ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

CITAD Ta Horas Da Yan Mata Kan Fasahar Zamani

by Leadership Hausa
3 years ago
CITad

Cibiyar Bunkasa Fasahar Sadarwa (CITAD), ta horas da yan mata ashirin da biyar da aka zakulo daga sassan Nijeriya kan yadda za su shiga a dama da su wajen fasahar sadarwar zamani da jagoranci.

Da take magana da yan jarida a yayin horon na kwanaki biyu da ya gudana a Bauchi makon jiya, jamiar kula da bangaren jinsi na CITAD, Zainab Aminu, ta ce, an zabo matan ne kuma an ba su horo na musamman a bangarorin shugabanci ta yadda za su shiga a dama da su a bangaren fasahar sadarwa tare da fuskantar kalubalen da mata ke fuskanta dangane da mu’amala da fasahar zamani.

  • CITAD Ta Bai Wa ‘Yan Jarida 10 Tallafi Don Gudanar Da Bincike Game Da Cin Hanci
  • Manyan Kalubalen Da Ke Durkusar Da Kiwon Kifi A Nijeriya

Ta ce, matan sun kuma samu horon yadda za su rungumi bangaren ICT domin shawo kan wariyar da ake yi wa mata a wannan fannin da kuma basu damar shiga a dama da su a bangaren fasahar sadarwa, hadi da tsare-tsaren da suka shafi kyautata harkokin jinsi.

ADVERTISEMENT

Jamiar ta kara da cewa bangarorin da horon ya kuma maida hankali sun hada da tsare-tsaren fasahar sadarwa, matakan amfani da yanar gizo, hanyoyin da ake amfani da kafafen sadarwa ba tare da wani musgunawa ko cin zarafinsu ba, hadi da tsare-tsaren yadda za su samu damar kirkirar abubuwa tare da samar da damarmaki ga mata.

Zainab Aminu ta kara da cewa, lokaci ya yi da mata za su amfana da dukkanin damarmakin da ke cikin fasahar zamani ba tare da tsangwama ba.

LABARAI MASU NASABA

Hukumar NCCE Ta Yi Tsare-tsaren Bunƙasa Horar Da Malamai

Abubuwan Da Ya Kamata Magidanci Ya Sani Bayan Matarsa Ta Haihu

Wannan horaswar ta jagoranci na da manufar wayar da kan mata kan yadda za su samu damar shiga a dama da su kan tsare-tsare da yadda za su shiga a yi da su a bangaren ICT da kuma dabarun yadda za su samu ilimi kan sauye-sauye, ta shaida.

Ita ma da take magana, daraktan cibiyar kere-kere ta Bloom, Hannah Kabrang, ta ce, horaswar zai taimakesu wajen kara samun damarmakin yadda za su fuskanci tsare-tsaren fasahar sadarwa da kuma yadda za su taimaki mata su shiga a dama da su wajen amfanuwa da zamani.

Ita ma Sadiya Lawan, daliba a jamiar Dutsin-Ma, da ta kasance mahalarciyar taron, ta ce, sun samu gogewar yadda za su fuskanci kowani irin kalubalen da ke fuskantar mata a kafafen sadarwar zamani da kuma fasahar zamani gaba daya.

Tana mai cewa an kuma basu horon ta yadda su ma za su koyar da wasu yadda za su fuskanci wadannan matsalolin da mata ke fuskanta musamman a kasar nan.

CITad
Leadership Hausa
+ postsBio
  • Leadership Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/leadership-hausa/
    Jerin Gwarazan Taurarinmu
  • Leadership Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/leadership-hausa/
    Jerin Gwarazan Taurarinmu
  • Leadership Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/leadership-hausa/
    “Ba Gudu Ba Ja Da Baya Game Da Tsarin “Call-up system” A NPA”
  • Leadership Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/leadership-hausa/
    Gwarzon Ma’aikacin Gwamnati Na Shekarar 2025, Dakta Zacch Adedeji

MASU ALAKA

Hukumar NCCE Ta Yi Tsare-tsaren Bunƙasa Horar Da Malamai
Ilimi

Hukumar NCCE Ta Yi Tsare-tsaren Bunƙasa Horar Da Malamai

May 31, 2026
Abubuwan Da Ya Kamata Magidanci Ya Sani Bayan Matarsa Ta Haihu
Ilimi

Abubuwan Da Ya Kamata Magidanci Ya Sani Bayan Matarsa Ta Haihu

May 30, 2026
Layya Babbar Ibada A Musulunci Na 1
Bakon Marubuci

Layya Babbar Ibada A Musulunci Na 1

May 27, 2026
Next Post
Amfanin Danyen Kwai Wajen Magance Kurajen Fuska

Amfanin Danyen Kwai Wajen Magance Kurajen Fuska

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.