ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnonin Arewa Sun Nemi A Gaggauta Ceto Ƴan Makaranta Mata Ta Kebbi Da Aka Yi Garkuwa Da Su

by Khalid Idris Doya and Sulaiman
10 months ago
kebbi

Ƙungiyar Gwamnonin Jihohin Arewa (NSGF) ta yi kakkausar suka kan harin da aka kai Makarantar Ƴan Mata ta Gwamnati (GGCSS) da ke garin Maga a ƙaramar hukumar Danko/Wasagu ta Jihar Kebbi, wanda ya kai ga sace ɗalibai da dama tare da kashe wasu jami’ai.

 

Da ya ke tsokaci kan wannan mummunan lamari ta cikin sanarwar da Malam Ismaila Uba Misilli, Babban Daraktan Yaɗa Labarun Gwamnan Jihar Gombe ya fitar, shugaban ƙungiyar kuma Gwamnan Jihar Gombe Muhammadu Inuwa Yahaya, ya bayyana lamarin a matsayin abin takaici.

ADVERTISEMENT
  • Sin: Ya Zama Wajibi A Dakile Mummunan Yanayin Wanzuwar Tashe-tashen Hankula Da Yunwa
  • Wani Mai Taɓin Ƙwaƙwalwa Ya Kashe Soja A Legas

Gwamna Inuwa ya kuma ce sace yaran rashin hankali ne da ba za a amince da shi ba, tare da bayyana cewa ci gaba da kai hare-hare a makarantu yana babbar barazana ga zaman lafiyan Arewa da makomar ilimi a ƙasar nan.

 

LABARAI MASU NASABA

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

Gwamna Inuwa Yahaya, a madadin takwarorinsa na ƙungiyar, ya jajantawa gwamnati da al’ummar Jihar Kebbi musamman iyalan ɗaliban da aka sace da kuma waɗanda suka rasa rayukansu a harin.

 

Ya kuma bai wa Gwamna Nasir Idris na Jihar ta Kebbi tabbacin haɗin kai da goyon bayan ƙungiyar a wannan mawuyacin lokaci.

 

Gwamna Yahaya ya ce dole ne makarantu su zama wuraren koyo, ba wai wuraren tashin hankali ba, yana mai gargaɗin cewa ci gaba da kai hare-hare kan cibiyoyin ilimi yana barazana ga nasarorin da aka samu wajen inganta harkokin karatu a makarantu da kuma daƙile matsalar yaran da basa zuwa makaranta a yankin.

 

Ya nuna matuƙar damuwa kan irin halin da ƴan matan makarantar da aka sacen ke ciki, ya kuma yi ƙira da a gaggauta gudanar da wani shiri na haɗin gwiwa da jami’an tsaro don ganin an ceto su da kuma kama waɗanda suka aikata laifin.

 

Da ya ke jaddada ƙudurin ƙungiyar gwamnonin na Arewa na haɗa kai da gwamnatin tarayya da hukumomin tsaro, Gwamna Yahaya ya bayyana cewa, tsaro, ilimi da walwalar matasan Nijeriya na ci gaba da zama babban muradin ƙungiyar.

 

Shugaban ƙungiyar ta gwamnonin Arewa ya yi addu’ar Allah ya dawo da ‘yan matan makarantar da aka sace da wuri lafiya, ya kuma jajantawa iyalan waɗanda abin ya shafa, tare da yin ƙira ga al’umma su kasance cikin shiri da haɗin kai da jami’an tsaro a ƙoƙarin da suke na kawar da miyagun laifuka a yankin.

Kebbi
Khalid Idris Doya
+ posts Bio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Yaro Ya Harbe Kansa Har Lahira Bayan Mafarauci Ya Yi Sakaci Da Bindigarsa A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    An Kama Mutane 5 Da Sassan Jikin Ɗan’Adam Za Su Yi Tsafi A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mai Neman Takarar Gwamnan Bauchi, Bala Jibrin, Ya Fice Daga APC Kan Zargin Ɗoki-ɗora
Kebbi
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto
  • Sulaiman
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi
  • Sulaiman
    Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

MASU ALAKA

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto
Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja
Labarai

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Next Post
Ba Za A Amince Da Sake Farfado Da Ra’ayin Nuna Karfin Soja Na Japan Ba

Ba Za A Amince Da Sake Farfado Da Ra’ayin Nuna Karfin Soja Na Japan Ba

LABARAI MASU NASABA

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.