• English
  • Business News
Sunday, June 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Zamfara Za Ta Zamanantar Da Asibitin Kwararru Na Yeriman Bakura Da Daga Darajarsa  

by Leadership Hausa
1 year ago
in Labarai, Kananan Labarai
0
Gwamnatin Zamfara Za Ta Zamanantar Da Asibitin Kwararru Na Yeriman Bakura Da Daga Darajarsa  
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan jihar Zamfara Dauda Lawal ya amince da shirin gyara, tare da sake inganta asibitin ƙwararru na Yeriman Bakura da ke Gusau domin magance ƙalubalen da ake fuskanta na samar da ingantaccen kiwon lafiya a Jihar Zamfara.

Gwamnan ya amince da aikin gyaran asibitin ƙwararrun ne a ranar Litinin a taron Majalisar Zartarwa karo na sha tara a gidan gwamnati da ke Gusau.

A wata sanarwa da mai magana da yawun Gwamnan, Sulaiman Bala Idris ya fitar, ya bayyana cewa za a fara aikin gyaran ne nan take, kuma ana sa ran gyaran zai mayar da asibitin zuwa babbar cibiyar lafiya ta zamani kuma mai isassun kayan aiki irin na zamani.

A cewar sanarwar, an yanke wannan shawarar ne a daidai lokacin da aka ayyana dokar ta-ɓaci a ɓangaren kiwon lafiya na Zamfara.

  • Sojoji Sun Hallaka Kasurgumin Dan Bindiga, Kachalla Damina Da Yaransa

Ya ce, “A jiya lokacin da Gwamna Lawal ya jagoranci zaman Majalisar Zartarwa, ya amince da yadda za a yi gaggawar gyara asibitin ƙwararru na Yeriman Bakura.

Labarai Masu Nasaba

FIRS Ta Umarci A Rika Bude Ofishoshin Karbar Haraji A karshen Mako

EFCC Ta Gurfanar Da Wasu Kamfanoni Biyu Gaban Kuliya Bisa Damfarar Naira Miliyan 80

“Asibitin ƙwararru na jihar ya daɗe a lalace kuma ba shi da isassun kayan aikin kiwon lafiya. Hakan ke tilasta majiyyata yin tattaki zuwa Sakkwato ko Kaduna domin samun wankin ƙoda da sauran gwaje-gwajen lafiya.

“Alhaji Mustapha Falaki, Shugaban Cibiyar Kiwon Lafiya ta Minjirya, ya gabatar wa majalisar koke kan halin da asibitin ƙwararrun ke ciki a halin yanzu da kuma matakan da za a ɗauka na sake fasalin cibiyar.

“A cikin shirin gyaran asibitin, za a gina sabbin gine-gine da wuraren kiwon lafiya, za a samar da na’urorin kiwon lafiya, sannan a horar da masu amfani da na’urorin don mayar da asibitin ƙwararru ya zama wurin kiwon lafiya na zamani da ingantattun kayan aikin da za su samar da ingantacciyar kiwon lafiya ga al’ummar jihar.

A yayin taron majalisar, an tattauna batutuwa masu muhimmanci da dama. Ɗaya daga cikin manyan batutuwan da aka tattauna shi ne manufofin kyautata jin daɗin jama’a da zamnatakewa a jihar. Wannan manufar na da nufin haɗa kan al’umma daban-daban da inganta walwala waɗanda suka dace da hangen nesan Jihar Zamfara a matsayin ɗaya daga cibiyar ci gaban al’ummar Nijeriya. Manufar ita ce tsare-tsare don taimakawa wajen jagorantar zuba jari a harkokin gwamnati da masu zaman kansu don inganta jin daɗin jama’a da zamantakewarsu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Asibitin KwararruGusauKayan AikiYeriman BakuraZamaniZamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Yi Bikin Mu’Amalar Matasa Da Yaran Sin Da Amurka A Birnin Beijing

Next Post

Fahimtar Juna Tsakanin Matasan Sin Da Amurka Zai Haskaka Makomar Dangantakar Kasashen Biyu

Related

FIRS Ta Umarci A Rika Bude Ofishoshin Karbar Haraji A karshen Mako
Labarai

FIRS Ta Umarci A Rika Bude Ofishoshin Karbar Haraji A karshen Mako

7 hours ago
EFCC Ta Gurfanar Da Wasu Kamfanoni Biyu Gaban Kuliya Bisa Damfarar Naira Miliyan 80
Labarai

EFCC Ta Gurfanar Da Wasu Kamfanoni Biyu Gaban Kuliya Bisa Damfarar Naira Miliyan 80

9 hours ago
Bam Ya Fashe A Kano, Ya Kashe Mutane 5
Manyan Labarai

Bam Ya Fashe A Kano, Ya Kashe Mutane 5

15 hours ago
Ƴan Ta’adda Sun Kashe Matafiya 12 A Filato 
Manyan Labarai

Ƴan Ta’adda Sun Kashe Matafiya 12 A Filato 

15 hours ago
Kuratan Sojoji 1,196 Aka Yaye A Makarantar Horar Da Sojoji Ta Zariya
Labaran Kasuwanci

Kuratan Sojoji 1,196 Aka Yaye A Makarantar Horar Da Sojoji Ta Zariya

16 hours ago
Minista Ya Yaba Wa Hafsoshin Soji Kan Cigaban Da Aka Samu A Fannin Tsaron Ƙasa
Labarai

Minista Ya Yaba Wa Hafsoshin Soji Kan Cigaban Da Aka Samu A Fannin Tsaron Ƙasa

18 hours ago
Next Post
Amurka

Fahimtar Juna Tsakanin Matasan Sin Da Amurka Zai Haskaka Makomar Dangantakar Kasashen Biyu

LABARAI MASU NASABA

FIRS Ta Umarci A Rika Bude Ofishoshin Karbar Haraji A karshen Mako

FIRS Ta Umarci A Rika Bude Ofishoshin Karbar Haraji A karshen Mako

June 21, 2025
CMG Ya Ja Hankulan Baki A Dandalin Tattaunawar Tattalin Arziki Na Kasa Da Kasa Na St. Petersburg Karo Na 28 

CMG Ya Ja Hankulan Baki A Dandalin Tattaunawar Tattalin Arziki Na Kasa Da Kasa Na St. Petersburg Karo Na 28 

June 21, 2025
Yankin Taiwan Ya Yi Taron Bikin Bauta Na Kakan Gargajiyar Sin Fuxi

Yankin Taiwan Ya Yi Taron Bikin Bauta Na Kakan Gargajiyar Sin Fuxi

June 21, 2025
EFCC Ta Gurfanar Da Wasu Kamfanoni Biyu Gaban Kuliya Bisa Damfarar Naira Miliyan 80

EFCC Ta Gurfanar Da Wasu Kamfanoni Biyu Gaban Kuliya Bisa Damfarar Naira Miliyan 80

June 21, 2025
Sin A Shirye Take Ta Yi Aiki Da Rasha Don Daukaka Amincewar Juna Ta Fuskar Siyasa Da Karfafa Muradun Juna

Sin A Shirye Take Ta Yi Aiki Da Rasha Don Daukaka Amincewar Juna Ta Fuskar Siyasa Da Karfafa Muradun Juna

June 21, 2025
Jigawa Za Ta Samar Da Kashi 25 Na Shinkafar Da Nijeriya Ke Bukata – Hon Abdurahman 

Jigawa Za Ta Samar Da Kashi 25 Na Shinkafar Da Nijeriya Ke Bukata – Hon Abdurahman 

June 21, 2025
Tottenham Da West Ham Sun Nuna Sha’awar Daukar Dan Wasan Nijeriya Raphael Onyedika

Tottenham Da West Ham Sun Nuna Sha’awar Daukar Dan Wasan Nijeriya Raphael Onyedika

June 21, 2025
Wakilin Sin Ya Yi Kira A Yayyafa Ruwa Ga Rikicin Isra’ila Da Iran

Wakilin Sin Ya Yi Kira A Yayyafa Ruwa Ga Rikicin Isra’ila Da Iran

June 21, 2025
Kungiyar Gamayyar Gidajen Rediyo Da Telabijin Na Kasashen Afirka Ta Ba CMG Kyautar Karramawa

Kungiyar Gamayyar Gidajen Rediyo Da Telabijin Na Kasashen Afirka Ta Ba CMG Kyautar Karramawa

June 21, 2025
Bam Ya Fashe A Kano, Ya Kashe Mutane 5

Bam Ya Fashe A Kano, Ya Kashe Mutane 5

June 21, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.