• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hadin Gwiwa Da Kasar Sin Na Ingiza Bunkasar Kasashen Afirka

byCMG Hausa
2 years ago
Sin

Yayin da kasar Sin tare da kasashen Afirka ke kara azamar cika alkawuran da suka yiwa juna, na bunkasa hadin gwiwa da cudanya ta bangarori da dama, masharhanta na cewa “Kwalliya tana biyan kudin sabulu”, inda tuni hadin gwiwar kasar Sin da kasashen na Afirka ya haifar da ci gaban tattalin arziki, da kyautatuwar zamantakewar al’ummun sassan biyu. Alal misali, mun ga yadda bikin baje kolin tattalin arziki da cinikayya tsakanin Sin da Afirka karo na 3 da ya gabata, ya kara karfafa alakar cinikayya, da tattalin arziki tsakanin Sin da kasashen Afirka, tare da kara tabbatar da matsayin kasar Sin, na kasancewar muhimmiyar abokiyar cudanyar kasashen na Afirka a wannan fanni.

Idan ba a manta ba, yayin baje kolin na bana, wakilai daga kasashen Afirka 53, da karin wasu hukumomin kasa da kasa da dama sun hallara, kuma adadin masu baje hajoji a bikin ya kai 1,500, adadin da ya karu da kaso 70 bisa dari kan na shekarar 2021. Albarkacin matakai daban daban da sassan biyu ke dauka na raya huldar cinikayya da kasuwanci, yanzu haka Sin ta kai matsayin abokiyar cinikayyar Afirka mafi girma, kuma kasa ta hudu a girman zuba jari a nahiyar.

  • SCO Ta Ba Da Sanarwar Hadin Gwiwa Game Da Tsaro, Da Sauye-sauye Na Zamani

Bisa huldodin da Sin da kasashen Afirka ke rayawa, tasirin Sin a fannin bunkasar tattalin arzikin kasashen Afirka ya wuce batun samar da ababen more rayuwa kadai, domin kuma ya kunshi karin sassan samar da ci gaba daban daban. Ciki har da gina yankunan raya tattalin arziki na musamman da Sin din ke daukar nauyi a kasashen nahiyar da dama, wanda hakan ke samar da karin damammaki na bunkasa fannin masana’antun Afirka, da kuma kara fadada guraben ayyukan yi.

A daya bangaren, su ma kasashen Afirka ba a bar su a baya ba, wajen bullo da tsare-tsaren bunkasa cinikayya, da zuba jari tsakaninsu da bangaren Sin. Ga misali, yayin taron baje kolin kasa da kasa karo na 47 da ya gudana a birnin Dar es Salaam na kasar Tanzania a farkon makon nan, an kebe ranar Talata a matsayin ranar kasar Sin, tare da kebe rumfuna sama da 100 na baje hajojin kamfanonin kasar.

Wannan mataki dai ya kasance wata dama dake kara jaddada muhimmancin alakar cinikayya tsakanin Sin da Tanzania, da ma sauran kasashen Afirka, wadda a wannan karo ta baiwa masu yawon bude ido zarafin kara fahimtar wannan kasa mai ni’ima da karbar baki.

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Manazarta da dama na ganin a halin da ake ciki, Sin da kasashen Afirka na kara fadada cudanya mai armashi ta fuskoki da dama, ta yadda hakan ke haifar da karin damammaki ga junan su, da habaka samar da ababen more rayuwar jama’a musamman a kasashen Afirka, da ingiza ci gaban masana’antu da musaya, matakin da ko shakka babu, na yin matukar tasiri ga ci gaban kasashen Afirka, a matsayin su na kasashe masu tasowa. (Saminu Alhassan)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko
Daga Birnin Sin

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan
Daga Birnin Sin

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana
Daga Birnin Sin

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Next Post
Magudin Jarrabawar UTME: Okebukola Ya Shawarci Makarantu Da Su Rungumi Tsarin JAMB

Magudin Jarrabawar UTME: Okebukola Ya Shawarci Makarantu Da Su Rungumi Tsarin JAMB

LABARAI MASU NASABA

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version