• English
  • Business News
Saturday, October 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hadin Gwiwa Tsakanin Matasan Sin Da Afirka Zai Fadada Cin Gajiyar Kasashen Su

by CMG Hausa
3 years ago
Sin

Bayan kammalar dandalin matasan Sin da Afirka karo na biyu da aka gudanar a ‘yan kwanakin baya ta kafar bidiyo, masana da masu fashin baki sun nuna gamsuwa da ma’anar dandalin, bisa yadda aka yi amfani da shi wajen yin kira da a karfafa kawance, da hadin gwiwa a fannoni daban daban, domin raya Sin da Afirka bisa juriya da cin moriyar juna yadda ya kamata.

Dandalin wanda kungiyar sada zumunta tsakanin jama’ar kasar Sin da ta kasashen waje ko CPAFFC ta shirya, ya hallara masu ruwa da tsaki a fannin tsara manufofi, da ma’aikatan diflomasiyya, da masana, da dalibai, da wakilai daga kungiyoyin lura da walwalar jama’a, ya jaddada muhimmancin karfafa hadin gwiwa tsakanin matasan Sin da na kasashen Afirka, a matsayin wani ginshiki na kyautata rayuwar bil adama.

  • Xi Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Taron Ilimi Karo Na 16 Na Cibiyoyin Kimiya Na Kasashe Masu Tasowa

Wanda kuma nasarar sa za ta bude wani sabon babin goyon bayan juna tsakanin Sin da kasashen Afirka, musamman da yake batu ake yi na matasa, wadanda Bahaushe kan ce da su “Manyan Gobe”.
Alal hakika, Sin da kasashen Afirka, sun jima suna raya kawance da goyon bayan juna a lokutan yalwa da na tunkarar wahalhalu, kuma a matsayin ta na babbar kasa mai tasowa, Sin bata taba mantawa da abokan huldar ta na kasashen Afirka ba, inda take samar musu da tallafi ciki har da na kiwon lafiya, tare da taimakon samar da manyan ababen more rayuwa, kamar layukan dogo, da manyan hanyoyin mota, da gadoji, da cibiyoyin samar da lantarki, da filayen jiragen sama da sauran su.

La’akari da hakan ne ma, masana da dama ke ganin ko shakka ba bu, idan aka yi amfani da dandalin matasan Sin da Afirka, wajen yaukaka dangantakar sassan biyu, hakan zai kara ingiza cimma manyan nasarori a fannoni daban daban tsakanin sassan biyu, musamman ganin cewa, tuni an samar da manyan manufofin bunkasa hadin gwiwar sassan biyu, karkashin dandalin tattauna hadin gwiwar Sin da Afirka, da shawarar nan ta “Ziri Daya Da hanya Daya”.

Don haka dai, akwai bukatar matasan Sin da na kasashen Afirka su kara wucewa gaba wajen fadada kawance, da musaya, da hadin gwiwa tsakanin su, domin cimma kafuwar al’umma guda ta Sin da Afirka, mai makomar bai daya a dukkanin fannoni.

LABARAI MASU NASABA

An Bude Taron Sanin Makamar Aiki Na Cika Shekaru 80 Da Kafuwar MDD A Wuhan Na Kasar Sin

Kamfanin Gine-Gine Na CCECC Ya Fara Gina Wani Titin Mota Da Zai Rage Cunkoso A Birnin Abuja Na Tarayyar Najeriya

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Bude Taron Sanin Makamar Aiki Na Cika Shekaru 80 Da Kafuwar MDD A Wuhan Na Kasar Sin
Daga Birnin Sin

An Bude Taron Sanin Makamar Aiki Na Cika Shekaru 80 Da Kafuwar MDD A Wuhan Na Kasar Sin

October 18, 2025
Kamfanin Gine-Gine Na CCECC Ya Fara Gina Wani Titin Mota Da Zai Rage Cunkoso A Birnin Abuja Na Tarayyar Najeriya
Daga Birnin Sin

Kamfanin Gine-Gine Na CCECC Ya Fara Gina Wani Titin Mota Da Zai Rage Cunkoso A Birnin Abuja Na Tarayyar Najeriya

October 18, 2025
Masanin Ilimin Physics Chen Ning Yang Ya Rasu Yana Da Shekaru 103
Daga Birnin Sin

Masanin Ilimin Physics Chen Ning Yang Ya Rasu Yana Da Shekaru 103

October 18, 2025
Next Post
‘Yan Bindiga Sun Bukaci N40m Kudin Fansar Yara 20 Da Suka Sace A Neja

'Yan Bindiga Sun Sace Matafiya A Hanyar Abuja Zuwa Kogi

LABARAI MASU NASABA

gombe

Ɗaliban Jihar Gombe Sun Samu Ƙarin Kashi 100 Na Kuɗin Tallafin Karatu

October 18, 2025
Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma

Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma

October 18, 2025
An Bude Taron Sanin Makamar Aiki Na Cika Shekaru 80 Da Kafuwar MDD A Wuhan Na Kasar Sin

An Bude Taron Sanin Makamar Aiki Na Cika Shekaru 80 Da Kafuwar MDD A Wuhan Na Kasar Sin

October 18, 2025
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya

DHQ Ta Ƙaryata Rahoton Yunƙurin Yi Wa Tinubu Juyin Mulki

October 18, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas

‘Yansanda Sun Kai Samame Maboyar ‘Yan Ta’adda, Sun Kwato Miyagun Kwayoyi A Gombe

October 18, 2025
Kamfanin Gine-Gine Na CCECC Ya Fara Gina Wani Titin Mota Da Zai Rage Cunkoso A Birnin Abuja Na Tarayyar Najeriya

Kamfanin Gine-Gine Na CCECC Ya Fara Gina Wani Titin Mota Da Zai Rage Cunkoso A Birnin Abuja Na Tarayyar Najeriya

October 18, 2025
ASUU

Cikin Wata 9 Farfesoshi 309 Sun Bar Aiki A Jami’o’in Gwamnati, In Ji ASUU

October 18, 2025
Masanin Ilimin Physics Chen Ning Yang Ya Rasu Yana Da Shekaru 103

Masanin Ilimin Physics Chen Ning Yang Ya Rasu Yana Da Shekaru 103

October 18, 2025
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

October 18, 2025
Kasar Sin Ta Gargadi Amurka Game Da Yunkurin Samarwa Yankin Taiwan Makamai

Kasar Sin Ta Gargadi Amurka Game Da Yunkurin Samarwa Yankin Taiwan Makamai

October 18, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.