ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hadin Gwiwa Da Kasar Sin Na Ingiza Bunkasar Kasashen Afirka

by CMG Hausa
3 years ago
Sin

Yayin da kasar Sin tare da kasashen Afirka ke kara azamar cika alkawuran da suka yiwa juna, na bunkasa hadin gwiwa da cudanya ta bangarori da dama, masharhanta na cewa “Kwalliya tana biyan kudin sabulu”, inda tuni hadin gwiwar kasar Sin da kasashen na Afirka ya haifar da ci gaban tattalin arziki, da kyautatuwar zamantakewar al’ummun sassan biyu. Alal misali, mun ga yadda bikin baje kolin tattalin arziki da cinikayya tsakanin Sin da Afirka karo na 3 da ya gabata, ya kara karfafa alakar cinikayya, da tattalin arziki tsakanin Sin da kasashen Afirka, tare da kara tabbatar da matsayin kasar Sin, na kasancewar muhimmiyar abokiyar cudanyar kasashen na Afirka a wannan fanni.

Idan ba a manta ba, yayin baje kolin na bana, wakilai daga kasashen Afirka 53, da karin wasu hukumomin kasa da kasa da dama sun hallara, kuma adadin masu baje hajoji a bikin ya kai 1,500, adadin da ya karu da kaso 70 bisa dari kan na shekarar 2021. Albarkacin matakai daban daban da sassan biyu ke dauka na raya huldar cinikayya da kasuwanci, yanzu haka Sin ta kai matsayin abokiyar cinikayyar Afirka mafi girma, kuma kasa ta hudu a girman zuba jari a nahiyar.

  • SCO Ta Ba Da Sanarwar Hadin Gwiwa Game Da Tsaro, Da Sauye-sauye Na Zamani

Bisa huldodin da Sin da kasashen Afirka ke rayawa, tasirin Sin a fannin bunkasar tattalin arzikin kasashen Afirka ya wuce batun samar da ababen more rayuwa kadai, domin kuma ya kunshi karin sassan samar da ci gaba daban daban. Ciki har da gina yankunan raya tattalin arziki na musamman da Sin din ke daukar nauyi a kasashen nahiyar da dama, wanda hakan ke samar da karin damammaki na bunkasa fannin masana’antun Afirka, da kuma kara fadada guraben ayyukan yi.

ADVERTISEMENT

A daya bangaren, su ma kasashen Afirka ba a bar su a baya ba, wajen bullo da tsare-tsaren bunkasa cinikayya, da zuba jari tsakaninsu da bangaren Sin. Ga misali, yayin taron baje kolin kasa da kasa karo na 47 da ya gudana a birnin Dar es Salaam na kasar Tanzania a farkon makon nan, an kebe ranar Talata a matsayin ranar kasar Sin, tare da kebe rumfuna sama da 100 na baje hajojin kamfanonin kasar.

Wannan mataki dai ya kasance wata dama dake kara jaddada muhimmancin alakar cinikayya tsakanin Sin da Tanzania, da ma sauran kasashen Afirka, wadda a wannan karo ta baiwa masu yawon bude ido zarafin kara fahimtar wannan kasa mai ni’ima da karbar baki.

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Manazarta da dama na ganin a halin da ake ciki, Sin da kasashen Afirka na kara fadada cudanya mai armashi ta fuskoki da dama, ta yadda hakan ke haifar da karin damammaki ga junan su, da habaka samar da ababen more rayuwar jama’a musamman a kasashen Afirka, da ingiza ci gaban masana’antu da musaya, matakin da ko shakka babu, na yin matukar tasiri ga ci gaban kasashen Afirka, a matsayin su na kasashe masu tasowa. (Saminu Alhassan)

Sin
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa
Daga Birnin Sin

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Next Post
Magudin Jarrabawar UTME: Okebukola Ya Shawarci Makarantu Da Su Rungumi Tsarin JAMB

Magudin Jarrabawar UTME: Okebukola Ya Shawarci Makarantu Da Su Rungumi Tsarin JAMB

LABARAI MASU NASABA

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.