• English
  • Business News
Monday, August 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka A Fannin Kimiyya Da Fasaha Zai Taimakawa Afirka Wajen Samun Ci Gaba

by Sulaiman and CGTN Hausa
1 year ago
in Ra'ayi Riga
0
Hadin Gwiwar Sin Da Afirka A Fannin Kimiyya Da Fasaha Zai Taimakawa Afirka Wajen Samun Ci Gaba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin kasar Sin ta gudanar da babban taron karrama masu nazarin kimiyya da fasaha a jiya, inda aka samar da dimbin kyaututuka ga fitattun ma’aikata masu nazarin kimiyya da fasaha na kasar, don yaba musu bisa muhimmiyar gudunmowar da suka samar a fannin nazari kan bangarori masu alaka da kimiyyar lissafi ta Physics, da aikin safiyo ta tauraron dan Adam mai hango abubuwan dake doron kasa, da sinadaran da ake amfani da su wajen hada kayayyakin latironi, gami da aikin gona, da dai sauransu. Mai bayar da kyautuka a wajen taron shi ne shugaban kasar Sin Xi Jinping, lamarin da ya nuna matukar muhimmancin da kasar Sin ta dora ma kimiyya da fasaha, da bangaren kirkire-kirkire. To, sai dai wane irin tasiri ci gaban kasar Sin ta fuskar kimiyya da fasaha zai samar wa kasashen Afirka?

Dangane da wannan tambaya, su ‘yan Afirka suke da ikon ba da amsa. Olusegun Oyebade Ikusika, wani shehun malami ne dake aiki a jami’ar Fort Hare ta kasar Afirka ta Kudu, wanda ke mai da hankali kan nazarin hadin gwiwar da ake yi tsakanin kasashen Afirka da kasar Sin ta fuskar kimiyya da fasaha, cikin shekarun nan. Yayin da yake hira da manema labaru na kasar Sin a kwanan baya, ya ce, ilimi da fasahohi na kasar Sin, da hadin gwiwar Afirka da Sin a fannin kimiyya da fasaha, suna taka muhimmiyar rawa wajen taimakon kasashen Afirka tinkarar manyan kalubaloli, musamman ma a fannonin aikin jinya da kiwon lafiya, da tabbatar da samar da isashen abinci, da dai sauransu.

  • Peng Liyuan Da Uwargidan Shugaban Poland Sun Ziyarci Cibiyar Gabatar Da Wasannin Fasahohi Ta Sin
  • An Yi Jana’izar Sirikar Ganduje A Kano

Furfesa Ikusika ya ambaci taimakon da kasar Sin ta ba kasashen Afirka, a kokarinsu na tinkarar annoba da cututtuka. Misali, bayan da aka samu barkewar annobar cutar Ebola a yankin yammacin Afirka a shekarar 2014, nan take kasar Sin ta tura kwararrun ma’aikata masu ilimin aikin likitanci zuwa wuraren da annobar ta shafa, inda suka yi aiki kafada da kafada da likitocin kasashen Afirka. An ce, ya zuwa shekarar 2015, an riga an tura kwararrun likitocin kasar Sin 102, cikin jeri 13, zuwa kasashen Afirka, inda suka ba da taimako kan kokarin yakar cutar Ebola, bisa ilimi da fasahohin da suka mallaka ta fuskar aikin likitanci. Sa’an nan, bayan da annobar cutar COVID-19 ta barke, kasar Sin ta ba da tallafin ginin hedkwatar cibiyar kandagarkin yaduwar cututtuka ta kungiyar kasashen Afirka (AU), wanda shi ma ya kansance alamar hadin gwiwar da Afirka da Sin suke yi ta fuskar kimiyya da fasaha masu alaka da aikin likitanci da kiwon lafiya.

Ban da haka, Farfesa Ikusika ya ambaci hadin kan kasashen Afirka da kasar Sin a fannin aikin gona, inda a wannan bangare, ya ba da misalin kasar Madagascar. A cewarsa, kasar ta dade tana fama da matsalar koma bayan fasaharta ta noman shinkafa. Ganin haka ya sa kasar fara hadin gwiwa da kasar Sin a shekarar 2007, inda ma’aikata masu fasahohi na kasar Sin suka fara yayata fasahar noman shinkafar da aka tagwaita irinta a kasar ta Madagascar, ta yadda yawan shinkafar da a kan girba a kasar ya karu zuwa ton 7.5 kan gona mai kadada guda. Zuwa yanzu, kasar tana kan gaba a tsakanin kasashen Afirka, a fannonin yawan noman shinkafar da aka tagwaita irinta, da yawan shinkafar da aka samar. Haka zalika, ita ce kasar Afirka daya tilo, wadda ta mallaki cikakken tsarin masana’atu mai alaka da shinkafar da aka tagwaita irinta, wanda ya kunshi bangarorin samar da iri, da noman shinkafa, da sarrafa ta, gami da sayar da kayayyakin abinci da aka hada da shinkafar.

Sa’an nan bisa matsayinsa na mai nazarin kimiyya da fasaha na kasar Afirka ta Kudu, Olusegun Ikusika ya ambaci wani bikin da gidan jakadancin Sin dake kasar Afirka ta Kudu ya gudanar, wanda ya ba matasan kasar damar hira tare da ‘yan saman jannatin kasar Sin dake cikin tashar binciken sararin samaniya ta kasar. A cewarsa, wannan biki ya ba kasashen Afirka ta Kudu da Sin damar kara fahimtar juna a bangaren kimiyya da fasaha, da janyo hankalin karin matasan kasar Afirka ta Kudu ga fasahohi masu alaka da zirga-zirgar kumbuna a sararin samaniya.

Labarai Masu Nasaba

Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe

Amurka: “Afirka Ba Ta Cikin Jerin Fannoni Da Muka Ba Da Fifiko A Kai”

Sai dai kafofin watsa labaru na kasashen yammacin duniya sun saba da shafa bakin fenti kan duk wani hadin gwiwar da ake yi tsakanin kasar Sin da kasashen Afirka. Misali, sun ce wai hadin kan Sin da Afirka ta fuskar kimiyya da fasaha ya nuna alamar “sabon nau’in mulkin mallaka”. Dangane da zancen, Farfesa Ikusika ya musanta cewa, ba a taba saka wani sharadi kan hadin gwiwar Sin da Afirka a fannin kimiyya da fasaha ba, kana wannan huldar hadin kai ta amfani kasashen Afirka, a kokarinsu na kawar da talauci, da neman samun ci gaban tattalin arziki. Alal misali, fasahar kasar Sin ta noman laimar kwado, wadda aka fi san ta da fasahar Juncao, ta riga ta zame wa dimbin manoman kasashen Afirka wata muhimmiyar dabarar samun wadata.

Hakika, duk mutumin da ya shaida yadda ma’aikata masu nazarin kimiyya da fasaha na kasar Sin suke gudanar da ayyukansu a nahiyar Afirka, to, ba zai taba nuna shakku kan sahihancinsu ba. Misali, a kasar Kenya, Farfesa Xiong Youcai da abokan aikinsa na jami’ar Lanzhou ta kasar Sin sun shiga kauyukan kasar har sau 30 cikin shekaru 12 da suka gabata, don yada fasahar noman masara mai tsimin ruwa ta hanyar amfani da wani nau’in leda na musamman wajen rufe gonaki, wadda ta sa aka samu karuwar masara da ta kai kashi 99% zuwa 240%. Wesly Kiprotich, wani matashi dan kasar Kenya ne dake bin Farfesa Xiong domin koyon ilimin aikin gona, a cewarsa, “Manoman kasarmu su kan kammala aiki da kimanin karfe 2 da wani abu da rana, amma Farfesa Xiong da abokan aikinsa su kan fara aiki da karfe 8 na safe, kuma ba sa gama aiki sai zuwa karfe 6 na maraice. Mutane suna mamaki, suna cewa kamar ba su san gajiya ba. ”

To, mene ne abun da Farfesa Xiong yake nema? A cewarsa, kawai yana neman ganin wata fasahar noma mai farin jini a kasar Sin, ta ci gaba da taka rawar gani a fannin ingiza aikin gona, bayan kai ta nahiyar Afirka. Wannan yunkuri na son ganin ci gaban harkoki a kasashen Afirka, ya zo daga tunanin Sinawa na “Al’ummar dan Adam mai makomar bai daya”. A ganin mutanen Sin, ya kamata dukkan mutanen duniya su samu damar jin dadin rayuwa, ta hakan ne za a iya tabbatar da zaman lafiya da ci gaban al’ummar dan Adam mai dorewa, a duniyarmu.

To, bisa wannan tunani mai muhimmanci, za mu san cewa, tabbas hadin gwiwar Sin da Afirka ta fuskar kimiyya da fasaha za ta ci gaba da amfanawa kokarin kasashen Afirka na raya tattalin arziki. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Alakar Sin da AfirkaKimiyyaNoma
ShareTweetSendShare
Previous Post

Henry Na Gab Da Zamowa Sabon Kocin Tawagar Kwallon Kafa Ta Kasar Wales

Next Post

Kafa Kananan Rukunoni Ba Zai Haifar Da Komai Ba Face Tsananta Sabani

Related

Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe
Ra'ayi Riga

Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe

4 hours ago
Amurka: “Afirka Ba Ta Cikin Jerin Fannoni Da Muka Ba Da Fifiko A Kai”
Ra'ayi Riga

Amurka: “Afirka Ba Ta Cikin Jerin Fannoni Da Muka Ba Da Fifiko A Kai”

4 days ago
Mai Cin Moriyar Kai Da Mai Cin Moriyar Juna
Ra'ayi Riga

Mai Cin Moriyar Kai Da Mai Cin Moriyar Juna

6 days ago
Bai Kamata a Rika Kai wa Fararen Hula Hari Ba!
Ra'ayi Riga

Bai Kamata a Rika Kai wa Fararen Hula Hari Ba!

2 weeks ago
Tursasawa Kasashen Afirka Karbar Bakin Haure Daga Amerika Kuskure Ne
Ra'ayi Riga

Tursasawa Kasashen Afirka Karbar Bakin Haure Daga Amerika Kuskure Ne

2 weeks ago
Wace Kasa Ce Take Son Zama “Kasa Ta Uku Mai Tsaro” A Wurin Amurka?
Ra'ayi Riga

Wace Kasa Ce Take Son Zama “Kasa Ta Uku Mai Tsaro” A Wurin Amurka?

2 weeks ago
Next Post
Kafa Kananan Rukunoni Ba Zai Haifar Da Komai Ba Face Tsananta Sabani

Kafa Kananan Rukunoni Ba Zai Haifar Da Komai Ba Face Tsananta Sabani

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Gwangwaje Ƴan Wasan Ƙwallon Kwando Ta Mata Da Dala $100,000 Kowace

Tinubu Ya Gwangwaje Ƴan Wasan Ƙwallon Kwando Ta Mata Da Dala $100,000 Kowace

August 4, 2025
Rundunar PLA Ta Yi Sintiri A Yankin Tekun Kudancin Sin Cikin Shirin Ko Ta-Kwana

Rundunar PLA Ta Yi Sintiri A Yankin Tekun Kudancin Sin Cikin Shirin Ko Ta-Kwana

August 4, 2025
Cinikin Kamfanoni a Kasar Sin Ya Ci Gaba Da Habaka Cikin Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Bana 

Cinikin Kamfanoni a Kasar Sin Ya Ci Gaba Da Habaka Cikin Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Bana 

August 4, 2025
Xi Jinping Ya Ba Da Muhimmin Umarnin Jin Ra’ayoyin Masu Amfani Da Intanet Kan Tsara Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-Biyar Na 15

Xi Jinping Ya Ba Da Muhimmin Umarnin Jin Ra’ayoyin Masu Amfani Da Intanet Kan Tsara Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-Biyar Na 15

August 4, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Kwato ₦21bn, Ta Kashe Ƴan Ta’adda 78 — DG NOA

Gwamnatin Tarayya Ta Kwato ₦21bn, Ta Kashe Ƴan Ta’adda 78 — DG NOA

August 4, 2025
Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe

Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe

August 4, 2025
Kwamitin Bincike Ya Miƙa Rahoto Kan Kwamishinan Sufuri Ga Gwamnatin Kano

Kwamitin Bincike Ya Miƙa Rahoto Kan Kwamishinan Sufuri Ga Gwamnatin Kano

August 4, 2025
Ruwan Wuta Ne Kawai Maganin ‘Yan Ta’adda Ba Sasanci Ba – Mataimakin Gwamnan Zamfara

Ruwan Wuta Ne Kawai Maganin ‘Yan Ta’adda Ba Sasanci Ba – Mataimakin Gwamnan Zamfara

August 4, 2025
Gwamna Buni Ya Bukaci Sabon Sarkin Gudi Ya Jagoranci Zaman Lafiya, Hadin Kai, Da Ci Gaban Kasa

Gwamna Buni Ya Bukaci Sabon Sarkin Gudi Ya Jagoranci Zaman Lafiya, Hadin Kai, Da Ci Gaban Kasa

August 4, 2025
Gina Tituna A Karkara Yana Bunkasa Tattalin Arziki – Gwamna Sule

Gina Tituna A Karkara Yana Bunkasa Tattalin Arziki – Gwamna Sule

August 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.