kiwata lafiyarsu.

“Wannan shi ne karo na farko a Jihar Zamfara da gwamnati take yin gangami don kula da kiwon lafiyar jama’a masu fama da manyan cututtuka.

“Wannan gangami ya bayar da dama ga dukkanin ‘yan jiha daga kauyuka da birane don su amfana.

“Wannan yana daga cikin ƙoƙarin gwamnatin Dauda Lawal na tabbatar da yi wa sashen kiwon lafiya garanbawul. Kuma wannan gangami na bayar da tallafin ana bada shi ne ga dukkanin jama’ar da ke ƙananan hukumomi 14.

“Ana yin wannan gangami ne a babban asibitin Gusau, babban asibitin Sarki Fahad, da kuma Asibitin Kwararru na Yariman Bakura.” In ji shi.

Zamfara
Hussein Yero
+ postsBio
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero/
    Tsaro: Gwamna Lawal Ya Jaddada Kudirin Yaki da ‘Yan Ta’adda Ba Tare Da Sulhu Ba
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero/
    Yaƙi Da Ta’addanci: Gwamnan Zamfara Ya Jinjina Wa Jami’an Tsaro Bisa Ƙwato Ɗarurruwan Shanu
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero/
    ’Yan Bindiga Sun Sace Dattawan Zamfara 50 Yayin Taron Sulhu A Cikin Daji
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero/
    Ɗan Takarar Sanata A Zamfara Ya Koka Kan Yi Wa Rayuwarsa Barazana

MASU ALAKA

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto
Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja
Labarai

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Next Post
Tottenham Na Neman Gift Orban Na Gent Domin Maye Gurbin Kane

Tottenham Na Neman Gift Orban Na Gent Domin Maye Gurbin Kane

LABARAI MASU NASABA

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.