• English
  • Business News
Wednesday, July 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Ya Shaida Cewa Ba Lallai Ba Ne A Ci Nasara Daga Faduwar Wani Bangare Ba

by CGTN Hausa and Sulaiman
10 months ago
in Ra'ayi Riga
0
Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Ya Shaida Cewa Ba Lallai Ba Ne A Ci Nasara Daga Faduwar Wani Bangare Ba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan harkokin wajen tarayyar Nijeriya, Yusuf Maitama Tuggar ya ce, “mu baligai ne, kada kasashen yamma su dauke mu a matsayin yara, don muna da ‘yancin zabin abin da muke so.” Ministan ya yi furucin ne a lokacin da yake amsa tambayar wakilin kafar CGTN, a yayin taron kolin dandalin hadin gwiwar Sin da Afirka (FOCAC) da ya gudana a kwanakin baya a birnin Beijing.

 

Tabbas kasar Sin ta samu ci gaban a zo a gani a cikin ‘yan shekarun nan, sai dai hakan ya sa wasu mutanen kasashen Amurka da yammacin duniya ba su ji dadi ba, don haka, suka yi ta yayata kalaman wai “Sin barazana ce”, tare da shafa wa kasar bakin fenti kan cewa wai tana kafa “sabon salon mulkin mallaka” a kasashen Afirka da ma jefa kasashen cikin matsalolin basussuka. Amma wadannan mutane sun sha kaye a yunkurinsu na lalata huldar da ke tsakanin Sin da kasashen Afirka, sabo da ba su san ainihin dalilin da ya sa Sin da kasashen Afirka suke rungumar juna ba.

  • Xi Jinping Ya Taya Murnar Ranar Malamai Ta Kasar Sin
  • Nijeriya Ta Samu Lambobin Yabo 7 A Wasannin Nakasassu Ta Bana

A hakika, ba wai cikin ‘yan shekarun nan ne huldar da ke tsakanin Sin da kasahen Afirka ta bunkasa ba. Kasar Sin ta fara taimaka wa kasashen Afirka ne tun a lokacin da ita kanta ke cikin kangin talauci. A farkon shekarun 1970, bayan da kasashe masu ci gaba suka ki taimaka musu, sai Tanzania da Zambia suka juya ga kasar Sin suka roke ta don ta ba da taimakon gina wata layin dogon da zai hada kasashen biyu. Daga baya, magina da injiniyoyi sama da dubu 50 na kasar Sin sun yi iyakacin kokarin kammala wannan aikin da a bakin kasashen yamma abu ne da ba zai yiwu ba, matakin da ya samar da muhimmin taimako ga kasashen biyu da ba da jimawa ba suka samu ‘yancin kansu wajen tabbatar da dogaro da kai ta fannin tattalin arziki. A kuma cikin shekarun 1970, kasashen Afirka ne suka ba da muhimmin taimako wajen maido da kujerar kasar Sin a MDD, wadanda suka tsaya tare da kasar Sin wajen kiyaye halastacciyar moriyarta a duniya.

 

Labarai Masu Nasaba

Girman Kai Da Son Zuciya Ba Za Su Sa A Amince Ko Ba Da Hadin Kai Ba

“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

Sin da kasashen Afirka sun fara kulla abota ne a lokacin da suke gwagwarmayyar neman ‘yancin kansu, wadda ta kara bunkasa a lokacin da suke kokarin neman ci gabansu. Da aka shiga sabon karni na 21, bisa tsarin dandalin FOCAC da ma shawarar “Ziri Daya da Hanya Daya”, kasar Sin ta taimaka wa kasashen Afirka gina ko gyara hanyoyin mota da tsawonsu ya kai kusan kilomita dubu 100, da ma layukan dogo sama da kilomita dubu 10, sai kuma gadoji kusan dubu da tashoshin jiragen ruwa kusan 100…A sa’i daya kuma, kasashen Afirka ma sun yi kokarin ba wa kasar Sin taimako gwargwadon karfinsu. Ba za mu taba mantawa ba, a lokacin da mummunar girgizar kasa ta afkawa gundumar Wenchuan ta kasar Sin a shekarar 2008, kasar Equatorial Guinea ta samar wa kasar Sin gudummawar kudin Euro miliyan guda, daga baya, ta kuma samar da miliyoyin daloli na gina wata makarantar firamare a lardin Yunnan da ke kudu maso yammacin kasar Sin.

 

Yanzu haka, kasar Sin na kokarin zamanintar da kanta, kuma zamanintar da kansu buri ne na bai daya ga kasashen Afirka. A gun taron kolin FOCAC na wannan karo, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya sanar da wasu shirye-shiryen kawance guda 10 da ake son aiwatarwa tare da kasashen Afirka nan da shekaru uku masu zuwa a kokarin zamanintar da kansu, shirye-shiryen da suka shafi fannoni 10 da suka hada da musayar al’adu da hada-hadar cinikayya da hadin gwiwar tsarin masana’antu da hadewa da juna da sauransu. Domin aiwatar da shirye-shiryen, gwamnatin kasar Sin za ta kuma samar da tallafin kudi da yawansa ya kai yuan biliyan 360 nan da shekaru uku masu zuwa. A cewar shugaba Xi Jinping, “Ba za a bar kowace kasa a baya ba a kokarin da ake yi na zamanintar da kai.”

 

Makomar Sin da kasashen Afirka daya ce a kullum, makamantan abubuwan da suka faru gare su a tarihi da ma burinsu na bai daya ya hada su tare, daidai kamar yadda karin magana na Afirka ya bayyana, wadanda ke bin hanya daya su ne abokai na gaske.

 

A gun taron kolin, shugaban tarayyar Nijeriya ya ce, hadin gwiwar Sin da kasashen Afirka da ke cike da nasarori ya shaida cewa, ba lallai ba ne a ci nasara daga faduwar wani bangare a yayin da kasa da kasa ke neman ci gabansu. Abin haka yake, a zamanin da muke ciki na dunkulewar tattalin arzikin duniya, kasa da kasa sun kasance suna cude-ni-in-cude-ka, kuma duniyarmu na da girman da ya ishi kasa da kasa su samu ci gaba tare, ba sai an ci nasara daga faduwar wani bangare ba.

 

A yayin da huldar da ke tsakanin Sin da kasashen Afirka ke dada bunkasa, karin kasashe na mai da hankalinsu a kan Afirka, hakan ya sa kasar Sin matukar farin ciki. Kasar Sin na maraba da kasa da kasa da su kara ba wa kasashen Afirka goyon baya da kuma taimaka musu, sabo da ci gaban dan Adam ba ya iya rabuwa da ci gaban kasashen Afirka, kuma idan ba a kai ga zamanintar da kasashen Afirka ba, to, ba maganar zamanintarwar duniya ke nan.(Lubabatu Lei)

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin: Ya Kamata Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Da Afirka Ta Kasance Cikin Adalci, Daidaito Kuma A Bayyane

Next Post

Ambaliya: Fursunoni 200 Sun Tsere Daga Gidan Yari A Maiduguri

Related

Girman Kai Da Son Zuciya Ba Za Su Sa A Amince Ko Ba Da Hadin Kai Ba
Ra'ayi Riga

Girman Kai Da Son Zuciya Ba Za Su Sa A Amince Ko Ba Da Hadin Kai Ba

10 hours ago
“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai
Ra'ayi Riga

“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

4 days ago
Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin

5 days ago
Rawar Ganin Da BRICS Ke Takawa Wajen Samar Wa Kasashe Masu Tasowa ‘Yanci A Tsarin Gudanar Da Harkokin Kasa Da Kasa
Ra'ayi Riga

Rawar Ganin Da BRICS Ke Takawa Wajen Samar Wa Kasashe Masu Tasowa ‘Yanci A Tsarin Gudanar Da Harkokin Kasa Da Kasa

7 days ago
Kayayyakin Sin Na Kara Samun Karbuwa A Kasuwar Duniya
Ra'ayi Riga

Kayayyakin Sin Na Kara Samun Karbuwa A Kasuwar Duniya

2 weeks ago
Dutsen Da Amurka Ta Jefa Ya Fado Kasa
Ra'ayi Riga

Dutsen Da Amurka Ta Jefa Ya Fado Kasa

2 weeks ago
Next Post
Ambaliya: Fursunoni 200 Sun Tsere Daga Gidan Yari A Maiduguri

Ambaliya: Fursunoni 200 Sun Tsere Daga Gidan Yari A Maiduguri

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Yi Nasarar Harba Kumbon Dakon Kaya Na Tianzhou-9

Sin Ta Yi Nasarar Harba Kumbon Dakon Kaya Na Tianzhou-9

July 15, 2025
Ƙungiyar Buzaye Ta Yi Wa Nijeriya Ta’aziyyar Rasuwar Muhammadu Buhari

Ƙungiyar Buzaye Ta Yi Wa Nijeriya Ta’aziyyar Rasuwar Muhammadu Buhari

July 15, 2025
VFS Ta Ƙaddamar Da Cibiyar Yin Biza Zuwa Birtaniya A Kano

VFS Ta Ƙaddamar Da Cibiyar Yin Biza Zuwa Birtaniya A Kano

July 15, 2025
Xi Ya Gana Da Shugabannin Tawagogin Kasa Da Kasa Masu Halartar Taron SCO

Xi Ya Gana Da Shugabannin Tawagogin Kasa Da Kasa Masu Halartar Taron SCO

July 15, 2025
An Gudanar Da Taro Game Da Sana’ar Sarrafa Sinadarai Na Kasa Da Kasa Karo Na 12 A Beijing

An Gudanar Da Taro Game Da Sana’ar Sarrafa Sinadarai Na Kasa Da Kasa Karo Na 12 A Beijing

July 15, 2025
Yawan Karuwar GDPn Sin A Rabin Farkon Bana Ya Kai 5.3%

Yawan Karuwar GDPn Sin A Rabin Farkon Bana Ya Kai 5.3%

July 15, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 20, Sun Ƙona Gidaje A Ƙauyukan Filato

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 20, Sun Ƙona Gidaje A Ƙauyukan Filato

July 15, 2025
Shugaba Xi Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Game Da Aikin Raya Birane 

Shugaba Xi Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Game Da Aikin Raya Birane 

July 15, 2025
Ƴansanda Sun Cafke Mutane Biyu Bisa Zargin Kashe Ɗan Ƙasar China

Ƴansanda Sun Cafke Mutane Biyu Bisa Zargin Kashe Ɗan Ƙasar China

July 15, 2025
Taron Matasan Sin Da Afrika Kan Tsaro Zai Kirkiro Wata Sabuwar Mahanga Ta Magance Matsalolin Tsaro

Taron Matasan Sin Da Afrika Kan Tsaro Zai Kirkiro Wata Sabuwar Mahanga Ta Magance Matsalolin Tsaro

July 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.