• English
  • Business News
Saturday, July 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Zamfara Za Ta Zamanantar Da Asibitin Kwararru Na Yeriman Bakura Da Daga Darajarsa  

by Leadership Hausa
1 year ago
in Labarai, Kananan Labarai
0
Gwamnatin Zamfara Za Ta Zamanantar Da Asibitin Kwararru Na Yeriman Bakura Da Daga Darajarsa  
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan jihar Zamfara Dauda Lawal ya amince da shirin gyara, tare da sake inganta asibitin ƙwararru na Yeriman Bakura da ke Gusau domin magance ƙalubalen da ake fuskanta na samar da ingantaccen kiwon lafiya a Jihar Zamfara.

Gwamnan ya amince da aikin gyaran asibitin ƙwararrun ne a ranar Litinin a taron Majalisar Zartarwa karo na sha tara a gidan gwamnati da ke Gusau.

A wata sanarwa da mai magana da yawun Gwamnan, Sulaiman Bala Idris ya fitar, ya bayyana cewa za a fara aikin gyaran ne nan take, kuma ana sa ran gyaran zai mayar da asibitin zuwa babbar cibiyar lafiya ta zamani kuma mai isassun kayan aiki irin na zamani.

A cewar sanarwar, an yanke wannan shawarar ne a daidai lokacin da aka ayyana dokar ta-ɓaci a ɓangaren kiwon lafiya na Zamfara.

  • Sojoji Sun Hallaka Kasurgumin Dan Bindiga, Kachalla Damina Da Yaransa

Ya ce, “A jiya lokacin da Gwamna Lawal ya jagoranci zaman Majalisar Zartarwa, ya amince da yadda za a yi gaggawar gyara asibitin ƙwararru na Yeriman Bakura.

Labarai Masu Nasaba

A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

Biyan ‘Yan Fansho Naira Biliyan 22: NUP Da NLC Sun Bukaci A Yi Koyi Da Gwamna Abba

“Asibitin ƙwararru na jihar ya daɗe a lalace kuma ba shi da isassun kayan aikin kiwon lafiya. Hakan ke tilasta majiyyata yin tattaki zuwa Sakkwato ko Kaduna domin samun wankin ƙoda da sauran gwaje-gwajen lafiya.

“Alhaji Mustapha Falaki, Shugaban Cibiyar Kiwon Lafiya ta Minjirya, ya gabatar wa majalisar koke kan halin da asibitin ƙwararrun ke ciki a halin yanzu da kuma matakan da za a ɗauka na sake fasalin cibiyar.

“A cikin shirin gyaran asibitin, za a gina sabbin gine-gine da wuraren kiwon lafiya, za a samar da na’urorin kiwon lafiya, sannan a horar da masu amfani da na’urorin don mayar da asibitin ƙwararru ya zama wurin kiwon lafiya na zamani da ingantattun kayan aikin da za su samar da ingantacciyar kiwon lafiya ga al’ummar jihar.

A yayin taron majalisar, an tattauna batutuwa masu muhimmanci da dama. Ɗaya daga cikin manyan batutuwan da aka tattauna shi ne manufofin kyautata jin daɗin jama’a da zamnatakewa a jihar. Wannan manufar na da nufin haɗa kan al’umma daban-daban da inganta walwala waɗanda suka dace da hangen nesan Jihar Zamfara a matsayin ɗaya daga cibiyar ci gaban al’ummar Nijeriya. Manufar ita ce tsare-tsare don taimakawa wajen jagorantar zuba jari a harkokin gwamnati da masu zaman kansu don inganta jin daɗin jama’a da zamantakewarsu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Asibitin KwararruGusauKayan AikiYeriman BakuraZamaniZamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Yi Bikin Mu’Amalar Matasa Da Yaran Sin Da Amurka A Birnin Beijing

Next Post

Fahimtar Juna Tsakanin Matasan Sin Da Amurka Zai Haskaka Makomar Dangantakar Kasashen Biyu

Related

A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya
Labarai

A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

5 hours ago
Biyan Tukuici: Gwamna Yusuf Ya Ƙaddamar Da Tallafin Naira 50,000 Ga Mata 5,200 Duk Wata A Kano
Labarai

Biyan ‘Yan Fansho Naira Biliyan 22: NUP Da NLC Sun Bukaci A Yi Koyi Da Gwamna Abba

5 hours ago
Kasar Sin Ta Nuna Alhinin Rasuwar Tsohon Shugaban Nijeriya Buhari
Labarai

Za A Dinga Tunawa Da Buhari A Matsayin Waliyyi A Siyasar Nijeriya —Dakta Zangina

6 hours ago
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Manyan Labarai

Tinubu Ya Nada Ɗan Babangida A Matsayin Shugaban Bankin Manoma

7 hours ago
‘Yan Kasuwa Na Shirin Yi Wa Dangote Zanga-zanga Kan Rage Farashin Gas
Labarai

‘Yan Kasuwa Na Shirin Yi Wa Dangote Zanga-zanga Kan Rage Farashin Gas

7 hours ago
Lai Ching-Te Bai Cancanci Zama Jagoran Yankin Taiwan Ba
Ra'ayi Riga

Lai Ching-Te Bai Cancanci Zama Jagoran Yankin Taiwan Ba

8 hours ago
Next Post
Amurka

Fahimtar Juna Tsakanin Matasan Sin Da Amurka Zai Haskaka Makomar Dangantakar Kasashen Biyu

LABARAI MASU NASABA

Dangote

Dalilin Da Ya Sa Dangote Ya Jinjina Wa Hukumar NPA

July 18, 2025
Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

July 18, 2025
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

July 18, 2025
Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

July 18, 2025
majalisar kasa

Kirkirar Sabbin Jihohi Da Kananan Hukumomi Sun Dabaibaye Sauraron Jin Ra’ayoyin Gyaran Tsarin Mulki

July 18, 2025
Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Zambia Da Ci 5-0

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Zambia Da Ci 5-0

July 18, 2025
Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

July 18, 2025
A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

July 18, 2025
Biyan Tukuici: Gwamna Yusuf Ya Ƙaddamar Da Tallafin Naira 50,000 Ga Mata 5,200 Duk Wata A Kano

Biyan ‘Yan Fansho Naira Biliyan 22: NUP Da NLC Sun Bukaci A Yi Koyi Da Gwamna Abba

July 18, 2025
Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria

July 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.