ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

CITAD Ta Horas Da Yan Mata Kan Fasahar Zamani

by Leadership Hausa
3 years ago
CITad

Cibiyar Bunkasa Fasahar Sadarwa (CITAD), ta horas da yan mata ashirin da biyar da aka zakulo daga sassan Nijeriya kan yadda za su shiga a dama da su wajen fasahar sadarwar zamani da jagoranci.

Da take magana da yan jarida a yayin horon na kwanaki biyu da ya gudana a Bauchi makon jiya, jamiar kula da bangaren jinsi na CITAD, Zainab Aminu, ta ce, an zabo matan ne kuma an ba su horo na musamman a bangarorin shugabanci ta yadda za su shiga a dama da su a bangaren fasahar sadarwa tare da fuskantar kalubalen da mata ke fuskanta dangane da mu’amala da fasahar zamani.

  • CITAD Ta Bai Wa ‘Yan Jarida 10 Tallafi Don Gudanar Da Bincike Game Da Cin Hanci
  • Manyan Kalubalen Da Ke Durkusar Da Kiwon Kifi A Nijeriya

Ta ce, matan sun kuma samu horon yadda za su rungumi bangaren ICT domin shawo kan wariyar da ake yi wa mata a wannan fannin da kuma basu damar shiga a dama da su a bangaren fasahar sadarwa, hadi da tsare-tsaren da suka shafi kyautata harkokin jinsi.

ADVERTISEMENT

Jamiar ta kara da cewa bangarorin da horon ya kuma maida hankali sun hada da tsare-tsaren fasahar sadarwa, matakan amfani da yanar gizo, hanyoyin da ake amfani da kafafen sadarwa ba tare da wani musgunawa ko cin zarafinsu ba, hadi da tsare-tsaren yadda za su samu damar kirkirar abubuwa tare da samar da damarmaki ga mata.

Zainab Aminu ta kara da cewa, lokaci ya yi da mata za su amfana da dukkanin damarmakin da ke cikin fasahar zamani ba tare da tsangwama ba.

LABARAI MASU NASABA

Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace

Hukumar Ilimin Bai-ɗaya Ta Jihar Yobe Ta Raba Kayan Karatu

Wannan horaswar ta jagoranci na da manufar wayar da kan mata kan yadda za su samu damar shiga a dama da su kan tsare-tsare da yadda za su shiga a yi da su a bangaren ICT da kuma dabarun yadda za su samu ilimi kan sauye-sauye, ta shaida.

Ita ma da take magana, daraktan cibiyar kere-kere ta Bloom, Hannah Kabrang, ta ce, horaswar zai taimakesu wajen kara samun damarmakin yadda za su fuskanci tsare-tsaren fasahar sadarwa da kuma yadda za su taimaki mata su shiga a dama da su wajen amfanuwa da zamani.

Ita ma Sadiya Lawan, daliba a jamiar Dutsin-Ma, da ta kasance mahalarciyar taron, ta ce, sun samu gogewar yadda za su fuskanci kowani irin kalubalen da ke fuskantar mata a kafafen sadarwar zamani da kuma fasahar zamani gaba daya.

Tana mai cewa an kuma basu horon ta yadda su ma za su koyar da wasu yadda za su fuskanci wadannan matsalolin da mata ke fuskanta musamman a kasar nan.

CITad
Leadership Hausa
+ postsBio
  • Leadership Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/leadership-hausa/
    Jerin Gwarazan Taurarinmu
  • Leadership Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/leadership-hausa/
    Jerin Gwarazan Taurarinmu
  • Leadership Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/leadership-hausa/
    “Ba Gudu Ba Ja Da Baya Game Da Tsarin “Call-up system” A NPA”
  • Leadership Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/leadership-hausa/
    Gwarzon Ma’aikacin Gwamnati Na Shekarar 2025, Dakta Zacch Adedeji

MASU ALAKA

Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace
Ilimi

Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace

June 20, 2026
Hukumar Ilimin Bai-ɗaya Ta Jihar Yobe Ta Raba Kayan Karatu
Ilimi

Hukumar Ilimin Bai-ɗaya Ta Jihar Yobe Ta Raba Kayan Karatu

June 20, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund
Ilimi

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Next Post
Amfanin Danyen Kwai Wajen Magance Kurajen Fuska

Amfanin Danyen Kwai Wajen Magance Kurajen Fuska

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

June 25, 2026
Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

June 25, 2026
APC Ta Dage Yakin Zaben Shugaban Kasarta A Kano

An Dakatar Da Shugaban APC Na Kebbi Da Kwamishina Kan Zaɓen Cike Gurbin Zuru

June 25, 2026
Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.