Tsohon babban sakataren hukumar jami’o’i na kasa (NUC), Farfesa Peter Okebukola, ya ce, zargin magundin jarrabawa da ake zargin daliba, Ejikeme Joy Mmesoma, ya zama izina ga harkar zana jarrabawar manyan makaraantun da ke kasar nan.
Okebukola wanda ya daganta abinda dalibar ta aikata da abin takaici, inda ya shawarci hukumomin manyan makarantu da ke a kasar nan da su rungumi tsari da dabarun zamani na Oloyede, don kawo karshen aikata magudin jarrabawa a makarantun kasar nan da makaratun gwamnati.
- Majalisa Ta Dakatar Da JAMB Daga Hukunta Dalibar Da Ta Yi Sakamakon Bogi
- JAMB Ta Haramta Wa Dalibar Da Ta Yi Sakamakon Bogi Sake Zana Jarabawa
Ya ce, mutane da dama na sane da yadda magatakardar hukumar JAMB, Farfesa Ishaq Oloyede, ke yin kokarin tabatar da ganin an tabbatar da gaskiya wajen zana jarrabawar JAMB.
Daliba Mmesoma dai, ta yi ikirarin cewa, ta samu maki 362 na sakamakon jarrabawar UTME da dalibai suka zana a 2023, inda aka yi ta murnar samun wannnan makin nata a matsayin wadda ta fi kowanne dalibin da ya zana jarrabawar samun maki.
JAMB dai ta yi zargin cewa, sakamakon jarrabawar da Ejikeme ta yi ikirarin samu na bogi ne, wanda ta zarge da sauya samakakon daga makin da ta samu na 249, inda hakan ya janyo cece-kuce da mayar da martani daga wasu al’umar kasar nan.