• English
  • Business News
Sunday, August 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

by Yusuf Shuaibu
3 weeks ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A wani bangare na kokarin gina hadakar jam’iyyar ADC gabanin zaben 2027, jam’iyyar ta fara tusashe karfin PDP a wasu jihohin Nijeriya sakamakon jan hankalin manyan ‘yan siyasa daga PDP da APC.

Duk da cewa ADC ta riga ta karbe tsarin PDP a Yobe, Gombe, Adamawa da wasu jihohi na arewa, amma mafi yawancin masana harkokin siyasa suna ganin cewa akwai sauran rina a kaba.

  • Sauye-sauyen Tinubu Suna Taimaka Wa Farfaɗowar Tattalin Arzikin Nijeriya — Minista
  • EFCC Ta Kama Ƴan Ƙasashen Waje 146 Kan Laifukan Zambar Kuɗaɗe

Wannan ya zo ne tun bayan da Gwamna Jihar Borno, Babagana Zulum ya musanta rahotannin kafafen watsa labarai cewa zai jagoranci wasu gwamnonin guda biyar daga APC zuwa ADC.

Haka kuma, dan takarar shugaban kasa na jam’iyar LP a 2023, Mista Peter Obi, ya ce zai ci gaba da kare muradun magoya bayansa da abokan siyasarsa.

Sannan ministan Babban Birnin Tarayya Abuja, Nyesom Wike, ya caccaki sakatare na wucin gadi na ADC, Rauf Aregbesola, kan ya bayar da rahoton aikinsa a matsayinsa na ministan harkokin cikin gida a lokacin mulkin da ya gabata.

Labarai Masu Nasaba

ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?

Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

Da yake tabbatar da daukar salon tsarin PDP a jihohin Yobe, Gombe da Adamawa, Mista Paul Ibe, mai ba da shawara kan harkokin watsa labarai ga tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar, ya ce shugabannin PDP a jihohin arewa sun yi hadin gwiwa da hadakar jam’iyyar.

Ibe ya ce: “Hadakar na samun karfi. Atiku Abubakar zai ci gaba da bayar da gudunmuwa don tabbatar da cewa hadin gwiwar na jam’iyyar.”

“Bayan samun hakan, za ka iya ganin sakamakon. Shugabannin PDP na Yobe sun hade da ADC, haka ma na Gombe. Shugabannin Adamawa ma sun yi alkawarin amincewa. Wannan lamari yana samar da sakamakon da ake bukata.”

Haka kuma ya da yabawa rawar da Atiku ya taka wajen hada kan kungiyoyi daban-daban na siyasa, yana bayyana hakan a matsayin alamar shugabanci na gari.

“A makon da ya wuce, tsarin siyasa yana juyawa zuwa ga mulkin jam’iyya guda, wanda ya tuna da zamanin Abacha. Wannan hadakar tana mayar da martani ne ga irin wannan barazana,” Ibe ya shaida hakan.

Ya kwatanta kalubalen gina hadakan da cewa kamar sabbin ma’aurata ne da ke daidaita rayuwa tare

Shugaban kungiyar shugabannin PDP na jihohi (PDPSCF), da kuma shugaban PDP na Jihar Imo, Mista Austin Nwachukwu, ya bayyana rahotannin tusashewar a matsayin shadi fadi, yana mai jaddada cewa PDP na nan da karfi da hadin kai.

Nwachukwu ya ce, “Shugabannin jam’iyyar a Yobe da Borno sun ki yarda da wannan ikirarin. Wadannan labaru ne na boge da aka kirkira don jawo hankalin al’umma.

“Yawancin wadannan ‘yan siyasarmu sun haura shekaru fiye da 70. Me suke nema a yanzu? Kudaden ritaya ko yi wa kasa hidima.”

A cewarsa, PDP ta kasance kan duga-duganta, yayin da ya yi watsar da labarin dusashewar a matsayin abin da ba shi da tasiri. Ya ce, “Da yawa daga cikin wadanda suka fita sun koma PDP. Muna waADC fatan alkairi, amma PDP ta fi karfin ta dusashe ta a kowanne lokaci.”

A halin yanzu, mai magana da yawun ADC na wucin gadi, Bolaji Abdullahi, ya jaddada cewa hadakar na da tasiri dun tunkarar APC mai mulki a 2027.

A cikin wata tattaunawa da manema labarai, Abdullahi ya ce, “ADC na wakiltar hadakar ‘yan Nijeriya da ke tsayawa kan gazawar wannan gwamnati. A cikin watannin da ke tafe, za ku ga ba mambobin PDP ba kadai har ma da wasu jam’iyyun adawa kamar SDP, LP, da NNPP za su shigo cikinmu.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ADC
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

Next Post

Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

Related

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?

1 week ago
Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 
Tambarin Dimokuradiyya

Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

1 week ago
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Masu Neman Takarar Shugaban Kasa A PDP Sun Kara Matsa Kaimi Bayan Ficewar Atiku

1 week ago
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

2 weeks ago
majalisar kasa
Tambarin Dimokuradiyya

Kirkirar Sabbin Jihohi Da Kananan Hukumomi Sun Dabaibaye Sauraron Jin Ra’ayoyin Gyaran Tsarin Mulki

2 weeks ago
Ko Yanzu Tinubu Ya Yi Rawar Gani, Kuma Yana Ƙoƙari Sosai – Buhari
Rahotonni

Muhimman Abubuwa 10 Da Kowa Zai So Ya Sani Game Da Marigayi Shugaban Ƙasa Buhari

3 weeks ago
Next Post
Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

LABARAI MASU NASABA

Shugabar Tanzania Ta Kaddamar Da Cibiyar Cinikayya Da Jigila Da Sin Ta Gina A Kasar

Shugabar Tanzania Ta Kaddamar Da Cibiyar Cinikayya Da Jigila Da Sin Ta Gina A Kasar

August 3, 2025
Manoma Sun Caccaki Tinubu Kan Ƙarfafa Shigo Da Shinkafa Da Masara Daga Ƙasashen Waje

Manoma Sun Caccaki Tinubu Kan Ƙarfafa Shigo Da Shinkafa Da Masara Daga Ƙasashen Waje

August 3, 2025
Amurka Ta Gargaɗi Ƴan Nijeriya Kan Zuwa Ƙasarta Domin Haihuwa

Amurka Ta Gargaɗi Ƴan Nijeriya Kan Zuwa Ƙasarta Domin Haihuwa

August 3, 2025
Ministan Yaɗa Labarai Ya Buƙaci A Kwantar Da Hankali Kan Dakatar Da Gidan Rediyon Badeggi FM

ADC Ta Yi Allah-wadai Da Rufe Gidan Rediyon Badeggi FM A Neja

August 3, 2025
Gwamnatin Katsina Ta Gabatar Da Matsayarta A Taron Jin Ra’ayiyin Jama’a

Gwamnatin Katsina Ta Gabatar Da Matsayarta A Taron Jin Ra’ayiyin Jama’a

August 3, 2025
Borno Za Ta Sake Tsugunar Da ‘Yan Gudun Hijira 5,000 Kafin Damuna Ta Kare

Borno Za Ta Sake Tsugunar Da ‘Yan Gudun Hijira 5,000 Kafin Damuna Ta Kare

August 3, 2025
Samun Kuɗi Ya Fi Samun Ɗaukaka Wahala A Kannywood -Baba Sadiƙ

Samun Kuɗi Ya Fi Samun Ɗaukaka Wahala A Kannywood -Baba Sadiƙ

August 3, 2025
Ministan Yaɗa Labarai Ya Buƙaci A Kwantar Da Hankali Kan Dakatar Da Gidan Rediyon Badeggi FM

Ministan Yaɗa Labarai Ya Buƙaci A Kwantar Da Hankali Kan Dakatar Da Gidan Rediyon Badeggi FM

August 3, 2025
Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

August 3, 2025
Ban Yi Danasanin Shiga Harkar Fim Ba – Baba Ƙarami

Ban Yi Danasanin Shiga Harkar Fim Ba – Baba Ƙarami

August 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.