ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

by Yusuf Shuaibu
11 months ago
ADC

A wani bangare na kokarin gina hadakar jam’iyyar ADC gabanin zaben 2027, jam’iyyar ta fara tusashe karfin PDP a wasu jihohin Nijeriya sakamakon jan hankalin manyan ‘yan siyasa daga PDP da APC.

Duk da cewa ADC ta riga ta karbe tsarin PDP a Yobe, Gombe, Adamawa da wasu jihohi na arewa, amma mafi yawancin masana harkokin siyasa suna ganin cewa akwai sauran rina a kaba.

  • Sauye-sauyen Tinubu Suna Taimaka Wa Farfaɗowar Tattalin Arzikin Nijeriya — Minista
  • EFCC Ta Kama Ƴan Ƙasashen Waje 146 Kan Laifukan Zambar Kuɗaɗe

Wannan ya zo ne tun bayan da Gwamna Jihar Borno, Babagana Zulum ya musanta rahotannin kafafen watsa labarai cewa zai jagoranci wasu gwamnonin guda biyar daga APC zuwa ADC.

ADVERTISEMENT

Haka kuma, dan takarar shugaban kasa na jam’iyar LP a 2023, Mista Peter Obi, ya ce zai ci gaba da kare muradun magoya bayansa da abokan siyasarsa.

Sannan ministan Babban Birnin Tarayya Abuja, Nyesom Wike, ya caccaki sakatare na wucin gadi na ADC, Rauf Aregbesola, kan ya bayar da rahoton aikinsa a matsayinsa na ministan harkokin cikin gida a lokacin mulkin da ya gabata.

LABARAI MASU NASABA

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya Sun Shiga Rudani A Yayin Da Wa’adin Mika Sunayen Mambobi Ya Shude

Da yake tabbatar da daukar salon tsarin PDP a jihohin Yobe, Gombe da Adamawa, Mista Paul Ibe, mai ba da shawara kan harkokin watsa labarai ga tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar, ya ce shugabannin PDP a jihohin arewa sun yi hadin gwiwa da hadakar jam’iyyar.

Ibe ya ce: “Hadakar na samun karfi. Atiku Abubakar zai ci gaba da bayar da gudunmuwa don tabbatar da cewa hadin gwiwar na jam’iyyar.”

“Bayan samun hakan, za ka iya ganin sakamakon. Shugabannin PDP na Yobe sun hade da ADC, haka ma na Gombe. Shugabannin Adamawa ma sun yi alkawarin amincewa. Wannan lamari yana samar da sakamakon da ake bukata.”

Haka kuma ya da yabawa rawar da Atiku ya taka wajen hada kan kungiyoyi daban-daban na siyasa, yana bayyana hakan a matsayin alamar shugabanci na gari.

“A makon da ya wuce, tsarin siyasa yana juyawa zuwa ga mulkin jam’iyya guda, wanda ya tuna da zamanin Abacha. Wannan hadakar tana mayar da martani ne ga irin wannan barazana,” Ibe ya shaida hakan.

Ya kwatanta kalubalen gina hadakan da cewa kamar sabbin ma’aurata ne da ke daidaita rayuwa tare

Shugaban kungiyar shugabannin PDP na jihohi (PDPSCF), da kuma shugaban PDP na Jihar Imo, Mista Austin Nwachukwu, ya bayyana rahotannin tusashewar a matsayin shadi fadi, yana mai jaddada cewa PDP na nan da karfi da hadin kai.

Nwachukwu ya ce, “Shugabannin jam’iyyar a Yobe da Borno sun ki yarda da wannan ikirarin. Wadannan labaru ne na boge da aka kirkira don jawo hankalin al’umma.

“Yawancin wadannan ‘yan siyasarmu sun haura shekaru fiye da 70. Me suke nema a yanzu? Kudaden ritaya ko yi wa kasa hidima.”

A cewarsa, PDP ta kasance kan duga-duganta, yayin da ya yi watsar da labarin dusashewar a matsayin abin da ba shi da tasiri. Ya ce, “Da yawa daga cikin wadanda suka fita sun koma PDP. Muna waADC fatan alkairi, amma PDP ta fi karfin ta dusashe ta a kowanne lokaci.”

A halin yanzu, mai magana da yawun ADC na wucin gadi, Bolaji Abdullahi, ya jaddada cewa hadakar na da tasiri dun tunkarar APC mai mulki a 2027.

A cikin wata tattaunawa da manema labarai, Abdullahi ya ce, “ADC na wakiltar hadakar ‘yan Nijeriya da ke tsayawa kan gazawar wannan gwamnati. A cikin watannin da ke tafe, za ku ga ba mambobin PDP ba kadai har ma da wasu jam’iyyun adawa kamar SDP, LP, da NNPP za su shigo cikinmu.”

ADC
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Masana Tattalin Arziki Sun Yi Watsi Da Rahoton NBS Kan Tattalin Arziki
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Alƙawarin Wa’adi Ɗaya Na Peter Obi Ya Raba Kawunan Ƴan Arewa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    ‘Yan Majalisar Wakilai 50 Da Suka Rasa Tikitin Takara A Zaɓen Fid Da Gwani Na APC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Zaɓen Fitar Da Gwani: APC Na Fuskantar Barazanar Tawaye

MASU ALAKA

ADC
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

May 16, 2026
Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya Sun Shiga Rudani A Yayin Da Wa’adin Mika Sunayen Mambobi Ya Shude

May 15, 2026
Abincin Da Ya Kamata Ku Ci Lokacin Al’ada
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Hadakar ‘Yan Adawa Ta Rushe Yayin Da Tikitin Takarar Shugaban Kasa Ya Raba Kan Shugabannin ADC

May 9, 2026
Next Post
Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.