• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hadin Gwiwa Da Kasar Sin Na Ingiza Bunkasar Kasashen Afirka

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Hadin Gwiwa Da Kasar Sin Na Ingiza Bunkasar Kasashen Afirka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yayin da kasar Sin tare da kasashen Afirka ke kara azamar cika alkawuran da suka yiwa juna, na bunkasa hadin gwiwa da cudanya ta bangarori da dama, masharhanta na cewa “Kwalliya tana biyan kudin sabulu”, inda tuni hadin gwiwar kasar Sin da kasashen na Afirka ya haifar da ci gaban tattalin arziki, da kyautatuwar zamantakewar al’ummun sassan biyu. Alal misali, mun ga yadda bikin baje kolin tattalin arziki da cinikayya tsakanin Sin da Afirka karo na 3 da ya gabata, ya kara karfafa alakar cinikayya, da tattalin arziki tsakanin Sin da kasashen Afirka, tare da kara tabbatar da matsayin kasar Sin, na kasancewar muhimmiyar abokiyar cudanyar kasashen na Afirka a wannan fanni.

Idan ba a manta ba, yayin baje kolin na bana, wakilai daga kasashen Afirka 53, da karin wasu hukumomin kasa da kasa da dama sun hallara, kuma adadin masu baje hajoji a bikin ya kai 1,500, adadin da ya karu da kaso 70 bisa dari kan na shekarar 2021. Albarkacin matakai daban daban da sassan biyu ke dauka na raya huldar cinikayya da kasuwanci, yanzu haka Sin ta kai matsayin abokiyar cinikayyar Afirka mafi girma, kuma kasa ta hudu a girman zuba jari a nahiyar.

  • SCO Ta Ba Da Sanarwar Hadin Gwiwa Game Da Tsaro, Da Sauye-sauye Na Zamani

Bisa huldodin da Sin da kasashen Afirka ke rayawa, tasirin Sin a fannin bunkasar tattalin arzikin kasashen Afirka ya wuce batun samar da ababen more rayuwa kadai, domin kuma ya kunshi karin sassan samar da ci gaba daban daban. Ciki har da gina yankunan raya tattalin arziki na musamman da Sin din ke daukar nauyi a kasashen nahiyar da dama, wanda hakan ke samar da karin damammaki na bunkasa fannin masana’antun Afirka, da kuma kara fadada guraben ayyukan yi.

A daya bangaren, su ma kasashen Afirka ba a bar su a baya ba, wajen bullo da tsare-tsaren bunkasa cinikayya, da zuba jari tsakaninsu da bangaren Sin. Ga misali, yayin taron baje kolin kasa da kasa karo na 47 da ya gudana a birnin Dar es Salaam na kasar Tanzania a farkon makon nan, an kebe ranar Talata a matsayin ranar kasar Sin, tare da kebe rumfuna sama da 100 na baje hajojin kamfanonin kasar.

Wannan mataki dai ya kasance wata dama dake kara jaddada muhimmancin alakar cinikayya tsakanin Sin da Tanzania, da ma sauran kasashen Afirka, wadda a wannan karo ta baiwa masu yawon bude ido zarafin kara fahimtar wannan kasa mai ni’ima da karbar baki.

Labarai Masu Nasaba

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Manazarta da dama na ganin a halin da ake ciki, Sin da kasashen Afirka na kara fadada cudanya mai armashi ta fuskoki da dama, ta yadda hakan ke haifar da karin damammaki ga junan su, da habaka samar da ababen more rayuwar jama’a musamman a kasashen Afirka, da ingiza ci gaban masana’antu da musaya, matakin da ko shakka babu, na yin matukar tasiri ga ci gaban kasashen Afirka, a matsayin su na kasashe masu tasowa. (Saminu Alhassan)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Amsar Xi Jinping Ta Ba Duniya Damar Fahimtar Tsarin Binciken Hada-hadar Kudin Na Kasar Sin

Next Post

Magudin Jarrabawar UTME: Okebukola Ya Shawarci Makarantu Da Su Rungumi Tsarin JAMB

Related

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

7 hours ago
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata
Daga Birnin Sin

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

8 hours ago
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

10 hours ago
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya
Daga Birnin Sin

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

11 hours ago
Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar
Daga Birnin Sin

Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

18 hours ago
Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin

19 hours ago
Next Post
Magudin Jarrabawar UTME: Okebukola Ya Shawarci Makarantu Da Su Rungumi Tsarin JAMB

Magudin Jarrabawar UTME: Okebukola Ya Shawarci Makarantu Da Su Rungumi Tsarin JAMB

LABARAI MASU NASABA

UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.