• English
  • Business News
Friday, September 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnonin Arewa Sun Amince Da Kafa Ƴansandan Jihohi: Ko Hakan Zai Yi Tasiri Ga Sha’anin Tsaro?

by Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
3 hours ago
in Uwargida Sarautar Mata
0
Gwamnonin Arewa Sun Amince Da Kafa Ƴansandan Jihohi: Ko Hakan Zai Yi Tasiri Ga Sha’anin Tsaro?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Batun kafa Rundunar Ƴan Sanda mallakar gwamnatocin jihohi ya dade yana ɗaukar hankalin al’umma, inda ake tafka muhawara kan alfanu da rashin alfanun ƙirƙiro da jami’an da manufarsu ita ce taimakawa wajen kawar da matsalolin tsaro da suka ƙi ƙarewa.

Masu ruwa da tsaki sun buƙaci kafa ƴan sandan jihohi ne saboda yadda taɓarɓarewar sha’anin tsaro a yankin Arewa ya kai ƙololuwar mataki, ta yadda ƴan ta’adda ke cin karen su ba babbaka ta hanyar yi wa al’umma kisan ƙare dangi, garkuwa da mutane, ƙone garuruwa, sanya dubun-dubatar jama’a gudun hijira da hanawa ɗimbin al’umma noma. Rahoton ƙididdigar 2024–2025 ya nuna Rundunar Ƴan Sanda a Nijeriya na da jami’ai dubu 370,000 tare da shirin ɗaukar ƙarin jami’ai dubu 30,000 a kowace shekara zuwa shekaru shida, domin a kai ga ƴan sanda 650,000 a faɗin ƙasa. Sai dai adadin yawan ƴan sanda a Nijeriya ya saɓa da shawarar Majalisar Ɗinkin Duniya na aƙalla jami’i ɗaya ya riƙa kula da mutane 450.

  • Yadda Tinubu Ya Shawo Kan Gwamnonin Arewa Wajen Amincewa Da Kafa Ƴansandan Jihohi
  • Tinubu Ya Bayar Da Umarni Karya Farashin Kayan Abinci A Nijeriya

Shugaba Bola Ahmad Tinubu ya bayyana cewa kafa ƴan sandan jihohi ba zaɓi ba ne, wajibi ne domin ceto rayukan al’umma da dukiyoyinsu daga hannun makasa. A kwanan nan Ƙungiyar Gwamnonin Arewa ta tabbatar da cikakken goyon bayanta ga kafa Rundunar Ƴan Sanda a jihohi a matsayin mataki na kawo ƙarshen matsalar tsaro da ta dabaibaye yankin Arewa. Kakakin ƙungiyar, Gwamnan Gombe Muhammad Inuwa Yahaya, ya ce Gwamnonin Arewa 19 sun amince a kafa ƴan sandan jihohi tare da haɗa su cikin sauran hukumomin tsaro wajen kawar da matsalolin tsaron ƙasa.

Sai dai, masana tsaro da ƙungiyoyin dattawa sun yi kashedi kan yiwuwar wasu gwamnoni su yi amfani da rundunar don muzgunawa abokan adawa. Farfesa Tukur Baba ya nuna damuwa kan batun kuɗin gudanarwa da yiwuwar biyan albashi, yana tambaya: “Mene ne zai faru idan aka kasa biyan jami’an da ke riƙe da makamai?” Tsohon Sufeto Janar na ƴan sanda Mike Okiro ma ya bayyana cewa kafa ƴan sandan jihohi ba shi ne mafita ba, yana mai jaddada cewa matsalar tsaro a Nijeriya ta samo asali ne daga ƙarancin kuɗi, kayan aiki da jami’ai.

A gefe guda, wasu shugabanni sun yaba da wannan mataki. Ƙungiyoyi kamar Dattawan Arewa, ACF, da Afenifere sun bayyana goyon bayansu, suna mai cewa kafa ƴan sandan jihohi na da matuƙar muhimmanci a wannan lokaci. Sai dai wasu, kamar tsohon Sanata Shehu Sani da Anthony Sani, sun nuna cewa akwai barazanar amfani da rundunar wajen cimma muradun siyasa.

Labarai Masu Nasaba

Ko Kin San… Matsalolin Mahaifa Da Suke Hana Haihuwa 

Ki Bar Auna Yadda Mijinki Yake Miki Da Yadda Wani Yake Wa Matarsa


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ArewaBuhari TinubuPoliceƳansanda
ShareTweetSendShare
Previous Post

Nijeriya Na Shirin Samun Jarin Dala Biliyan 60 A Fannin Gas – Shugaban NNPCL

Next Post

Ba Lallai Ne FIFA Ta Cirewa Afrika Ta Kudu Maki 3 Ba – Rayond Hack

Related

aure
Uwargida Sarautar Mata

Ko Kin San… Matsalolin Mahaifa Da Suke Hana Haihuwa 

2 months ago
Ki Bar Auna Yadda Mijinki Yake Miki Da Yadda Wani Yake Wa Matarsa
Uwargida Sarautar Mata

Ki Bar Auna Yadda Mijinki Yake Miki Da Yadda Wani Yake Wa Matarsa

2 months ago
Ko Kin San… Yadda Ake Magance Cutar Sanyi Ga Ma’aurata (Infection)
Uwargida Sarautar Mata

Ko Kin San… Yadda Ake Magance Cutar Sanyi Ga Ma’aurata (Infection)

2 months ago
Wasu Abubuwa Da Ke Sa Maza Hana Mata Fita Unguwa (Uwargida)
Uwargida Sarautar Mata

Kula Da Kanki Bayan Haihuwa Abu Ne Muhimmi

3 months ago
aure
Uwargida Sarautar Mata

Kar Ki Bari Naman Sallah Ya Kashe Miki Aure Yar’uwa

3 months ago
Arewa
Uwargida Sarautar Mata

Hanyoyi Goma Sha Daya Da Mace Za Ta Bi Domin Janyo Hankalin Mijinta

6 months ago
Next Post
Ba Lallai Ne FIFA Ta Cirewa Afrika Ta Kudu Maki 3 Ba – Rayond Hack

Ba Lallai Ne FIFA Ta Cirewa Afrika Ta Kudu Maki 3 Ba – Rayond Hack

LABARAI MASU NASABA

Ahlul Faidhati Mai Diwani Group

Yadda Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Suka Yi Maulidin Cikar Annabi (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa 

September 12, 2025
Ƙungiyar Ƙwadago Ta Ba Gwamnati Wa’adin Kwana 14 Ta Janye Sabon Harajin Man Fetur

Ƙungiyar Ƙwadago Ta Ba Gwamnati Wa’adin Kwana 14 Ta Janye Sabon Harajin Man Fetur

September 12, 2025
Likitoci Masu Neman Ƙwarewa Sun Fara Yajin Aikin Ƙasa A Nijeriya

Likitoci Masu Neman Ƙwarewa Sun Fara Yajin Aikin Ƙasa A Nijeriya

September 12, 2025
Ba Lallai Ne FIFA Ta Cirewa Afrika Ta Kudu Maki 3 Ba – Rayond Hack

Ba Lallai Ne FIFA Ta Cirewa Afrika Ta Kudu Maki 3 Ba – Rayond Hack

September 12, 2025
Gwamnonin Arewa Sun Amince Da Kafa Ƴansandan Jihohi: Ko Hakan Zai Yi Tasiri Ga Sha’anin Tsaro?

Gwamnonin Arewa Sun Amince Da Kafa Ƴansandan Jihohi: Ko Hakan Zai Yi Tasiri Ga Sha’anin Tsaro?

September 12, 2025
Nijeriya Na Shirin Samun Jarin Dala Biliyan 60 A Fannin Gas – Shugaban NNPCL

Nijeriya Na Shirin Samun Jarin Dala Biliyan 60 A Fannin Gas – Shugaban NNPCL

September 12, 2025
Yadda Tinubu Ya Shawo Kan Gwamnonin Arewa Wajen Amincewa Da Kafa Ƴansandan Jihohi

Yadda Tinubu Ya Shawo Kan Gwamnonin Arewa Wajen Amincewa Da Kafa Ƴansandan Jihohi

September 12, 2025
Rashin Wutar Lantarki: Masana Sun Nuna Damuwa Kan Asarar Dala Biliyan 29 Da Ƙananan Masana’antu Ke Yi

Rashin Wutar Lantarki: Masana Sun Nuna Damuwa Kan Asarar Dala Biliyan 29 Da Ƙananan Masana’antu Ke Yi

September 12, 2025
Buƙatar Daƙile Yawan Ɓacewar Mutane A Nijeriya

Buƙatar Daƙile Yawan Ɓacewar Mutane A Nijeriya

September 12, 2025
Tattalin Arzikin Sin Babban Ginshiki Ne Na Karuwar Tattalin Arzikin Duniya

Tattalin Arzikin Sin Babban Ginshiki Ne Na Karuwar Tattalin Arzikin Duniya

September 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.