• English
  • Business News
Friday, October 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnonin Arewa Maso Gabas Sun Fara Taronsu Karo Na 11 A Yobe

by Muhammad Maitela and Sulaiman
5 months ago
Arewa

Gwamnonin Arewa Maso Gabas sun fara taron kungiyar gwamnonin, a karo na 11, wanda aka fara da kimanin karfe 11:00 na safiyar ranar Alhamis, a Damaturu, babban birnin jihar Yobe. 

 

Taron ya samu halartar gwamnonin yankin da suka hada da Ahmad Umar Fintiri, Adamawa; Farfesa Babagana Umara Zulum, Borno da mataimakin Gwamna, Hon. Auwalu Jatau, Bauchi.

  • Binciken Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Ya Nuna Gazawar Gwamnatin Trump Kwanaki 100 Bayan Kama Aiki
  • Mutum 20,000 Sun Nemi Gurbin Aikin Mutum 4,000 Cikin Kwana Ɗaya A Adamawa

Sa’ilin da yake jawabi kan taron, shugaban kungiyar gwamnonin yankin, kuma Gwamnan jihar Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum, ya jaddada bukatar daukin gaggawa wajen magance matsalolin da yankin ke fuskanta, musamman a fannonin karancin abinci, tabarbarewar harkokin sufuri, kiwon lafiya, sannan uwa uba, koma bayan tattalin arziki.

 

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Motar Hilux Ɗin Da Aka Sace A Kano A Hanyar Zuwa Nijar

Jami’an Tsaro Sun Cafke Ɓarayin Kayayyakin Turakun Wutar Lantarki Na Hanyar Mando Zuwa Jos

Gwamnan Zulum ya yi tsokaci dangane da yadda tabarbarewar harkokin tsaro ke ci gaba da zafafa a yankin, yayin da kuma ya yaba wa kokarin sojojin Nijeriya, inda ya ce, “Ina kira gareku, ku ci gaba da yaki da yan ta’adda har sai mun kawo karshen wannan matsalar.”

 

“Dawowar hare-haren yan ta’adda a cikin jihohinmu wani al’amari ne mai matukar tayar da hankali wanda hakan zai iya wargaza nasarorin da aka samu a fagen yaki da matsalolin tsaro a yankin. Ina mai bayar da shawarar cewa, sojojinmu su fadada sabbin dabarun da suke dasu wajen dakile farmakin yan ta’adda.”

 

Gwamna Zulum ya ce, “kangin talaucin da yankinmu yake fuskanta, abin tsoro ne, kuma ya zama dole mu dauki ingantattun matakai don magance wannan kalubale. Mu fahimci cewa talauci babbar barazana ne ga tattalin arziki, wanda zai iya shafi zamantakewa.”

 

“A kokarin nemo madafa, noma kadai ba zai kasance mafita ba, a yaki da talauci. Dole mu kara mayar da hankali kan samar da kyakkyawan yanayi don kafa kananan da matsakaitan masana’antu a yankin mu.”

 

“Abin ya hada da sa hannun jari a kayayyakin more rayuwa, bayar da fifiko wajen zuba jari mai yawa ga kamfanoni masu zaman kansu, don habaka kasuwanci da kirkire-kirkire.”

 

Ya ce dole ne su yi aiki don rage talauci ta hanyar samar da ayyukan yi, bunkasa tunani tare da tallafa wa kananan masana’amtu, bunkasa kasuwanci, ta fuskar habaka masana’antu, don fadada tattalin arziki tare da samar da dama ga matasa.

 

Da farko, mai masaukin bakin taron, kuma Gwamnan jihar Yobe, Mai Mala Buni, a lokacin da yake jawabin bude taron, ya ce a matsayinsu na Gwamnonin yankin za su yi amfani da dandamalin wajen yanke shawarar da za ta kai ga samar da mafita ga matsalolin da yankin yake fuskanta.

 

“Irin karfin niyya da kyakkyawan kudurori, shawara mai nagarta, da daukakar mataki a cikin gaggawa, wanda shugabanin mu da suka gabata, ko shakka babu sun haskaka makomar yankin Arewa Masu Gabas.

 

“Yau ma gashi mun taru domin daukar sabbin kudurori da shawarwari nagari, don bin sawun magabatanmu wajen kawo ci gaba a yankinmu.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

‘Yansanda Sun Kama Motar Hilux Ɗin Da Aka Sace A Kano A Hanyar Zuwa Nijar
Labarai

‘Yansanda Sun Kama Motar Hilux Ɗin Da Aka Sace A Kano A Hanyar Zuwa Nijar

October 9, 2025
TCN
Labarai

Jami’an Tsaro Sun Cafke Ɓarayin Kayayyakin Turakun Wutar Lantarki Na Hanyar Mando Zuwa Jos

October 9, 2025
Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI
Labarai

Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI

October 9, 2025
Next Post
Kano

Ranar Ma'aikata: Gwamnan Kano Ya Biya Basussukan Fansho, Ya ƙirƙiro Sabbin Ma'aikatu

LABARAI MASU NASABA

An Jinjinawa Tallafin Kamfanonin Sin Ga Tsarin Bunkasa Masana’antun Senegal

An Jinjinawa Tallafin Kamfanonin Sin Ga Tsarin Bunkasa Masana’antun Senegal

October 9, 2025
Masu Kallon Fina-Finai Na Sin Sun Gamsu Da Fina-Finan Da Aka Gabatar A Lokacin Hutun Bikin Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar Sin Ta 2025

Masu Kallon Fina-Finai Na Sin Sun Gamsu Da Fina-Finan Da Aka Gabatar A Lokacin Hutun Bikin Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar Sin Ta 2025

October 9, 2025
‘Yansanda Sun Kama Motar Hilux Ɗin Da Aka Sace A Kano A Hanyar Zuwa Nijar

‘Yansanda Sun Kama Motar Hilux Ɗin Da Aka Sace A Kano A Hanyar Zuwa Nijar

October 9, 2025
Sin Na Ci Gaba Da Goyon Bayan Kawo Karshen Rikicin Gaza

Sin Na Ci Gaba Da Goyon Bayan Kawo Karshen Rikicin Gaza

October 9, 2025
TCN

Jami’an Tsaro Sun Cafke Ɓarayin Kayayyakin Turakun Wutar Lantarki Na Hanyar Mando Zuwa Jos

October 9, 2025
An Yi Tafiye-tafiye Miliyan 16.34 Da Suka Shafi Shiga Da Fita Daga Kasar Sin Yayin Hutun Kwanaki 8 Na Kasar 

An Yi Tafiye-tafiye Miliyan 16.34 Da Suka Shafi Shiga Da Fita Daga Kasar Sin Yayin Hutun Kwanaki 8 Na Kasar 

October 9, 2025
Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI

Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI

October 9, 2025
Duniya Ta Kara Ganin Bunkasuwar Sin a Lokacin Hutun Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar

Duniya Ta Kara Ganin Bunkasuwar Sin a Lokacin Hutun Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar

October 9, 2025
Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC

Batun Umarnin Kotu Na Kama Tsohon Shugaban INEC Ƙage Ne Kawai – Shugaban Jam’iyyar AA 

October 9, 2025
An Samu Karuwar Sayayya Yayin Hutun Bikin Kafuwar Kasar Sin

An Samu Karuwar Sayayya Yayin Hutun Bikin Kafuwar Kasar Sin

October 9, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.