ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwarzon Kamfani A Shekarar 2024: AVSATEL Communications Limited

by Leadership Hausa
2 years ago
Avsatel

Jaridar LEADERSHIP ta zaɓi kamfanin AVSATEL a matsayin gwarzon shekara ta 2024, saboda gagarumar gudummawar da ya bayar wajen samar da tsaro da aminci a sararin samaniya da kula da zirga-zirgar jiragen sama da kawo ci gaban samar da kayayyakin cikin gida Nijeriya.

AVSATEL, kamfanin cikin gida Nijeriya ne mai kula da zirga-zirgar jiragen sama, ya kawo sauyi a fannin zirga-zirgar jiragen sama a Nijeriya ta hanyar yin amfani da tauraron dan adam mai sauri da tsarin sanya ido cikin hanzari kan yanayin sararin samaniyar ƙasa.

  • Kano Ta Kaddamar Da Cibiyar Tafi-da-gidanka Ta Farko A Nijeriya Don Yi Wa Motoci Lasisi
  • Za A Shafe Kwanaki Uku Ana Zabga Ruwa Da Tsawa Daga Lahadi – Hasashen NiMet 

Bayan da Nijeriya ta fuskanci jarabawa a sararin samanya, ciki har da hatsarurrukan jiragen Sosoliso da ADC, gwamnatin Nijeriyar ta bai wa kamfanin AVSATEL amana don bayar da tsaro da ɗaukaka darajar kayayyakin aikin sufuri a ƙasar. AVSATEL ya amsa kira tare da fara inganta na’urorin sufuri a manyan filayen jiragen sama na Abuja da Legas da Fatakwal da kuma Kano, sai kuma aikin filayen jiragen sama na Birnin Kebbi da Lafia. Ta hanyar waɗannan ayyukan, AVSATEL ya samar da kyakkyawan yanayi mai aminci a sararin samaniyar Nijeriya, tare da ingantattun tsare-tsare waɗanda ke ƙara tabbatar da ci gaba da sa ido kan zirga-zirgar jiragen sama.

ADVERTISEMENT

AVSATEL bai tsaya a fagen fasaha kadai ba, ya taka rawar gani wajen samar da kayayyakin aiki don ɗorewar hanyoyin sufurin jiragen sama a Nijeriya. Ɗaya daga cikin ci gaba da AVSATEL ya samar, shi ne samar da wuri don sayar da kayan aiki da gyare-gyare na na’urorin sufuri a Abuja, wanda hakan ya bayar da damar yin gyare-gyare da sauri ba tare da jira har sai an sayo wani kayan gyara daga ƙasashen waje ba. Wannan wuri ya bayar da gudummawa matuka wajen rage ɓata lakacin gyara tare da tabbatar da cewa an samar da muhimman abubuwan da za a iya amfani da su nan take.

AVSATEL ya yi nasarar samar da ƙwararru a fannin jiragen sama na Nijeriya, ta hanyar samar da shirye-shiryen horaswa na kamfanin, ya bai wa ɗaruruwan ƙwararru masana harkokin sufurin jiragen sama na Nijeriya fasahar zamani, inda yanzu suke zama a matsayin jagorori a ɓangaren kula da sararin samaniya. Hadin guiwar AVSATEL tare da abokan hulɗa na ƙasa da ƙasa daga Faransa da Koriya ta Kudu da Finland da kuma Austria sun bayar da damar horar da ma’aikata a Hukumar Kula da Sararin Samaniya ta Nijeriya (NAMA), da Hukumar Kula da Yanayi ta Nijeriya (NIMET).

LABARAI MASU NASABA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Kamfanin na AVSATEL ya kuma ƙara mayar da hankali wajen horar da ma’aikata kashe gobara don ƙara bunƙasa ɓangaren sufurin jiragen sama don bayar da agajin gaggawa. Kamfanin ya samar da shirye-shiryen horo na musamman ga ma’aikatan kashe gobara. Wannan tunani na bayar da horo ga ma’aikatan ya nuna irin kishi da himmar AVSATEL wajen tabbatar da cewa bai tsaya ga tsaron sararin samaniyar Nijeriya kaɗai ba, har ma da kiyaye rayuwar al’umma da matafiya a duk faɗin ƙasar.

 Saboda ficen da kamfanin ya yi, ya samu takardar shaida ta ISO 2001-2015 daga Hukumar Kula da Ƙayayyakin Amfani ta Nijeriya (SON). AVSATEL ya fito da irin cikakken shiri mai inganci da bangaren sufurin jiragen sama na Nijeriya ke da shi.

Kamfanin ya shafe fiye da shekaru ashirin yana tabbatar da nutsuwa da aminci a cikin zukatan matafiya na cikin gida da na ƙetare a yayin gudanar da tafiye-tafiyensu da zirga-zirga a sararin samaniyar Nijeriya.

Avsatel
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu
  • Leadership Hausa
    Ikirarin Cewa Sanata Abdul’aziz Yari Abubakar, Marafan Sokoto, Nauyi Ne Ga Jihar Zamfara Da Jam’iyyar APC Ba Ta Da Tushe
  • Leadership Hausa
    Nazarin Kisan Gillar Da ‘Yan Kato Da Gora Suka Yi Wa Wani Matashi A Biniwe

MASU ALAKA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna
Labarai

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Next Post
Terra Ya Yi Nasarar Zama Sinadarin Ɗanɗanon Girki Mafi Daɗi A Shekara Ta 2024

Terra Ya Yi Nasarar Zama Sinadarin Ɗanɗanon Girki Mafi Daɗi A Shekara Ta 2024

LABARAI MASU NASABA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.