• English
  • Business News
Tuesday, November 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

by Yusuf Shuaibu
4 months ago
ADC

A wani bangare na kokarin gina hadakar jam’iyyar ADC gabanin zaben 2027, jam’iyyar ta fara tusashe karfin PDP a wasu jihohin Nijeriya sakamakon jan hankalin manyan ‘yan siyasa daga PDP da APC.

Duk da cewa ADC ta riga ta karbe tsarin PDP a Yobe, Gombe, Adamawa da wasu jihohi na arewa, amma mafi yawancin masana harkokin siyasa suna ganin cewa akwai sauran rina a kaba.

  • Sauye-sauyen Tinubu Suna Taimaka Wa Farfaɗowar Tattalin Arzikin Nijeriya — Minista
  • EFCC Ta Kama Ƴan Ƙasashen Waje 146 Kan Laifukan Zambar Kuɗaɗe

Wannan ya zo ne tun bayan da Gwamna Jihar Borno, Babagana Zulum ya musanta rahotannin kafafen watsa labarai cewa zai jagoranci wasu gwamnonin guda biyar daga APC zuwa ADC.

Haka kuma, dan takarar shugaban kasa na jam’iyar LP a 2023, Mista Peter Obi, ya ce zai ci gaba da kare muradun magoya bayansa da abokan siyasarsa.

Sannan ministan Babban Birnin Tarayya Abuja, Nyesom Wike, ya caccaki sakatare na wucin gadi na ADC, Rauf Aregbesola, kan ya bayar da rahoton aikinsa a matsayinsa na ministan harkokin cikin gida a lokacin mulkin da ya gabata.

LABARAI MASU NASABA

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

2027: Peter Obi Ya Shiga Rudani Kan Jam’iyyar Da Zai Tsaya Takara

Da yake tabbatar da daukar salon tsarin PDP a jihohin Yobe, Gombe da Adamawa, Mista Paul Ibe, mai ba da shawara kan harkokin watsa labarai ga tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar, ya ce shugabannin PDP a jihohin arewa sun yi hadin gwiwa da hadakar jam’iyyar.

Ibe ya ce: “Hadakar na samun karfi. Atiku Abubakar zai ci gaba da bayar da gudunmuwa don tabbatar da cewa hadin gwiwar na jam’iyyar.”

“Bayan samun hakan, za ka iya ganin sakamakon. Shugabannin PDP na Yobe sun hade da ADC, haka ma na Gombe. Shugabannin Adamawa ma sun yi alkawarin amincewa. Wannan lamari yana samar da sakamakon da ake bukata.”

Haka kuma ya da yabawa rawar da Atiku ya taka wajen hada kan kungiyoyi daban-daban na siyasa, yana bayyana hakan a matsayin alamar shugabanci na gari.

“A makon da ya wuce, tsarin siyasa yana juyawa zuwa ga mulkin jam’iyya guda, wanda ya tuna da zamanin Abacha. Wannan hadakar tana mayar da martani ne ga irin wannan barazana,” Ibe ya shaida hakan.

Ya kwatanta kalubalen gina hadakan da cewa kamar sabbin ma’aurata ne da ke daidaita rayuwa tare

Shugaban kungiyar shugabannin PDP na jihohi (PDPSCF), da kuma shugaban PDP na Jihar Imo, Mista Austin Nwachukwu, ya bayyana rahotannin tusashewar a matsayin shadi fadi, yana mai jaddada cewa PDP na nan da karfi da hadin kai.

Nwachukwu ya ce, “Shugabannin jam’iyyar a Yobe da Borno sun ki yarda da wannan ikirarin. Wadannan labaru ne na boge da aka kirkira don jawo hankalin al’umma.

“Yawancin wadannan ‘yan siyasarmu sun haura shekaru fiye da 70. Me suke nema a yanzu? Kudaden ritaya ko yi wa kasa hidima.”

A cewarsa, PDP ta kasance kan duga-duganta, yayin da ya yi watsar da labarin dusashewar a matsayin abin da ba shi da tasiri. Ya ce, “Da yawa daga cikin wadanda suka fita sun koma PDP. Muna waADC fatan alkairi, amma PDP ta fi karfin ta dusashe ta a kowanne lokaci.”

A halin yanzu, mai magana da yawun ADC na wucin gadi, Bolaji Abdullahi, ya jaddada cewa hadakar na da tasiri dun tunkarar APC mai mulki a 2027.

A cikin wata tattaunawa da manema labarai, Abdullahi ya ce, “ADC na wakiltar hadakar ‘yan Nijeriya da ke tsayawa kan gazawar wannan gwamnati. A cikin watannin da ke tafe, za ku ga ba mambobin PDP ba kadai har ma da wasu jam’iyyun adawa kamar SDP, LP, da NNPP za su shigo cikinmu.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta
Tambarin Dimokuradiyya

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

October 17, 2025
peter
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Peter Obi Ya Shiga Rudani Kan Jam’iyyar Da Zai Tsaya Takara

October 17, 2025
peter
Tambarin Dimokuradiyya

Peter Obi Ya Bukaci INEC Ta Tabbatar Da Shaidar Karatun Dan Takara Kafin Shiga Zabe

October 10, 2025
Next Post
Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

LABARAI MASU NASABA

China Ta Gargaɗi Amurka Kan Tsoma Baki A Harkokin Nijeriya

China Ta Gargaɗi Amurka Kan Tsoma Baki A Harkokin Nijeriya

November 4, 2025
2023: Me Ya Sa Ake Rububin Wike?

Atiku Ya Fice Daga PDP Saboda Na Ƙi Bari Ya Lalata Mana Jam’iyya – Wike

November 4, 2025
Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha

Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha

November 4, 2025
Kalaman Trump A Kan Nijeriya Abun Damuwa Ne – Peter Obi 

Kalaman Trump A Kan Nijeriya Abun Damuwa Ne – Peter Obi 

November 4, 2025
Jami’an Tsaro Sun Dawo Da Fasfo Ɗin Sanata Natasha Bayan Ƙwace Shi A Abuja

Natasha Ta Zargi Akpabio Da Sanya Jami’an Tsaro Su Ƙwace Mata Fasfo A Filin Jirgin Saman Abuja 

November 4, 2025
Masu Kashe Mutane A Kudu Maso Gabas Kiristoci Ne – Soludo

Masu Kashe Mutane A Kudu Maso Gabas Kiristoci Ne – Soludo

November 4, 2025
Ribadu Ya Gana Da Hafsoshin Tsaro Biyo Bayan Kalaman Trump 

Ribadu Ya Gana Da Hafsoshin Tsaro Biyo Bayan Kalaman Trump 

November 4, 2025
Sarkin Kasar Spaniya Zai Kawo Ziyara Kasar Sin

Sarkin Kasar Spaniya Zai Kawo Ziyara Kasar Sin

November 3, 2025
Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Trump Dangane Da Gwajin Nukiliya A Asirce

Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Trump Dangane Da Gwajin Nukiliya A Asirce

November 3, 2025
An Bude Taron Kasuwanci Na Duniya Na 18 A Macau

An Bude Taron Kasuwanci Na Duniya Na 18 A Macau

November 3, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.