• English
  • Business News
Thursday, October 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Zamfara Ta Mika Ta’aziyya Ga Iyalan Rundunar CPG Da ‘Yan Bindiga Suka Kashe A Jihar

by Leadership Hausa and Sulaiman
1 year ago
Zamfara

A Talatar nan ne Gwamna Dauda Lawal ya yi ta’aziyya, tare da nuna alhinin kwanton ɓaunar da aka yi wa dakarun Askarawan Zamfara na ‘Community Protection Guards’, CPG inda aka kashe wasu daga cikin su a yankin Tsafe ta jihar Zamfara. 

 

Gungun wasu ‘yan bindiga ne suka yi wa Asakarwan kwanton ɓauna a Litinin ɗin nan da ta gabata a wani shingen binciken ababen hawa da aka kafa a Ƙaramar Hukumar Tsafe.

  • Tsohon Mamban Majalisar Dokokin Kasar Sin Wu Bangguo Ya Rasu Yana Da Shekaru 84
  • Yadda Muka Sanya Tinubu Ya Soke Kwangilar Aikin Hanyar Kankara Zuwa Katsina – Ibrahim Masari 

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris ya sanya wa hannu yau a Gusau, ya bayyana cewa Gwamna Lawal ya nuna takaici da baƙin ciki bisa wannan ɗanyen aiki da waɗannan ‘yan bindiga suka aikata, waɗanda ya ce yanzu haka an ci ƙarfin su, suna hanyar guduwa ne.

 

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Saki Naira Biliyan 2.3 Ga ASUU

Sulhu Da ’Yan Bindiga Ba Tare Da Sun Ajiye Makamai Ba Tamkar Miƙa Wuya Ne – Gwamna Lawal ga Hukumomin Tsaro

Daga nan Gwamnan ya jinjina wa Asakarawan, tare da sauran jami’an tsaro bisa sadaukarwar su ta kare rayukan al’umma.

 

Gwamnan ya ce, “Na samu wani mummunan rahoton kwanton ɓaunar da ‘yan bindiga suka yi jiya a Ƙaramar Hukumar Tsafe, wanda hakan ya yi sandiyyar rasa rayukan gwarazan Askaran Zamfara mutum tara.

 

“Askarawan da aka yi wa wannan kwanton ɓauna, su ne, Nasiru Aliyu, Jabiru Hassan, Abdullahi Dangude, Bashar Bawa, Mu’azu Musa, Anas Dahiru, Anas Yakubu, Lawali Yunusa da wani mutum ɗaya.

 

“Wannan kwanton ɓauna da aka yi wa jami’an mu, aiki ne na matsorata, domin yanzu haka ƙoƙarin guduwa suke yi sakamakon ruwan wutar da su ke sha daga jami’an tsaro a duk faɗin jihar.

 

“Dakarun jami’an tsaro za su ci gaba da fafarar waɗannan ‘yan bindiga domin karya lagon su a jihar Zamfara da ma yankin baki ɗaya.

 

“Ina so a madadina da gwamnatin jihar Zamfara in miƙa ta’aziyya ta ga iyalai da dangin waɗannan gwaraza da suka rasa rayukan su. Ba za mu taɓa mantawa da sadaukarwar su ba. Ina kuma addu’ar Allah kawo sauƙi ga waɗanda suka samu raunuka.

 

“Gwamnatina a shirye ta ke don bayar da duk wata gudumawa ga iyalan waɗannan gwaraza da suka rasa rayukan su.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Asuu
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Saki Naira Biliyan 2.3 Ga ASUU

October 29, 2025
Sulhu Da ’Yan Bindiga Ba Tare Da Sun Ajiye Makamai Ba Tamkar Miƙa Wuya Ne – Gwamna Lawal ga Hukumomin Tsaro
Labarai

Sulhu Da ’Yan Bindiga Ba Tare Da Sun Ajiye Makamai Ba Tamkar Miƙa Wuya Ne – Gwamna Lawal ga Hukumomin Tsaro

October 29, 2025
majalisar kasa
Labarai

Majalisar Wakilai Ta Amince Da Bukatar Amso Bashin Dala Biliyan 2.34 A Kasuwar Jari Ta Duniya

October 29, 2025
Next Post
Sin Za Ta Dauki Jerin Matakai Don Ingiza Bunkasuwar Tattalin Arzikinta

Sin Za Ta Dauki Jerin Matakai Don Ingiza Bunkasuwar Tattalin Arzikinta

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Nazarin CGTN Ya Yabawa Gudunmuwar Sin Ga Dunkulewar Yankin Asiya Da Pasifik

Sakamakon Nazarin CGTN Ya Yabawa Gudunmuwar Sin Ga Dunkulewar Yankin Asiya Da Pasifik

October 29, 2025
Asuu

Gwamnatin Tarayya Ta Saki Naira Biliyan 2.3 Ga ASUU

October 29, 2025
Sabon Ingantaccen Hadin Gwiwar “Sin-ASEAN 3.0″ Ya Kafa Sabon Misali Na Hadin Kan Yanki

Sabon Ingantaccen Hadin Gwiwar “Sin-ASEAN 3.0″ Ya Kafa Sabon Misali Na Hadin Kan Yanki

October 29, 2025
Sulhu Da ’Yan Bindiga Ba Tare Da Sun Ajiye Makamai Ba Tamkar Miƙa Wuya Ne – Gwamna Lawal ga Hukumomin Tsaro

Sulhu Da ’Yan Bindiga Ba Tare Da Sun Ajiye Makamai Ba Tamkar Miƙa Wuya Ne – Gwamna Lawal ga Hukumomin Tsaro

October 29, 2025
An Yi Taron Tataunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Moscow, Manama, Da Budapest

An Yi Taron Tataunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Moscow, Manama, Da Budapest

October 29, 2025
majalisar kasa

Majalisar Wakilai Ta Amince Da Bukatar Amso Bashin Dala Biliyan 2.34 A Kasuwar Jari Ta Duniya

October 29, 2025
An Samu Ingantuwar Yanayin Iska Da Ruwa Cikin Watanni 9 Na Farkon Bana A Sin

An Samu Ingantuwar Yanayin Iska Da Ruwa Cikin Watanni 9 Na Farkon Bana A Sin

October 29, 2025
Kotu Ta Umarci Ƙwace Dala 49,700 Daga Tsohon Jami’in INEC

Kotu Ta Umarci Ƙwace Dala 49,700 Daga Tsohon Jami’in INEC

October 29, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kara Kyautata Tsarin Kare Muradun Al’umma A Bangaren Shari’a

Yadda Kasar Sin Ke Kara Kyautata Tsarin Kare Muradun Al’umma A Bangaren Shari’a

October 29, 2025
COAS Shaibu Ya Sha Alwashin Murƙushe ‘Yan Ta’addar Lakurawa 

COAS Shaibu Ya Sha Alwashin Murƙushe ‘Yan Ta’addar Lakurawa 

October 29, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.