ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Muka Sanya Tinubu Ya Soke Kwangilar Aikin Hanyar Kankara Zuwa Katsina – Ibrahim Masari 

by El-Zaharadeen Umar
2 years ago
Kwangilar

Baban mai taimaka wa shugaban ƙasa a kan harkokin siyasa, Hon. Ibrahim Kabir Masari, ya bayyana dalilan da ya sa suka shiga suka fita shi da gwamna Dikko Raɗɗa aka soke aikin sake gina hanyar kankara zuwa Katsina daga hannun ɗan kwangilar.

Masari, ya yi wannan kalamai ne a Katsina a lokacin bikin raba shinkafar da gwamnatin tarayya ta bai wa Jihar Katsina domin raba wa al’umma su rage raɗaɗin rayuwa da ake fama da shi.

  • Ya Kamata Wike Ya Kyale Ribas Ta Zauna Lafiya – Fubara
  • An Kashe Dorinar Ruwa A Jihar Kebbi Bayan Ta Kashe Mai-Gadin Lambun Basarake

Wannan aikin hanyar mai tsawon kilo mita 170 da ta taso daga marabar kankara zuwa Katsina ta haɗa ƙananan hukumomi bakwai da yawansu manoma ne sannan suna fuskantar matsalar tsaro daga ‘yan bindiga

ADVERTISEMENT

Kamar yadda alkaluma suka nuna aikin wannan hanya zai ratsa kananan hukumomi guda 7 da suka haɗa da Malumfashi da Kankara da Ɗanmusa da Safana da Dutsinma da Kurfi da kuma Ɓatagarawa a Jihar Katsina.

Lokaci da aka ba da aikin wannan hanya al’umma da dama sun nuna farin cikinsu da samun wannan aiki wanda suka bayyana cewa zai taimaka wa al’umma musamman manoma sannan zai taimaka wa jami’an tsaro wajen kai ɗauki a yayin da aka kai hari wuce gona da iri.

LABARAI MASU NASABA

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sai dai kwatsam aka ji labarin ministan ayyuka na Nijeriya ya soke wannan kwangila daga hannun kamfanin da aka bai wa ita daga farko duk da cewa an fara aikin.

Shi ma a nasa jawabin babban mai taimaka wa shugaban kasa a harkokin siyasa Hon Ibrahim Masari ya bayyana wasu hanyoyi da gwamnatin tarayya ta bada aikinsu, sai dai ya ce hanyar kankara zuwa Katsina ba a ɗora ƙwarya a gurbinta ba shi ya sa suka je wajen shugaban ƙasa domin ya soke ta.

Ana dai zargin cewa wani jigo ne a jam’iyar PDP a Katsina kuma ɗaya daga cikin yaran Ministan Abuja, Nyesom Wike aka bai wa kwangilar aikin hanyar tun farko, lamarin da bai yi masu daɗi ba, inda suka shiga suka fita aka dakatar da aikin, wanda yanzu ba a san matsayin da aikin hanyar yake ciki ba.

Yanzu dai abin jira a gani shi ne, ko shugaban ƙasa zai sake ba da aikin hanyar a wani kamfanin da gwamna Dikko Raɗɗa da Hon. Ibrahim Kabir Masari suke so ko kuwa shike nan ruwa ta sha?

Kwangilar
El-Zaharadeen Umar
+ postsBio
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Mutum 1,000 Daga Jam’iyyar ADC Sun Koma PDP A Jihar Katsina
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Tinubu Ya Amince Da Ɗaukar Ma’aikatan Gandun Daji 1,000 Domin Matsalolin Tsaro A Katsina
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Matsalar Tsaro:Yadda Sabbin Matakan Gwamnati Ke Shafar Walwalar Al’ummar Jihar Katsina
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

MASU ALAKA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba
Labarai

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi
Labarai

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Next Post
‘Yan Bindiga Sun Sace Likitan Mata A Zamfara

'Yan Bindiga Sun Sace Likitan Mata A Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.