• English
  • Business News
Saturday, July 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hadin Gwiwar Afirka Da Sin Na Taimakawa Raya Duniya

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Hadin Gwiwar Afirka Da Sin Na Taimakawa Raya Duniya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Duniyarmu na fuskantar matsalolin da suka hada da yake-yake, da rashin tsaro, da koma bayan tattalin arziki, da karancin abinci, da annoba.

Wannan yanayi ya sa ake bukatar wani mataki da zai taimaka wajen saukaka yanayin da ake ciki da raya duniyarmu.

  • Sin: Hadin Gwiwar Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya Ta Haifar Da Sakamako Mai Kyau Da Fa’ida

To ko hadin gwiwar kasashen Afirka da kasar Sin, zai iya biyan bukatunmu a wannan fanni?
An gudanar da taron kolin masu tsara aiwatar da ayyukan da suka biyo bayan taron ministoci na 8, na dandalin tattaunawa kan hadin gwiwar Sin da Afirka (FOCAC)  ta kafar bidiyo jiya, inda manyan jami’an bangarorin Afirka da Sin, suka gabatar da hadaddiyar sanarwa da jawabai, wadanda suka nuna yadda hadin gwiwar bangarorin 2 ke taimakawa raya duniyar mu, musamman ta fannoni 2 dake kasa:
Da farko, hadin kan Afirka da Sin, ya sa ana samun hakikanin ci gaba.

An gudanar da taron ministoci na 8 na dandalin FOCAC a kasar Senegal, fiye da watanni 8 da suka wuce. Sai dai yaya ake aiwatar da yarjeniyoyin da aka cimma wajen taron?

A taro na wannan karo, an yi bayani kan wasu nasarorin da aka samu: Cikin fiye da watanni 8 da suka wuce, kamfanonin kasar Sin sun kammala ayyukan gina wasu manyan kayayyakin more rayuwa a kasashen Afirka, da suka hada da babbar gadar Fanggioni ta kasar Senegal, da tagwayen hanyoyi dake dab da filin jiragen sama na kasar Kenya, da babbar hanyar mota ta Kribi-Lolabe dake kasar Kamaru, da dai sauransu. Kana cikin watanni 7 da wuka wuce, kasar Sin ta shigo da kayayyaki masu darajar dala biliyan 70.6 daga kasashen Afirka, da zuba dala biliyan 2.17 ga kasuwannin Afirka.

Labarai Masu Nasaba

Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

Ban da wannan kuma, an tanadi ayyukan da za a gudanar da su kamar haka: kasar Sin za ta yafe wa wasu kasashe 17 dake nahiyar Afirka bashin da take binsu, da samar da karin tallafin abinci ga wasu kasashen da suke da bukata, da kara jiragen sama masu daukar fasinjoji, da suke zirga-zirga tsakanin Afirka da Sin, da dai sauransu.

Duk wata yarjejeniyar da aka kulla a baya, za a aiwatar da ita. Sa’an nan a yi cikakken bayani kan shirin da za a gudanar, don tabbatar da cika alkawuran. Wannan ya nuna yadda ake hadin gwiwa tsakanin Afirka da Sin don neman hakikanin ci gaba.

Sa’an nan, fanni na biyu shi ne, hadin gwiwar Afirka da Sin, a bude yake ga sauran bangarori.

Shin ko kasar Sin tana yin hadin gwiwa da kasashen Afirka don neman shawo kansu, da samun moriyar siyasa? Batun ba haka yake ba. Ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi, ya bayyana a wajen taron jiya cewa, “ Kasar Sin na son ganin gamayyar kasa da kasa sun ci gaba da mai da hankali kan kasashen Afirka, da nuna musu goyon baya.

Idan kasashen Afirka sun yarda, za a iya yin hadin kai tsakanin bangarori 3 ko fiye, a nahiyar Afirka. Kasashen Afirka suna bukatar wani yanayi na kwanciyar hankali da sada zumunta, maimakon ra’ayin yakin cacar baka, kana suna maraba da hadin gwiwar da zai amfani jama’a, maimakon shiga takarar wasu manyan kasashe.” Wannan magana ta nuna yadda bangaren Sin ke fahimtar ra’ayin kasashen Afirka.

Ta hanyar yin bincike kan tarihin hadin gwiwar Sin da Afirka, za mu iya fahimtar cewa, kasashen Afirka da kasar Sin, sun yi watsi da tunani na yakin cacar baka, wanda har yanzu kasashen yamma suke tsayawa a kai.

Sa’an nan sun juya ga tunanin al’ummar dan Adam mai makomar bai daya. Wanne ne daga cikin su zai fi amfanar al’ummun duniya?

Na san kowa zai iya ba da amsa.
Magance sabanin ra’ayi, da neman cimma matsaya, da kokarin hadin gwiwa don daidaita matsalolin da ake fuskanta, da neman samun hakikanin ci gaba, wannan shi ne ra’ayin da zai iya taimakawa, wajen kyautata yanayin da duniyarmu ke ciki, kuma babbar manufa ce da kasashen Afirka da kasar Sin ke tsayawa a kai, yayin da suke hadin gwiwa da juna. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda Matuka Jirgi Suka Shantake Da Bacci A Lokacin Sauka

Next Post

‘Yan Bindiga Sun Hallaka Lauya A Zamfara

Related

Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

6 hours ago
Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

7 hours ago
Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700
Daga Birnin Sin

Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

8 hours ago
Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria

9 hours ago
Hanya Mai Salon Musamman Da Kasar Sin Take Bi Wajen Raya Harkokin Kudi
Daga Birnin Sin

Hanya Mai Salon Musamman Da Kasar Sin Take Bi Wajen Raya Harkokin Kudi

10 hours ago
Peng Liyuan Ta Halarci Bikin Hada Hannun Matasa Da Yaran Sin Da Amurka Na Shekarar 2025
Daga Birnin Sin

Peng Liyuan Ta Halarci Bikin Hada Hannun Matasa Da Yaran Sin Da Amurka Na Shekarar 2025

20 hours ago
Next Post
‘Yan Bindiga Sun Hallaka Lauya A Zamfara

'Yan Bindiga Sun Hallaka Lauya A Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Dangote

Dalilin Da Ya Sa Dangote Ya Jinjina Wa Hukumar NPA

July 18, 2025
Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

July 18, 2025
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

July 18, 2025
Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

July 18, 2025
majalisar kasa

Kirkirar Sabbin Jihohi Da Kananan Hukumomi Sun Dabaibaye Sauraron Jin Ra’ayoyin Gyaran Tsarin Mulki

July 18, 2025
Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Zambia Da Ci 5-0

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Zambia Da Ci 5-0

July 18, 2025
Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

July 18, 2025
A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

July 18, 2025
Biyan Tukuici: Gwamna Yusuf Ya Ƙaddamar Da Tallafin Naira 50,000 Ga Mata 5,200 Duk Wata A Kano

Biyan ‘Yan Fansho Naira Biliyan 22: NUP Da NLC Sun Bukaci A Yi Koyi Da Gwamna Abba

July 18, 2025
Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria

July 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.