• English
  • Business News
Saturday, August 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hadarin Mota: NIS Ta Tabbatar Da Mutuwar Jamianta 4, 7 Sun Ji Rauni A Kano

by Sulaiman
2 years ago
in Labarai
0
Hadarin Mota: NIS Ta Tabbatar Da Mutuwar Jamianta 4, 7 Sun Ji Rauni A Kano
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar Kula da Shige da Fice ta Nijeriya (NIS) ta tabbatar da cewa jamianta 4 sun rasu yayin da wasu 7 suka ji raunuka a wani hadarin mota da ya rusa da su a Jihar Kano.
Mai magana da yawun hukumar, DCI Adedotun Aridegbe ya bayyana haka a shalkwatar hukumar a wani taron manema labarai da ya kira ranar Litinin.

Ya yi bayanin cewa, A jiya ne wasu maaikatanmu goma sha daya ke dawowa Abuja daga wani aiki a Kano, a cikin wata motar bas mai daukar kujeru goma sha takwas suka yi wani mumunar hatsari, a wani wuri yan kilomitoci kadan daga Kano. Sakamakon haka, maaikatanmu hudu sun rasa rayukansu. Wannan lokaci ne na jimami a Hukumar Kula da Shige da Fice ta Nijeriya.
Abokan aikinmu guda bakwai da suka samu raunuka daban-daban a halin yanzu suna karbar magani a Asibitin Koyarwa na Aminu Kano da ke Kano. Muna musu adduar samun lafiya cikin gaggawa.

  • ‘Yansanda Sun Cafke Malamin Addini Da Sassan Mutum Danye A Oyo
  • Nijeriya Da Saudiyya Sun Kulla Alakar Musayar Fasaha A Bangaren Mai

Hukumar ta bayyana cewa, ta sanar da iyalan jamian da abin ya shafa kafin ta kira taron manema labarai don bayyana wa duniya asalin abin da ya faru, inda yanzu haka ake shirin yi wa wadanda suka mutu janaiza ta bangirma.

Mukaddashiyar Kwanturola Janar ta Hukumar Kula da Shige da Fice, Caroline Wura-Ola Adepoju, ta yi matukar bakin ciki da wannan rashi, kuma da kanta ta mika ta’aziyya ga iyalan mamata tare da nanata cewa hukumar tana tare da iyalan magidantan da suka mutu cikin tallafawa a wannan lokaci na alhini. In ji shi.

Adedotun ya kuma ce, tuni Mukaddashiyar Kwanturola Janar ta ba da umarnin gudanar da bincike nan take don gano musabbabin hadarin. Kana ta sha alwashin daukar matakan da suka dace don hana faruwar hakan nan gaba.

Labarai Masu Nasaba

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

Wannan lokaci ne na jimami a tsakanin daukacin iyalan Hukumar Shige da Fice ta Nijeriya. Mukaddashiyar CGI ta umurci dukkan ofisoshi da rassan hukumar su sassauta tutocinsu na tsawon kwanaki bakwai masu zuwa. Za mu kuma yi zaman makoki na kwanaki uku don girmamawa da tunawa da abokan aikinmu da suka mutu. In mai magana da yawun hukumar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Hadarin motaKwale-KwaleNIS
ShareTweetSendShare
Previous Post

Manyan Kalubalen Da Ke Durkusar Da Kiwon Kifi A Nijeriya

Next Post

CITAD Ta Horas Da Yan Mata Kan Fasahar Zamani

Related

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya
Labarai

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

3 hours ago
Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi
Labarai

Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

4 hours ago
JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa
Labarai

JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

4 hours ago
Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba
Labarai

Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

5 hours ago
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Jagororin ‘Yan Bindiga A Abuja, Sun Ƙwato Makamai Da ₦7.4m

7 hours ago
Likitoci Sun Gano Wuka Da Aka Burma A Kirjin Wani Mutum Tsawon Shekara 8 
Labarai

Likitoci Sun Gano Wuka Da Aka Burma A Kirjin Wani Mutum Tsawon Shekara 8 

8 hours ago
Next Post
CITAD Ta Horas Da Yan Mata Kan Fasahar Zamani

CITAD Ta Horas Da Yan Mata Kan Fasahar Zamani

LABARAI MASU NASABA

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

August 22, 2025
UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

August 22, 2025
Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

August 22, 2025
Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

August 22, 2025
JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

August 22, 2025
Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

August 22, 2025
Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

August 22, 2025
Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

August 22, 2025
Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025

Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025

August 22, 2025
Ruben Dias Ya Rattaba Hannu Kan Sabon Kwantiragi A Manchester City

Ruben Dias Ya Rattaba Hannu Kan Sabon Kwantiragi A Manchester City

August 22, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.