ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nijeriya Da Saudiyya Sun Kulla Alakar Musayar Fasaha A Bangaren Mai

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Saudiyya

Gwamnatin Nijeriya da masarautar Saudiyya sun sanya hannun yarjejeniya domin bunkasa hadin guiwar fasaha, bangaren musayar fasahar sadarwa tsakanin kasashen biyu a bangaren mai da iskar gas.

Da ya ke bayani kan gagarumin matakin, a wata sanarwa, ministan albarkatun Mai, ya ce, hadin guiwar za ta taimaka wajen kara samar da hadin guiwa da fahimtar juna a tsakanin kasashen biyu dangane da bangaren samar da mai.

  • Tsohon Shugaban Karamar Hukumar Ngaski Ya Samu ‘Yanci Bayan Shafe Makonni 3 A Hannun ‘Yan Bindiga
  • Za A Samar Wa ‘Yan Nijeriya Gida 80,000 Cikin Shekara 4

Sanarwar dauke da sanya hannun Nneamaka Okafor, kakakin ministan mai Heineken Lokpobiri, ya ce, ministan ya wakilci Nijeriya a wajen bikin sanya hannun, inda ministan makamashi na kasar Saudiyya ya wakilci sarki Abdulaziz bin Salman, yayin rattaba hannun.

ADVERTISEMENT

Sanya hannun fahimtar junan (MoU), a cewar Lokpobiri, za ta taimaka sosai wa Nijeriya wajen kyautata fitar da mai da kuma fasaha hadi da bangaren makamashi.

Sanya hannun wacce ke da manufar kara kyautata alaka da juna da manufar samar da tsarin bunkasa harkokin mai da gas a kasashen biyu.

LABARAI MASU NASABA

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

Babban manufar sanya hannun sun hada da taimaka wa juna wajen musayar bayanai, musayar raayin fasaha ta hanyar da za a samu kafa da aza yanayin fahimta da kasashen biyu za su amfani junansu, sanarwar ta kara.

Tare da Saudiyya za mu samu damar bunkasa fasahohi a bangaren hako mai da iskar gas, Nijeriya za ta samu tagomashi sosai da musayar ilimi.

Ta fuskacin musayar fasaha, Nijeriya za ta samu damar da za ta kyautata harkokin makamashi da zai taimaka sosai wajen kara bunkasa hanyoyin da ake bi wajen fitar da mai da kuma shiga tsarin duniya.

Kazalika, amincewar yarjejeniyar ana sa ran zai janyo hankalin masu zuba hannun jari kai tsaye da su zo Nijeriya domin zuba hannun jari a bangaren mai da iskar gas. Kasar Saudiyya da take taka gagarumin rawa a kasuwar makamashi na duniya, ta na da gagarumin rawar da za ta taka wajen ci gaban zuba jari a Nijeriya.

Wannan, zai taimaka matuka gaya wajen cigaban tattalin arziki, samar da ayyukan yi da kuma bunkasa shimfida ayyukan raya kasa. Kuma, wannan matakin zai taimaka sosai wajen kyautata kasuwancin mai a Nijeriya, sannan, bangarorin cigaban tattalin arziki da dama za su samu damar habaka, a cewar ministan.

Bugu da kari, tsarin fahimtar junan, zai kuma taimaka wajen kyautata hadin guiwar fasahohi da na harkokin kudi.

Saudiyya
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa

MASU ALAKA

Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Next Post
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.