• English
  • Business News
Wednesday, June 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Ya Shaida Cewa Ba Lallai Ba Ne A Ci Nasara Daga Faduwar Wani Bangare Ba

by CGTN Hausa and Sulaiman
10 months ago
in Ra'ayi Riga
0
Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Ya Shaida Cewa Ba Lallai Ba Ne A Ci Nasara Daga Faduwar Wani Bangare Ba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan harkokin wajen tarayyar Nijeriya, Yusuf Maitama Tuggar ya ce, “mu baligai ne, kada kasashen yamma su dauke mu a matsayin yara, don muna da ‘yancin zabin abin da muke so.” Ministan ya yi furucin ne a lokacin da yake amsa tambayar wakilin kafar CGTN, a yayin taron kolin dandalin hadin gwiwar Sin da Afirka (FOCAC) da ya gudana a kwanakin baya a birnin Beijing.

 

Tabbas kasar Sin ta samu ci gaban a zo a gani a cikin ‘yan shekarun nan, sai dai hakan ya sa wasu mutanen kasashen Amurka da yammacin duniya ba su ji dadi ba, don haka, suka yi ta yayata kalaman wai “Sin barazana ce”, tare da shafa wa kasar bakin fenti kan cewa wai tana kafa “sabon salon mulkin mallaka” a kasashen Afirka da ma jefa kasashen cikin matsalolin basussuka. Amma wadannan mutane sun sha kaye a yunkurinsu na lalata huldar da ke tsakanin Sin da kasashen Afirka, sabo da ba su san ainihin dalilin da ya sa Sin da kasashen Afirka suke rungumar juna ba.

  • Xi Jinping Ya Taya Murnar Ranar Malamai Ta Kasar Sin
  • Nijeriya Ta Samu Lambobin Yabo 7 A Wasannin Nakasassu Ta Bana

A hakika, ba wai cikin ‘yan shekarun nan ne huldar da ke tsakanin Sin da kasahen Afirka ta bunkasa ba. Kasar Sin ta fara taimaka wa kasashen Afirka ne tun a lokacin da ita kanta ke cikin kangin talauci. A farkon shekarun 1970, bayan da kasashe masu ci gaba suka ki taimaka musu, sai Tanzania da Zambia suka juya ga kasar Sin suka roke ta don ta ba da taimakon gina wata layin dogon da zai hada kasashen biyu. Daga baya, magina da injiniyoyi sama da dubu 50 na kasar Sin sun yi iyakacin kokarin kammala wannan aikin da a bakin kasashen yamma abu ne da ba zai yiwu ba, matakin da ya samar da muhimmin taimako ga kasashen biyu da ba da jimawa ba suka samu ‘yancin kansu wajen tabbatar da dogaro da kai ta fannin tattalin arziki. A kuma cikin shekarun 1970, kasashen Afirka ne suka ba da muhimmin taimako wajen maido da kujerar kasar Sin a MDD, wadanda suka tsaya tare da kasar Sin wajen kiyaye halastacciyar moriyarta a duniya.

 

Labarai Masu Nasaba

Nuna Karfin Tuwo Ba Zai Kawo Zaman Lafiya Ga Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba

Daga Xi’an Zuwa Astana: Me Muka Koya Daga Taron Kolin Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya

Sin da kasashen Afirka sun fara kulla abota ne a lokacin da suke gwagwarmayyar neman ‘yancin kansu, wadda ta kara bunkasa a lokacin da suke kokarin neman ci gabansu. Da aka shiga sabon karni na 21, bisa tsarin dandalin FOCAC da ma shawarar “Ziri Daya da Hanya Daya”, kasar Sin ta taimaka wa kasashen Afirka gina ko gyara hanyoyin mota da tsawonsu ya kai kusan kilomita dubu 100, da ma layukan dogo sama da kilomita dubu 10, sai kuma gadoji kusan dubu da tashoshin jiragen ruwa kusan 100…A sa’i daya kuma, kasashen Afirka ma sun yi kokarin ba wa kasar Sin taimako gwargwadon karfinsu. Ba za mu taba mantawa ba, a lokacin da mummunar girgizar kasa ta afkawa gundumar Wenchuan ta kasar Sin a shekarar 2008, kasar Equatorial Guinea ta samar wa kasar Sin gudummawar kudin Euro miliyan guda, daga baya, ta kuma samar da miliyoyin daloli na gina wata makarantar firamare a lardin Yunnan da ke kudu maso yammacin kasar Sin.

 

Yanzu haka, kasar Sin na kokarin zamanintar da kanta, kuma zamanintar da kansu buri ne na bai daya ga kasashen Afirka. A gun taron kolin FOCAC na wannan karo, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya sanar da wasu shirye-shiryen kawance guda 10 da ake son aiwatarwa tare da kasashen Afirka nan da shekaru uku masu zuwa a kokarin zamanintar da kansu, shirye-shiryen da suka shafi fannoni 10 da suka hada da musayar al’adu da hada-hadar cinikayya da hadin gwiwar tsarin masana’antu da hadewa da juna da sauransu. Domin aiwatar da shirye-shiryen, gwamnatin kasar Sin za ta kuma samar da tallafin kudi da yawansa ya kai yuan biliyan 360 nan da shekaru uku masu zuwa. A cewar shugaba Xi Jinping, “Ba za a bar kowace kasa a baya ba a kokarin da ake yi na zamanintar da kai.”

 

Makomar Sin da kasashen Afirka daya ce a kullum, makamantan abubuwan da suka faru gare su a tarihi da ma burinsu na bai daya ya hada su tare, daidai kamar yadda karin magana na Afirka ya bayyana, wadanda ke bin hanya daya su ne abokai na gaske.

 

A gun taron kolin, shugaban tarayyar Nijeriya ya ce, hadin gwiwar Sin da kasashen Afirka da ke cike da nasarori ya shaida cewa, ba lallai ba ne a ci nasara daga faduwar wani bangare a yayin da kasa da kasa ke neman ci gabansu. Abin haka yake, a zamanin da muke ciki na dunkulewar tattalin arzikin duniya, kasa da kasa sun kasance suna cude-ni-in-cude-ka, kuma duniyarmu na da girman da ya ishi kasa da kasa su samu ci gaba tare, ba sai an ci nasara daga faduwar wani bangare ba.

 

A yayin da huldar da ke tsakanin Sin da kasashen Afirka ke dada bunkasa, karin kasashe na mai da hankalinsu a kan Afirka, hakan ya sa kasar Sin matukar farin ciki. Kasar Sin na maraba da kasa da kasa da su kara ba wa kasashen Afirka goyon baya da kuma taimaka musu, sabo da ci gaban dan Adam ba ya iya rabuwa da ci gaban kasashen Afirka, kuma idan ba a kai ga zamanintar da kasashen Afirka ba, to, ba maganar zamanintarwar duniya ke nan.(Lubabatu Lei)

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin: Ya Kamata Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Da Afirka Ta Kasance Cikin Adalci, Daidaito Kuma A Bayyane

Next Post

Ambaliya: Fursunoni 200 Sun Tsere Daga Gidan Yari A Maiduguri

Related

Nuna Karfin Tuwo Ba Zai Kawo Zaman Lafiya Ga Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba
Ra'ayi Riga

Nuna Karfin Tuwo Ba Zai Kawo Zaman Lafiya Ga Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba

14 hours ago
Daga Xi’an Zuwa Astana: Me Muka Koya Daga Taron Kolin Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya
Ra'ayi Riga

Daga Xi’an Zuwa Astana: Me Muka Koya Daga Taron Kolin Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya

6 days ago
Yafe Harajin Fito: Kasar Sin Na Cika Alkawarinta
Ra'ayi Riga

Yafe Harajin Fito: Kasar Sin Na Cika Alkawarinta

7 days ago
Daga Taklimakan Zuwa Sahara: Karin Abubuwan Al’ajabi Na Faruwa Bisa Hadin Gwiwar Sin Da Afirka A Fannin Yaki Da Kwararar Hamada
Ra'ayi Riga

Daga Taklimakan Zuwa Sahara: Karin Abubuwan Al’ajabi Na Faruwa Bisa Hadin Gwiwar Sin Da Afirka A Fannin Yaki Da Kwararar Hamada

1 week ago
Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Kara Habaka Daga Manyan Tsare-Tsare Zuwa Matakai Na Ainihi
Ra'ayi Riga

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Kara Habaka Daga Manyan Tsare-Tsare Zuwa Matakai Na Ainihi

2 weeks ago
Guguwa Za Ta Sa Kasashen Sin Da Afirka Su Kara Rike Hannayen Juna
Ra'ayi Riga

Guguwa Za Ta Sa Kasashen Sin Da Afirka Su Kara Rike Hannayen Juna

2 weeks ago
Next Post
Ambaliya: Fursunoni 200 Sun Tsere Daga Gidan Yari A Maiduguri

Ambaliya: Fursunoni 200 Sun Tsere Daga Gidan Yari A Maiduguri

LABARAI MASU NASABA

Sayar Da Makamai: Goyon Baya Ko Cin Riba?

Sayar Da Makamai: Goyon Baya Ko Cin Riba?

June 24, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Ƙaryata Rahoton Karɓo Lamuni Da Wata Jarida Ta Yaɗa

Gwamnatin Zamfara Ta Ƙaryata Rahoton Karɓo Lamuni Da Wata Jarida Ta Yaɗa

June 24, 2025
Kasar Sin Na Fatan Isra’ila Da Iran Za Su Tsagaita Bude Wuta Nan Bada Jimawa Ba

Kasar Sin Na Fatan Isra’ila Da Iran Za Su Tsagaita Bude Wuta Nan Bada Jimawa Ba

June 24, 2025
Majalisa Ta Yi Allah-wadai Da Kashe Wasu Matafiya ‘Yan Kaduna 13 A Jihar Filato

Majalisa Ta Yi Allah-wadai Da Kashe Wasu Matafiya ‘Yan Kaduna 13 A Jihar Filato

June 24, 2025
Al’ummun Afrika Da Sin Ba Za Su Taba Mantawa Da Gudunmuwar Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ba

Al’ummun Afrika Da Sin Ba Za Su Taba Mantawa Da Gudunmuwar Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ba

June 24, 2025
Barau Ya Nisanta Kansa Daga Kiraye-kirayen Ya Zama Mataimakin Tinubu A Zaben 2027

Barau Ya Nisanta Kansa Daga Kiraye-kirayen Ya Zama Mataimakin Tinubu A Zaben 2027

June 24, 2025
Shugabannin PDP Sun Ziyarci INEC Kan Neman Sanin Ka’idojinta

Shugabannin PDP Sun Ziyarci INEC Kan Neman Sanin Ka’idojinta

June 24, 2025
Sin Da Kasashen Musulmi Za Su Kara Zurfafa Dangantakarsu

Sin Da Kasashen Musulmi Za Su Kara Zurfafa Dangantakarsu

June 24, 2025
Sabbin Ministoci

Majalisar Dattawa Ta Kara Tsawaita Aiwatar Da Ayyukan Kasafin Kudi Na 2024 Da Wata 6

June 24, 2025
Nuna Karfin Tuwo Ba Zai Kawo Zaman Lafiya Ga Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba

Nuna Karfin Tuwo Ba Zai Kawo Zaman Lafiya Ga Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba

June 24, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.