ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka A Fannin Kimiyya Da Fasaha Zai Taimakawa Afirka Wajen Samun Ci Gaba

by Sulaiman and CGTN Hausa
2 years ago
Sin

Gwamnatin kasar Sin ta gudanar da babban taron karrama masu nazarin kimiyya da fasaha a jiya, inda aka samar da dimbin kyaututuka ga fitattun ma’aikata masu nazarin kimiyya da fasaha na kasar, don yaba musu bisa muhimmiyar gudunmowar da suka samar a fannin nazari kan bangarori masu alaka da kimiyyar lissafi ta Physics, da aikin safiyo ta tauraron dan Adam mai hango abubuwan dake doron kasa, da sinadaran da ake amfani da su wajen hada kayayyakin latironi, gami da aikin gona, da dai sauransu. Mai bayar da kyautuka a wajen taron shi ne shugaban kasar Sin Xi Jinping, lamarin da ya nuna matukar muhimmancin da kasar Sin ta dora ma kimiyya da fasaha, da bangaren kirkire-kirkire. To, sai dai wane irin tasiri ci gaban kasar Sin ta fuskar kimiyya da fasaha zai samar wa kasashen Afirka?

Dangane da wannan tambaya, su ‘yan Afirka suke da ikon ba da amsa. Olusegun Oyebade Ikusika, wani shehun malami ne dake aiki a jami’ar Fort Hare ta kasar Afirka ta Kudu, wanda ke mai da hankali kan nazarin hadin gwiwar da ake yi tsakanin kasashen Afirka da kasar Sin ta fuskar kimiyya da fasaha, cikin shekarun nan. Yayin da yake hira da manema labaru na kasar Sin a kwanan baya, ya ce, ilimi da fasahohi na kasar Sin, da hadin gwiwar Afirka da Sin a fannin kimiyya da fasaha, suna taka muhimmiyar rawa wajen taimakon kasashen Afirka tinkarar manyan kalubaloli, musamman ma a fannonin aikin jinya da kiwon lafiya, da tabbatar da samar da isashen abinci, da dai sauransu.

  • Peng Liyuan Da Uwargidan Shugaban Poland Sun Ziyarci Cibiyar Gabatar Da Wasannin Fasahohi Ta Sin
  • An Yi Jana’izar Sirikar Ganduje A Kano

Furfesa Ikusika ya ambaci taimakon da kasar Sin ta ba kasashen Afirka, a kokarinsu na tinkarar annoba da cututtuka. Misali, bayan da aka samu barkewar annobar cutar Ebola a yankin yammacin Afirka a shekarar 2014, nan take kasar Sin ta tura kwararrun ma’aikata masu ilimin aikin likitanci zuwa wuraren da annobar ta shafa, inda suka yi aiki kafada da kafada da likitocin kasashen Afirka. An ce, ya zuwa shekarar 2015, an riga an tura kwararrun likitocin kasar Sin 102, cikin jeri 13, zuwa kasashen Afirka, inda suka ba da taimako kan kokarin yakar cutar Ebola, bisa ilimi da fasahohin da suka mallaka ta fuskar aikin likitanci. Sa’an nan, bayan da annobar cutar COVID-19 ta barke, kasar Sin ta ba da tallafin ginin hedkwatar cibiyar kandagarkin yaduwar cututtuka ta kungiyar kasashen Afirka (AU), wanda shi ma ya kansance alamar hadin gwiwar da Afirka da Sin suke yi ta fuskar kimiyya da fasaha masu alaka da aikin likitanci da kiwon lafiya.

ADVERTISEMENT

Ban da haka, Farfesa Ikusika ya ambaci hadin kan kasashen Afirka da kasar Sin a fannin aikin gona, inda a wannan bangare, ya ba da misalin kasar Madagascar. A cewarsa, kasar ta dade tana fama da matsalar koma bayan fasaharta ta noman shinkafa. Ganin haka ya sa kasar fara hadin gwiwa da kasar Sin a shekarar 2007, inda ma’aikata masu fasahohi na kasar Sin suka fara yayata fasahar noman shinkafar da aka tagwaita irinta a kasar ta Madagascar, ta yadda yawan shinkafar da a kan girba a kasar ya karu zuwa ton 7.5 kan gona mai kadada guda. Zuwa yanzu, kasar tana kan gaba a tsakanin kasashen Afirka, a fannonin yawan noman shinkafar da aka tagwaita irinta, da yawan shinkafar da aka samar. Haka zalika, ita ce kasar Afirka daya tilo, wadda ta mallaki cikakken tsarin masana’atu mai alaka da shinkafar da aka tagwaita irinta, wanda ya kunshi bangarorin samar da iri, da noman shinkafa, da sarrafa ta, gami da sayar da kayayyakin abinci da aka hada da shinkafar.

Sa’an nan bisa matsayinsa na mai nazarin kimiyya da fasaha na kasar Afirka ta Kudu, Olusegun Ikusika ya ambaci wani bikin da gidan jakadancin Sin dake kasar Afirka ta Kudu ya gudanar, wanda ya ba matasan kasar damar hira tare da ‘yan saman jannatin kasar Sin dake cikin tashar binciken sararin samaniya ta kasar. A cewarsa, wannan biki ya ba kasashen Afirka ta Kudu da Sin damar kara fahimtar juna a bangaren kimiyya da fasaha, da janyo hankalin karin matasan kasar Afirka ta Kudu ga fasahohi masu alaka da zirga-zirgar kumbuna a sararin samaniya.

LABARAI MASU NASABA

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta

Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin

Sai dai kafofin watsa labaru na kasashen yammacin duniya sun saba da shafa bakin fenti kan duk wani hadin gwiwar da ake yi tsakanin kasar Sin da kasashen Afirka. Misali, sun ce wai hadin kan Sin da Afirka ta fuskar kimiyya da fasaha ya nuna alamar “sabon nau’in mulkin mallaka”. Dangane da zancen, Farfesa Ikusika ya musanta cewa, ba a taba saka wani sharadi kan hadin gwiwar Sin da Afirka a fannin kimiyya da fasaha ba, kana wannan huldar hadin kai ta amfani kasashen Afirka, a kokarinsu na kawar da talauci, da neman samun ci gaban tattalin arziki. Alal misali, fasahar kasar Sin ta noman laimar kwado, wadda aka fi san ta da fasahar Juncao, ta riga ta zame wa dimbin manoman kasashen Afirka wata muhimmiyar dabarar samun wadata.

Hakika, duk mutumin da ya shaida yadda ma’aikata masu nazarin kimiyya da fasaha na kasar Sin suke gudanar da ayyukansu a nahiyar Afirka, to, ba zai taba nuna shakku kan sahihancinsu ba. Misali, a kasar Kenya, Farfesa Xiong Youcai da abokan aikinsa na jami’ar Lanzhou ta kasar Sin sun shiga kauyukan kasar har sau 30 cikin shekaru 12 da suka gabata, don yada fasahar noman masara mai tsimin ruwa ta hanyar amfani da wani nau’in leda na musamman wajen rufe gonaki, wadda ta sa aka samu karuwar masara da ta kai kashi 99% zuwa 240%. Wesly Kiprotich, wani matashi dan kasar Kenya ne dake bin Farfesa Xiong domin koyon ilimin aikin gona, a cewarsa, “Manoman kasarmu su kan kammala aiki da kimanin karfe 2 da wani abu da rana, amma Farfesa Xiong da abokan aikinsa su kan fara aiki da karfe 8 na safe, kuma ba sa gama aiki sai zuwa karfe 6 na maraice. Mutane suna mamaki, suna cewa kamar ba su san gajiya ba. ”

To, mene ne abun da Farfesa Xiong yake nema? A cewarsa, kawai yana neman ganin wata fasahar noma mai farin jini a kasar Sin, ta ci gaba da taka rawar gani a fannin ingiza aikin gona, bayan kai ta nahiyar Afirka. Wannan yunkuri na son ganin ci gaban harkoki a kasashen Afirka, ya zo daga tunanin Sinawa na “Al’ummar dan Adam mai makomar bai daya”. A ganin mutanen Sin, ya kamata dukkan mutanen duniya su samu damar jin dadin rayuwa, ta hakan ne za a iya tabbatar da zaman lafiya da ci gaban al’ummar dan Adam mai dorewa, a duniyarmu.

To, bisa wannan tunani mai muhimmanci, za mu san cewa, tabbas hadin gwiwar Sin da Afirka ta fuskar kimiyya da fasaha za ta ci gaba da amfanawa kokarin kasashen Afirka na raya tattalin arziki. (Bello Wang)

Sin
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • Sulaiman
    ‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna
Sin
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

MASU ALAKA

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta
Ra'ayi Riga

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta

September 8, 2026
Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin

September 4, 2026
Samun Rarar Kudin Ciniki Ba “Laifi” Ba Ne, Hadin Gwiwa Da Cin Moriya Tare Ita Ce Mafita Ga Kowa
Ra'ayi Riga

Samun Rarar Kudin Ciniki Ba “Laifi” Ba Ne, Hadin Gwiwa Da Cin Moriya Tare Ita Ce Mafita Ga Kowa

September 2, 2026
Next Post
Kafa Kananan Rukunoni Ba Zai Haifar Da Komai Ba Face Tsananta Sabani

Kafa Kananan Rukunoni Ba Zai Haifar Da Komai Ba Face Tsananta Sabani

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.