ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, December 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnonin Arewa Sun Nemi A Gaggauta Ceto Ƴan Makaranta Mata Ta Kebbi Da Aka Yi Garkuwa Da Su

by Khalid Idris Doya and Sulaiman
1 month ago
kebbi

Ƙungiyar Gwamnonin Jihohin Arewa (NSGF) ta yi kakkausar suka kan harin da aka kai Makarantar Ƴan Mata ta Gwamnati (GGCSS) da ke garin Maga a ƙaramar hukumar Danko/Wasagu ta Jihar Kebbi, wanda ya kai ga sace ɗalibai da dama tare da kashe wasu jami’ai.

 

Da ya ke tsokaci kan wannan mummunan lamari ta cikin sanarwar da Malam Ismaila Uba Misilli, Babban Daraktan Yaɗa Labarun Gwamnan Jihar Gombe ya fitar, shugaban ƙungiyar kuma Gwamnan Jihar Gombe Muhammadu Inuwa Yahaya, ya bayyana lamarin a matsayin abin takaici.

ADVERTISEMENT
  • Sin: Ya Zama Wajibi A Dakile Mummunan Yanayin Wanzuwar Tashe-tashen Hankula Da Yunwa
  • Wani Mai Taɓin Ƙwaƙwalwa Ya Kashe Soja A Legas

Gwamna Inuwa ya kuma ce sace yaran rashin hankali ne da ba za a amince da shi ba, tare da bayyana cewa ci gaba da kai hare-hare a makarantu yana babbar barazana ga zaman lafiyan Arewa da makomar ilimi a ƙasar nan.

 

LABARAI MASU NASABA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Gwamna Inuwa Yahaya, a madadin takwarorinsa na ƙungiyar, ya jajantawa gwamnati da al’ummar Jihar Kebbi musamman iyalan ɗaliban da aka sace da kuma waɗanda suka rasa rayukansu a harin.

 

Ya kuma bai wa Gwamna Nasir Idris na Jihar ta Kebbi tabbacin haɗin kai da goyon bayan ƙungiyar a wannan mawuyacin lokaci.

 

Gwamna Yahaya ya ce dole ne makarantu su zama wuraren koyo, ba wai wuraren tashin hankali ba, yana mai gargaɗin cewa ci gaba da kai hare-hare kan cibiyoyin ilimi yana barazana ga nasarorin da aka samu wajen inganta harkokin karatu a makarantu da kuma daƙile matsalar yaran da basa zuwa makaranta a yankin.

 

Ya nuna matuƙar damuwa kan irin halin da ƴan matan makarantar da aka sacen ke ciki, ya kuma yi ƙira da a gaggauta gudanar da wani shiri na haɗin gwiwa da jami’an tsaro don ganin an ceto su da kuma kama waɗanda suka aikata laifin.

 

Da ya ke jaddada ƙudurin ƙungiyar gwamnonin na Arewa na haɗa kai da gwamnatin tarayya da hukumomin tsaro, Gwamna Yahaya ya bayyana cewa, tsaro, ilimi da walwalar matasan Nijeriya na ci gaba da zama babban muradin ƙungiyar.

 

Shugaban ƙungiyar ta gwamnonin Arewa ya yi addu’ar Allah ya dawo da ‘yan matan makarantar da aka sace da wuri lafiya, ya kuma jajantawa iyalan waɗanda abin ya shafa, tare da yin ƙira ga al’umma su kasance cikin shiri da haɗin kai da jami’an tsaro a ƙoƙarin da suke na kawar da miyagun laifuka a yankin.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja
Manyan Labarai

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta
Manyan Labarai

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka
Ra'ayi Riga

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Next Post
Ba Za A Amince Da Sake Farfado Da Ra’ayin Nuna Karfin Soja Na Japan Ba

Ba Za A Amince Da Sake Farfado Da Ra’ayin Nuna Karfin Soja Na Japan Ba

LABARAI MASU NASABA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

December 21, 2025
Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

December 21, 2025
Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

December 21, 2025
Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

December 21, 2025
An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.