ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

by Yusuf Shuaibu
1 year ago
ADC

A wani bangare na kokarin gina hadakar jam’iyyar ADC gabanin zaben 2027, jam’iyyar ta fara tusashe karfin PDP a wasu jihohin Nijeriya sakamakon jan hankalin manyan ‘yan siyasa daga PDP da APC.

Duk da cewa ADC ta riga ta karbe tsarin PDP a Yobe, Gombe, Adamawa da wasu jihohi na arewa, amma mafi yawancin masana harkokin siyasa suna ganin cewa akwai sauran rina a kaba.

  • Sauye-sauyen Tinubu Suna Taimaka Wa Farfaɗowar Tattalin Arzikin Nijeriya — Minista
  • EFCC Ta Kama Ƴan Ƙasashen Waje 146 Kan Laifukan Zambar Kuɗaɗe

Wannan ya zo ne tun bayan da Gwamna Jihar Borno, Babagana Zulum ya musanta rahotannin kafafen watsa labarai cewa zai jagoranci wasu gwamnonin guda biyar daga APC zuwa ADC.

ADVERTISEMENT

Haka kuma, dan takarar shugaban kasa na jam’iyar LP a 2023, Mista Peter Obi, ya ce zai ci gaba da kare muradun magoya bayansa da abokan siyasarsa.

Sannan ministan Babban Birnin Tarayya Abuja, Nyesom Wike, ya caccaki sakatare na wucin gadi na ADC, Rauf Aregbesola, kan ya bayar da rahoton aikinsa a matsayinsa na ministan harkokin cikin gida a lokacin mulkin da ya gabata.

LABARAI MASU NASABA

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

Da yake tabbatar da daukar salon tsarin PDP a jihohin Yobe, Gombe da Adamawa, Mista Paul Ibe, mai ba da shawara kan harkokin watsa labarai ga tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar, ya ce shugabannin PDP a jihohin arewa sun yi hadin gwiwa da hadakar jam’iyyar.

Ibe ya ce: “Hadakar na samun karfi. Atiku Abubakar zai ci gaba da bayar da gudunmuwa don tabbatar da cewa hadin gwiwar na jam’iyyar.”

“Bayan samun hakan, za ka iya ganin sakamakon. Shugabannin PDP na Yobe sun hade da ADC, haka ma na Gombe. Shugabannin Adamawa ma sun yi alkawarin amincewa. Wannan lamari yana samar da sakamakon da ake bukata.”

Haka kuma ya da yabawa rawar da Atiku ya taka wajen hada kan kungiyoyi daban-daban na siyasa, yana bayyana hakan a matsayin alamar shugabanci na gari.

“A makon da ya wuce, tsarin siyasa yana juyawa zuwa ga mulkin jam’iyya guda, wanda ya tuna da zamanin Abacha. Wannan hadakar tana mayar da martani ne ga irin wannan barazana,” Ibe ya shaida hakan.

Ya kwatanta kalubalen gina hadakan da cewa kamar sabbin ma’aurata ne da ke daidaita rayuwa tare

Shugaban kungiyar shugabannin PDP na jihohi (PDPSCF), da kuma shugaban PDP na Jihar Imo, Mista Austin Nwachukwu, ya bayyana rahotannin tusashewar a matsayin shadi fadi, yana mai jaddada cewa PDP na nan da karfi da hadin kai.

Nwachukwu ya ce, “Shugabannin jam’iyyar a Yobe da Borno sun ki yarda da wannan ikirarin. Wadannan labaru ne na boge da aka kirkira don jawo hankalin al’umma.

“Yawancin wadannan ‘yan siyasarmu sun haura shekaru fiye da 70. Me suke nema a yanzu? Kudaden ritaya ko yi wa kasa hidima.”

A cewarsa, PDP ta kasance kan duga-duganta, yayin da ya yi watsar da labarin dusashewar a matsayin abin da ba shi da tasiri. Ya ce, “Da yawa daga cikin wadanda suka fita sun koma PDP. Muna waADC fatan alkairi, amma PDP ta fi karfin ta dusashe ta a kowanne lokaci.”

A halin yanzu, mai magana da yawun ADC na wucin gadi, Bolaji Abdullahi, ya jaddada cewa hadakar na da tasiri dun tunkarar APC mai mulki a 2027.

A cikin wata tattaunawa da manema labarai, Abdullahi ya ce, “ADC na wakiltar hadakar ‘yan Nijeriya da ke tsayawa kan gazawar wannan gwamnati. A cikin watannin da ke tafe, za ku ga ba mambobin PDP ba kadai har ma da wasu jam’iyyun adawa kamar SDP, LP, da NNPP za su shigo cikinmu.”

ADC
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027

MASU ALAKA

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
Tambarin Dimokuradiyya

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

July 11, 2026
Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
Tambarin Dimokuradiyya

Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

July 11, 2026
makarfi
Tambarin Dimokuradiyya

Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi

June 26, 2026
Next Post
Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.