ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, November 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hadarin Mota: NIS Ta Tabbatar Da Mutuwar Jamianta 4, 7 Sun Ji Rauni A Kano

by Sulaiman
2 years ago
NIS

Hukumar Kula da Shige da Fice ta Nijeriya (NIS) ta tabbatar da cewa jamianta 4 sun rasu yayin da wasu 7 suka ji raunuka a wani hadarin mota da ya rusa da su a Jihar Kano.
Mai magana da yawun hukumar, DCI Adedotun Aridegbe ya bayyana haka a shalkwatar hukumar a wani taron manema labarai da ya kira ranar Litinin.

Ya yi bayanin cewa, A jiya ne wasu maaikatanmu goma sha daya ke dawowa Abuja daga wani aiki a Kano, a cikin wata motar bas mai daukar kujeru goma sha takwas suka yi wani mumunar hatsari, a wani wuri yan kilomitoci kadan daga Kano. Sakamakon haka, maaikatanmu hudu sun rasa rayukansu. Wannan lokaci ne na jimami a Hukumar Kula da Shige da Fice ta Nijeriya.
Abokan aikinmu guda bakwai da suka samu raunuka daban-daban a halin yanzu suna karbar magani a Asibitin Koyarwa na Aminu Kano da ke Kano. Muna musu adduar samun lafiya cikin gaggawa.

  • ‘Yansanda Sun Cafke Malamin Addini Da Sassan Mutum Danye A Oyo
  • Nijeriya Da Saudiyya Sun Kulla Alakar Musayar Fasaha A Bangaren Mai

Hukumar ta bayyana cewa, ta sanar da iyalan jamian da abin ya shafa kafin ta kira taron manema labarai don bayyana wa duniya asalin abin da ya faru, inda yanzu haka ake shirin yi wa wadanda suka mutu janaiza ta bangirma.

ADVERTISEMENT

Mukaddashiyar Kwanturola Janar ta Hukumar Kula da Shige da Fice, Caroline Wura-Ola Adepoju, ta yi matukar bakin ciki da wannan rashi, kuma da kanta ta mika ta’aziyya ga iyalan mamata tare da nanata cewa hukumar tana tare da iyalan magidantan da suka mutu cikin tallafawa a wannan lokaci na alhini. In ji shi.

Adedotun ya kuma ce, tuni Mukaddashiyar Kwanturola Janar ta ba da umarnin gudanar da bincike nan take don gano musabbabin hadarin. Kana ta sha alwashin daukar matakan da suka dace don hana faruwar hakan nan gaba.

LABARAI MASU NASABA

Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

Wannan lokaci ne na jimami a tsakanin daukacin iyalan Hukumar Shige da Fice ta Nijeriya. Mukaddashiyar CGI ta umurci dukkan ofisoshi da rassan hukumar su sassauta tutocinsu na tsawon kwanaki bakwai masu zuwa. Za mu kuma yi zaman makoki na kwanaki uku don girmamawa da tunawa da abokan aikinmu da suka mutu. In mai magana da yawun hukumar.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su
Manyan Labarai

Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

November 16, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

November 16, 2025
Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle
Manyan Labarai

Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

November 16, 2025
Next Post
CITAD Ta Horas Da Yan Mata Kan Fasahar Zamani

CITAD Ta Horas Da Yan Mata Kan Fasahar Zamani

LABARAI MASU NASABA

Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

November 16, 2025
Fasinjojin Da Kasar Sin Ta Yi Jigilarsu Ta Jirgin Kasa Daga Janairu Zuwa Oktoba Sun Kai Biliyan 3.95

Fasinjojin Da Kasar Sin Ta Yi Jigilarsu Ta Jirgin Kasa Daga Janairu Zuwa Oktoba Sun Kai Biliyan 3.95

November 16, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

November 16, 2025
Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku

Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku

November 16, 2025
Sin Ta Gargadi Philippines A Kan Ci Gaba Da Tayar Da Zaune Tsaye A Tekun Kudancinta

Sin Ta Gargadi Philippines A Kan Ci Gaba Da Tayar Da Zaune Tsaye A Tekun Kudancinta

November 16, 2025
An Yi Taron Karatun Sinanci Na Duniya Na 2025 A Beijing

An Yi Taron Karatun Sinanci Na Duniya Na 2025 A Beijing

November 16, 2025
Ana Mai Da Hankali Kan Dabarun Kasar Sin A Fannin Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya A Taron COP30

Ana Mai Da Hankali Kan Dabarun Kasar Sin A Fannin Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya A Taron COP30

November 16, 2025
Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

November 16, 2025
DSS

Hukumar DSS Ta Kama Wani Kan Zargin Ƙerawa Da Rarraba Makamai A Filato

November 16, 2025
ECOWAS

A Zamanantar Da Tsarin Karatu A Makarantun Koyar Da Ilimin Addinin Musulunci – ECOWAS

November 16, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.