• English
  • Business News
Thursday, September 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka A Fannin Tattalin Arzikin Dijital Ta Haifar Da Dimbin Sakamako

by CGTN Hausa
1 year ago
in Ra'ayi Riga
0
Hadin Gwiwar Sin Da Afirka A Fannin Tattalin Arzikin Dijital Ta Haifar Da Dimbin Sakamako
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A shekarun baya, manhajojin wayar salula da kamfanonin Sin suka zuba jari cikinsu na kara samun karbuwa a kasar Najeriya. Wani abokina ya taba gaya min cewa, ya kan yi amfani da Opay wajen tura kudi. Ya ce yadda ake amfani da shi na da sauki, saboda kusan babu wata dakatarwa. Sa’an nan wani aboki ya ambaci APP mai suna Boomplay, ya ce ya kan saurari wakoki a kansa, ganin yadda ake samun dimbin wakokin kasashen Afirka a cikin APP din. To, wadannan misalai sun nuna yadda hadin kan kasashen Afirka da kasar Sin ta fuskar tattalin arzikin dijital da ya shafi fasahohin zamani ya zurfafa.

A wajen taron kulla huldar hadin gwiwa tsakanin Sin da Afirka a fannonin tattalin arziki da cinikayya, da ya gudana a Nairobi na kasar Kenya, a kwanakin baya, jami’ar Hunan ta kasar Sin, da cibiyar binciken dabarun habaka hadin kan Sin da Afirka kan tattalin arizki da ciniki, sun gabatar da wani rahoto kan hadin kan Sin da Afirka ta fuskar tattalin arzikin dijital, inda suka yi cikakken bayani kan sakamakon da kasashen Afirka da kasar Sin suka samu, a kokarinsu na hadin gwiwa a fannin tattalin arikin dijital, cikin shekarun nan.

  • Sin Ta Kalubalanci Amurka Da Ta Samar Da Kyakkyawan Yanayin Hadin Gwiwa Kan Tinkarar Sauyin Yanayi Da Kyautata Tsarin Raya Tattalin Arzikin Duniya Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba
  • Xi Jinping Ya Nuna Matukar Godiya Ga Mahaifiyarsa

Rahoton ya nuna cewa, a fannin gina kayayyakin more rayuwa masu alaka da tattalin arzikin dijital, kasar Sin ta aiwatar da dimbin ayyuka na shimfida wayoyin sadarwa a karkashin teku, wadanda suka hada nahiyar Afirka da sauran nahiyoyi daban daban. Kana kamfanonin kasar Sin sun gina fiye da rabin tashohin wayar salula na kasashen Afirka.

A fannin samar da APP din wayar salula, dimbin kamfanonin hada-hadar kudi na kasar Sin na samar da hidimomin biyan kudi ta wayar salula, da tura kudi tsakanin kasashe, a nahiyar Afirka. Ban da haka, kamfanin Alibaba na kasar Sin ya yi hadin gwiwa tare da gwamnatin kasar Rwanda wajen kafa wani dandalin ciniki mai taken Afnea, wanda ya zama wani dandalin sarin kananan kayayyaki dake da farin jini a gabashin nahiyar Afirka.

Haka zalika, a fannin kirkiro fasahohi, kamfanin Huawei na kasar Sin ya kafa cibiyar adana alkaluma a kasar Afirka ta Kudu, wadda ta samar da hidimomi masu inganci da tsaro. Yayin da kamfanonin Sin ke hadin kai tare da kasashen Masar da Aljeriya, dai dai sauransu, wajen kafa cibiyar kula da ayyukan taurarin dan Adam ta kasar Sin da kasashen Afirka. Ban da haka, a fannin bayar da horo, Sin da kasashen Afirka sun kafa dimbin dandalin samar da ilimi da musayar fasahohi, karkashin hadin gwiwarsu.

Labarai Masu Nasaba

Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci

Tarihi: Mugunta Ba Za Ta Iya Lashe Adalci Ba

Wadannan abubuwa suna cikin dimbin sakamakon da aka ambata, cikin rahoton da aka gabatar, dangane da hadin gwiwar Sin da Afirka, ta fuskar tattalin arziki na dijital.

Sai dai me ya sa ake samun wannan yanayi mai armashi a hadin gwiwar Sin da Afirka a kokarinsu na raya tattalin arzikin dijital?

Da farko, an samu damar raya tattalin arzikin dijital a kasashen Afirka yanzu.

A fannin manufofi, kungiyar kasashen Afirka AU ta zartas da ajandar aiki ta shekarar 2063, inda ta saka burin mayar da nahiyar Afirka yankin tattalin arzikin dijital mai tsarin bai daya. Kana mambobin kungiyar sun dora muhimmanci kan raya tattalin arzikin dijital a cikin gida. Misali, kasar Najeriya ta tsara shirin kara saurin yanar gizo ko Internet, da sanya ta shafar karin mutane. Ban da haka, a fannin muhallin kasuwanci, habakar biranen kasashen Afirka cikin sauri ta samar da kasuwanni ga hidimomi na dijital, kana kafuwar yankin ciniki cikin ‘yanci na nahiyar Afirka ta ba da damar inganta hadin gwiwar kasashen Afirka ta fuskar tattalin arzikin dijital.

Na biyu, shi ne, fasahohin kasar Sin a fannin yanar gizo su ne a kan gaba a duniya.

An kammala aikin gina kayayyakin more rayuwa masu alaka da fasahohin sadarwa mafi girma a duniya, a kasar ta Sin, ta yadda ko a cikin kauyukan kasar ma, ana samun ingantaccen tsarin sadarwa. Ban da haka, kasar ita ta fara rungumar fasahar sadarwa mai inganci ta 5G, inda a karshen shekarar 2023, yawan al’ummar kasar masu wayoyin salula dake aiki da 5G ya kai miliyan 805. Ban da haka, kasar Sin ta kware a fannin kirkirar sabbin fasahohi, abin da ya sa ta kan gaba a duniya a fannonin mallakar fasahohi masu alaka da na’urorin kwaikwayon tunanin dan Adam, da aikin tsara karamin kayan latironi na Chip, da dai sauransu.

Kana dalili na uku shi ne, akidar kasar Sin ta fuskar hadin kai tare da kasashen Afirka bisa gaskiya, da kauna, da sahihanci, gami da samar da sakamako na zahiri, ta sa kasar yarda da gabatar da ingantattun fasahohi, da damammakin raya kasa, ga bangarorin Afirka.

Cikin shawarar kafa al’umma mai makomar bai daya a fannin yanar gizo bisa hadin gwiwar Sin da Afirka, da kasar Sin ta gabatar, kasar ta yi alkawarin taimakawa kasashen Afirka wajen gina kayayyakin aikin sadarwa, da kula da yanar gizo, da sayar da kayayyaki ga kasuwannin Sin ta hanyar cinikin yanar gizo, da kuma rage talauci ta hanyar amfani da fasahohin zamani, da sauransu.

A lokacin baya, mutane kalilan na kasashen Afirka ne suke da damar duba shafukan yanar gizo ko Internet. Amma zuwa yanzu, ci gaban fasahohi ya sa dimbin mazauna yankunan karkara na nahiyar Afirka na iya kallon shafukan Internet ta wayar salula, don more damammakin sadarwa da samun bayanai. Ta haka za mu iya ganin yadda fasahohin zamani ke haifar da rayuwa mai inganci a nahiyar Afirka. Sa’an nan abun da kasar Sin ke yi yanzu, shi ne kara saurin shigar da ingantattun fasahohi cikin nahiyar Afirka, ta yadda za a ba dukkan bangarorin Sin da Afirka damar amfanar juna, da samun ci gaba na bai daya. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AfirkaKenyaNahiyar Turai
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sanata Hanga Ya Kare Sukar Da Ake Yi Masa Kan Tallafin Tukwanen Yumɓu Da Likafani

Next Post

Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Bindiga A Kaduna

Related

Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci
Ra'ayi Riga

Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci

1 day ago
Tarihi: Mugunta Ba Za Ta Iya Lashe Adalci Ba
Ra'ayi Riga

Tarihi: Mugunta Ba Za Ta Iya Lashe Adalci Ba

1 week ago
Ci Gaban Sojojin Sin Yana Hidimar Manufar Zaman Lafiya A Ko Da Yaushe
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Sojojin Sin Yana Hidimar Manufar Zaman Lafiya A Ko Da Yaushe

2 weeks ago
Kowa Ya Ci Zomo Ya Ci Gudu: Shekaru 80 Da Nasarar Sinawa A Kan Zalunci Da Danniyar Japanawa
Ra'ayi Riga

Kowa Ya Ci Zomo Ya Ci Gudu: Shekaru 80 Da Nasarar Sinawa A Kan Zalunci Da Danniyar Japanawa

2 weeks ago
Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Ba Da Gudummawarta Wajen Kiyaye Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya 
Ra'ayi Riga

Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Ba Da Gudummawarta Wajen Kiyaye Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya 

2 weeks ago
Sin: Bin Tafarki Na Gaskiya
Ra'ayi Riga

Sin: Bin Tafarki Na Gaskiya

2 weeks ago
Next Post
Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Bindiga A Kaduna

Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Bindiga A Kaduna

LABARAI MASU NASABA

Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

September 17, 2025
Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

September 17, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

September 17, 2025
Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

September 17, 2025
Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

September 17, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Baje Kolin Sin Da ASEAN Ya Fadada Matsayar Bai Daya Ta Cudanyar Sassa Daban Daban

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Baje Kolin Sin Da ASEAN Ya Fadada Matsayar Bai Daya Ta Cudanyar Sassa Daban Daban

September 17, 2025
Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye

Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye

September 17, 2025
An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 

An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 

September 17, 2025
‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

September 17, 2025
Har Kullum Burin Sin Shi Ne Wanzar Da Daidaito Da Cimma Moriya Tare Da Amurka

Har Kullum Burin Sin Shi Ne Wanzar Da Daidaito Da Cimma Moriya Tare Da Amurka

September 17, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.