• English
  • Business News
Wednesday, September 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hadin Gwiwar CMG Da Kafafen Yada Labarai Na Afrika Zai Fahimtar Da Al’umma Kyakkyawar Aniyar Kasar Sin

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Hadin Gwiwar CMG Da Kafafen Yada Labarai Na Afrika Zai Fahimtar Da Al’umma Kyakkyawar Aniyar Kasar Sin
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Babban rukunin gidan rediyo da talabijin na kasar Sin CMG, da kungiyar kawancen gidajen rediyo ta Afrika, sun gudanar da taron dandalin tattaunawa kan hadin gwiwarsu, jiya Litinin a Nairobin kasar Kenya.

Muhimmancin kafofin watsa labarai a tsakanin al’umma abu ne mara misaltuwa, kasancewarsu tamkar gada tsakanin al’umma da wajen yankunansu. Kafar watsa labarai tamkar makaranta ce dake kan ilmantar da al’umma.

  • CMG Ya Sanya Hannu Kan Takardun Hadin Gwiwa Da Hukumar Sadarwar Wayar Tarho Ta Honduras

Hadin gwiwar CMG da kafafen yada labarai a nahiyar Afrika, musamman a irin wannan lokaci da karairaiyi da zarge-zarge suka kara yawa, zai taka gagarumar rawa wajen ilmantar da al’ummun nahiyar Afrika game da yanayin kasar Sin da kyakkaywar aniyarta gare su, har ma da dimbin tallafi da goyon baya da take ba nahiyar, haka kuma zai kara fahimtar da Sinawa ainihin yanayin da nahiyar Afrika ke ciki.

Rashin fahimta tamkar wata cuta ce dake bukatar kulawar likita. Yadda kafafen yada labarai na yammacin duniya suka yi kaka-gida a kasashenmu na Afrika, ya sa suke yada jita-jita da zummar haddasa fitina da shafawa Sin bakin fenti, domin cimma muradun kasashensu na babakere da dakile karbuwar kasar Sin a nahiyar.

Kyautatuwar alaka ko aminci mai karfi tsakanin Sin da kasashen Afrika, ya sa kafafen yada labarai na yammacin duniya ke kara wasa wukarsu na shafawa kasar Sin bakin fenti. Wannan ya sa nake ganin alaka ko kawance tsakanin kafafen yada labarai na Sin da Afrika ke da muhimmanci gaya, domin bangarorin biyu za su bayar da hakikanin labarai bisa yanayi na gaskiya da adalci ta yadda al’umma za su iya gane ainihin yanayin da duniya take ciki da ma wadanda ba sa son ganin ci gabansu.

Labarai Masu Nasaba

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

kamar yadda hadin gwiwar Sin da Afrika ke haifar da kyawawan sakamako a sauran fannoni, haka hadin gwiwa tsakanin CMG da kafafen yada labarai na Afrika zai yi kyakkyawan tasiri wajen fahimtar da al’umma game da irin kyakkaywar alakar dake tsakanin Sin da Afrika, domin su fahimci cewa, kasar Sin aminiya ce ta kwarai. Kana zai kai ga samun goyon bayan juna mai dorewa tsakanin al’ummomin, har ma da gina al’ummar Sin da Afrika mai makoma ta bai daya. Bugu da kuma kari, zai dakile yunkurin masu kokarin lalata wannan kyakkyawar dangataka.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Tsadar Rayuwa: Tinubu Na Duba Yiwuwar Dawo Da Tallafin Mai Na Wucin Gadi

Next Post

Kungiyar Dattawan Arewa Ta Bukaci Tinubu Ya Gaggauta Janye Takunkumin Da Aka Kakabawa Nijar

Related

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo
Daga Birnin Sin

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

10 hours ago
Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani
Daga Birnin Sin

Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

11 hours ago
Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok
Daga Birnin Sin

Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

12 hours ago
Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari
Daga Birnin Sin

Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

13 hours ago
Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi
Daga Birnin Sin

Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

14 hours ago
Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire
Daga Birnin Sin

Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire

16 hours ago
Next Post
Kungiyar Dattawan Arewa Ta Bukaci Tinubu Ya Gaggauta Janye Takunkumin Da Aka Kakabawa Nijar

Kungiyar Dattawan Arewa Ta Bukaci Tinubu Ya Gaggauta Janye Takunkumin Da Aka Kakabawa Nijar

LABARAI MASU NASABA

Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

September 17, 2025
Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

September 17, 2025
Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

September 16, 2025
Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

September 16, 2025
Sauye-sauyen Manufofin Gwamnati Na Iya Hana Masu HND Zuwa NYSC

An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos

September 16, 2025
Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

September 16, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

September 16, 2025
Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

September 16, 2025
Sojoji

Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba

September 16, 2025
Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

September 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.