• English
  • Business News
Tuesday, August 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka A Fannin Tattalin Arzikin Dijital Ta Haifar Da Dimbin Sakamako

by CGTN Hausa
1 year ago
in Ra'ayi Riga
0
Hadin Gwiwar Sin Da Afirka A Fannin Tattalin Arzikin Dijital Ta Haifar Da Dimbin Sakamako
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A shekarun baya, manhajojin wayar salula da kamfanonin Sin suka zuba jari cikinsu na kara samun karbuwa a kasar Najeriya. Wani abokina ya taba gaya min cewa, ya kan yi amfani da Opay wajen tura kudi. Ya ce yadda ake amfani da shi na da sauki, saboda kusan babu wata dakatarwa. Sa’an nan wani aboki ya ambaci APP mai suna Boomplay, ya ce ya kan saurari wakoki a kansa, ganin yadda ake samun dimbin wakokin kasashen Afirka a cikin APP din. To, wadannan misalai sun nuna yadda hadin kan kasashen Afirka da kasar Sin ta fuskar tattalin arzikin dijital da ya shafi fasahohin zamani ya zurfafa.

A wajen taron kulla huldar hadin gwiwa tsakanin Sin da Afirka a fannonin tattalin arziki da cinikayya, da ya gudana a Nairobi na kasar Kenya, a kwanakin baya, jami’ar Hunan ta kasar Sin, da cibiyar binciken dabarun habaka hadin kan Sin da Afirka kan tattalin arizki da ciniki, sun gabatar da wani rahoto kan hadin kan Sin da Afirka ta fuskar tattalin arzikin dijital, inda suka yi cikakken bayani kan sakamakon da kasashen Afirka da kasar Sin suka samu, a kokarinsu na hadin gwiwa a fannin tattalin arikin dijital, cikin shekarun nan.

  • Sin Ta Kalubalanci Amurka Da Ta Samar Da Kyakkyawan Yanayin Hadin Gwiwa Kan Tinkarar Sauyin Yanayi Da Kyautata Tsarin Raya Tattalin Arzikin Duniya Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba
  • Xi Jinping Ya Nuna Matukar Godiya Ga Mahaifiyarsa

Rahoton ya nuna cewa, a fannin gina kayayyakin more rayuwa masu alaka da tattalin arzikin dijital, kasar Sin ta aiwatar da dimbin ayyuka na shimfida wayoyin sadarwa a karkashin teku, wadanda suka hada nahiyar Afirka da sauran nahiyoyi daban daban. Kana kamfanonin kasar Sin sun gina fiye da rabin tashohin wayar salula na kasashen Afirka.

A fannin samar da APP din wayar salula, dimbin kamfanonin hada-hadar kudi na kasar Sin na samar da hidimomin biyan kudi ta wayar salula, da tura kudi tsakanin kasashe, a nahiyar Afirka. Ban da haka, kamfanin Alibaba na kasar Sin ya yi hadin gwiwa tare da gwamnatin kasar Rwanda wajen kafa wani dandalin ciniki mai taken Afnea, wanda ya zama wani dandalin sarin kananan kayayyaki dake da farin jini a gabashin nahiyar Afirka.

Haka zalika, a fannin kirkiro fasahohi, kamfanin Huawei na kasar Sin ya kafa cibiyar adana alkaluma a kasar Afirka ta Kudu, wadda ta samar da hidimomi masu inganci da tsaro. Yayin da kamfanonin Sin ke hadin kai tare da kasashen Masar da Aljeriya, dai dai sauransu, wajen kafa cibiyar kula da ayyukan taurarin dan Adam ta kasar Sin da kasashen Afirka. Ban da haka, a fannin bayar da horo, Sin da kasashen Afirka sun kafa dimbin dandalin samar da ilimi da musayar fasahohi, karkashin hadin gwiwarsu.

Labarai Masu Nasaba

Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe

Amurka: “Afirka Ba Ta Cikin Jerin Fannoni Da Muka Ba Da Fifiko A Kai”

Wadannan abubuwa suna cikin dimbin sakamakon da aka ambata, cikin rahoton da aka gabatar, dangane da hadin gwiwar Sin da Afirka, ta fuskar tattalin arziki na dijital.

Sai dai me ya sa ake samun wannan yanayi mai armashi a hadin gwiwar Sin da Afirka a kokarinsu na raya tattalin arzikin dijital?

Da farko, an samu damar raya tattalin arzikin dijital a kasashen Afirka yanzu.

A fannin manufofi, kungiyar kasashen Afirka AU ta zartas da ajandar aiki ta shekarar 2063, inda ta saka burin mayar da nahiyar Afirka yankin tattalin arzikin dijital mai tsarin bai daya. Kana mambobin kungiyar sun dora muhimmanci kan raya tattalin arzikin dijital a cikin gida. Misali, kasar Najeriya ta tsara shirin kara saurin yanar gizo ko Internet, da sanya ta shafar karin mutane. Ban da haka, a fannin muhallin kasuwanci, habakar biranen kasashen Afirka cikin sauri ta samar da kasuwanni ga hidimomi na dijital, kana kafuwar yankin ciniki cikin ‘yanci na nahiyar Afirka ta ba da damar inganta hadin gwiwar kasashen Afirka ta fuskar tattalin arzikin dijital.

Na biyu, shi ne, fasahohin kasar Sin a fannin yanar gizo su ne a kan gaba a duniya.

An kammala aikin gina kayayyakin more rayuwa masu alaka da fasahohin sadarwa mafi girma a duniya, a kasar ta Sin, ta yadda ko a cikin kauyukan kasar ma, ana samun ingantaccen tsarin sadarwa. Ban da haka, kasar ita ta fara rungumar fasahar sadarwa mai inganci ta 5G, inda a karshen shekarar 2023, yawan al’ummar kasar masu wayoyin salula dake aiki da 5G ya kai miliyan 805. Ban da haka, kasar Sin ta kware a fannin kirkirar sabbin fasahohi, abin da ya sa ta kan gaba a duniya a fannonin mallakar fasahohi masu alaka da na’urorin kwaikwayon tunanin dan Adam, da aikin tsara karamin kayan latironi na Chip, da dai sauransu.

Kana dalili na uku shi ne, akidar kasar Sin ta fuskar hadin kai tare da kasashen Afirka bisa gaskiya, da kauna, da sahihanci, gami da samar da sakamako na zahiri, ta sa kasar yarda da gabatar da ingantattun fasahohi, da damammakin raya kasa, ga bangarorin Afirka.

Cikin shawarar kafa al’umma mai makomar bai daya a fannin yanar gizo bisa hadin gwiwar Sin da Afirka, da kasar Sin ta gabatar, kasar ta yi alkawarin taimakawa kasashen Afirka wajen gina kayayyakin aikin sadarwa, da kula da yanar gizo, da sayar da kayayyaki ga kasuwannin Sin ta hanyar cinikin yanar gizo, da kuma rage talauci ta hanyar amfani da fasahohin zamani, da sauransu.

A lokacin baya, mutane kalilan na kasashen Afirka ne suke da damar duba shafukan yanar gizo ko Internet. Amma zuwa yanzu, ci gaban fasahohi ya sa dimbin mazauna yankunan karkara na nahiyar Afirka na iya kallon shafukan Internet ta wayar salula, don more damammakin sadarwa da samun bayanai. Ta haka za mu iya ganin yadda fasahohin zamani ke haifar da rayuwa mai inganci a nahiyar Afirka. Sa’an nan abun da kasar Sin ke yi yanzu, shi ne kara saurin shigar da ingantattun fasahohi cikin nahiyar Afirka, ta yadda za a ba dukkan bangarorin Sin da Afirka damar amfanar juna, da samun ci gaba na bai daya. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AfirkaKenyaNahiyar Turai
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sanata Hanga Ya Kare Sukar Da Ake Yi Masa Kan Tallafin Tukwanen Yumɓu Da Likafani

Next Post

Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Bindiga A Kaduna

Related

Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe
Ra'ayi Riga

Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe

1 day ago
Amurka: “Afirka Ba Ta Cikin Jerin Fannoni Da Muka Ba Da Fifiko A Kai”
Ra'ayi Riga

Amurka: “Afirka Ba Ta Cikin Jerin Fannoni Da Muka Ba Da Fifiko A Kai”

5 days ago
Mai Cin Moriyar Kai Da Mai Cin Moriyar Juna
Ra'ayi Riga

Mai Cin Moriyar Kai Da Mai Cin Moriyar Juna

1 week ago
Bai Kamata a Rika Kai wa Fararen Hula Hari Ba!
Ra'ayi Riga

Bai Kamata a Rika Kai wa Fararen Hula Hari Ba!

2 weeks ago
Tursasawa Kasashen Afirka Karbar Bakin Haure Daga Amerika Kuskure Ne
Ra'ayi Riga

Tursasawa Kasashen Afirka Karbar Bakin Haure Daga Amerika Kuskure Ne

2 weeks ago
Wace Kasa Ce Take Son Zama “Kasa Ta Uku Mai Tsaro” A Wurin Amurka?
Ra'ayi Riga

Wace Kasa Ce Take Son Zama “Kasa Ta Uku Mai Tsaro” A Wurin Amurka?

2 weeks ago
Next Post
Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Bindiga A Kaduna

Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Bindiga A Kaduna

LABARAI MASU NASABA

Shugaban ‘Yan Bindiga A Zamfara, Bello Turji, Ya Ajiye Makamai, Ya Saki Mutane 32

Shugaban ‘Yan Bindiga A Zamfara, Bello Turji, Ya Ajiye Makamai, Ya Saki Mutane 32

August 5, 2025
Xizang Ya Cimma Nasarorin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Suka Kafa Tarihi Cikin Shekaru Fiye Da 60

Xizang Ya Cimma Nasarorin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Suka Kafa Tarihi Cikin Shekaru Fiye Da 60

August 5, 2025
Gwamnatin Yobe Za Ta Yi Taron Girmama Ɗalibar Turanci Ta Duniya, Nafisa Abdullah

Gwamnatin Yobe Za Ta Yi Taron Girmama Ɗalibar Turanci Ta Duniya, Nafisa Abdullah

August 5, 2025
Gwamna Aiyedatiwa Ya Bai wa Ƴar Super Falcons Tosin Demehin ₦30m Da Gida

Gwamna Aiyedatiwa Ya Bai wa Ƴar Super Falcons Tosin Demehin ₦30m Da Gida

August 5, 2025
LASTMA Ta Rufe Gidan Casu A Legas Saboda Karya Dokar Hanya

LASTMA Ta Rufe Gidan Casu A Legas Saboda Karya Dokar Hanya

August 5, 2025
Ƴansanda Sun Kama Ƴan Uwa da Wasu Biyu Kan Ƙirkirar Garkuwa Da Kansu A Abuja

Ƴansanda Sun Kama Ƴan Uwa da Wasu Biyu Kan Ƙirkirar Garkuwa Da Kansu A Abuja

August 5, 2025
Tsauraran Manufofin Tattalin Arziƙin Tinubu Ya Ƙara Yawan Matalauta – Falana

Tsauraran Manufofin Tattalin Arziƙin Tinubu Ya Ƙara Yawan Matalauta – Falana

August 5, 2025
BUA Siminti Ya Ƙaddamar Da Shirin Horas Da Matasan Sakkwato

BUA Siminti Ya Ƙaddamar Da Shirin Horas Da Matasan Sakkwato

August 4, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Masu Samar Da Hidimar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Masu Samar Da Hidimar Intanet

August 4, 2025
Tinubu Ya Gwangwaje Ƴan Wasan Ƙwallon Kwando Ta Mata Da Dala $100,000 Kowace

Tinubu Ya Gwangwaje Ƴan Wasan Ƙwallon Kwando Ta Mata Da Dala $100,000 Kowace

August 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.