• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hadin Kan Sin Da Afrika A Bangaren Kiwon Lafiya Zai Ci Gaba Da Samun Nasarori

by Sulaiman and CGTN Hausa
9 months ago
in Ra'ayi Riga
0
Hadin Kan Sin Da Afrika A Bangaren Kiwon Lafiya Zai Ci Gaba Da Samun Nasarori
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

“Da na bude kofa da safe, sai na ga (maras lafiya)sun yi dogon layi suna jira, don neman samun tallafin kiwon lafiya daga wajenmu, abin da ya bayyana amincewarsu da ni da kuma tawagar likitoci da Sin ta tura musu.” Malama Zhang Youming mai shekaru 91 da haihuwa ce ta gaya min haka yayin da na ziyarce ta a birnin Changsha na tsakiyar kasar Sin a kwanan baya. Ta nuna min wani hoto, ta yi murmurshi ta waiwayi abubuwan da suka faru shekaru 60 da suka gabata, yayin da take ba da taimakon kiwon lafiya a Aljeriya.

 

A shekarar 1963, jim kadan bayan kasar Aljeriya ta samu ‘yancin kai bayan yake-yake na tsawon shekaru 10, tsarin kiwon lafiyarta ya fuskanci kalubale matuka, don haka gwamnatin kasar ta yi kira ga kasashen duniya da su ba ta taimako. Nan da nan kasar Sin ta tura wata tawagar likitocinta mai mambobi 13 zuwa kasar. A matsayin likita mai kula da mata da mata masu juna biyu Zhang Youming tana daya daga cikinsu. To, daga wannan lokaci, a karon farko tawagar likitocin kasar Sin ta fara gudanar da aiki a Afrika. A cikin wa’adin aikinta na tsawon shekaru 2 da rabi, Zhang Youming ta yi tiyata fiye da sau dubu. Zhang ta tuna da cewa, akwai wata mace mai juna biyu da ta shiga mawuyancin hali yayin haihuwa, daga bisani ta haifi jaririnta lami lafiya karkashin kulawarta, lamarin da ya sa wannan mace ta radawa danta suna “Basine”, saboda tana ganin cewa, likitar Sin ce ta ceci rayuwarta da ta danta.

  • Shugaban Kasar Sin Ya Bukaci A Daukaka Ra’ayin Gurguzu Mai Sigar Kasar Sin Yayin Da Deng Xiaoping Ke Cika Shekaru 120 Da Zuwa Duniya
  • Huawei Ya Kaddamar Da Horo Game Da Tsaron Yanar Gizo Ga Jami’an Zimbabwe

Tun daga shekarar 1963, likitoci masu dimbin yawa kamar Zhang Youming sun taba ko suna aiki a kasashen Afrika, sun yi kokarin samar da gudummawar jinya har wasunsu sun sadaukar da rayukansu.

 

Labarai Masu Nasaba

A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

Bil’Adama Zai Iya Tabbatar Da Kyakkyawar Makoma Ne Kadai Idan Ya Rike Tarihi A Zuci

Bangaren kiwo lafiya wani muhimmin bangare ne na hadin gwiwar Sin da Afrika. Kuma turawa kasashen Afrika tawagogin ba da tallafin kiwon lafiya, wani sashi ne na hadin gwiwar Sin da Afrika a bangaren kiwon lafiya. Ban da wannan kuma, Sin ta taimaka wajen aiwatar da shirye-shiryen kiwon lafiya 25 a Afirka, ciki hadda hedkwatar cibiyar magance cututuka masu yaduwa ta Afrika ta AU, da asibitin Bobo-Dioulasso na Burkina Faso da dai sauransu. Kazalika ta samarwa kasashen Afrika tallafin alluran rigakafi kimanin miliyan 240, matakin da ya taimakawa kasashen dake da bukata wajen samun isassun alluran.

 

Bisa kokarin da likitocin Sin suke ta yi, ba shakka, zumunci a tsakanin Sin da kasashen Afirka na ta karfafa. Hadin gwiwar bangarorin biyu ta fuskar kiwon lafiya zai ci gaba da samun nasarori a nan gaba, duba da cewa suna kokarin kafa kyakkyawar makomarsu ta bai daya a wannan bangare. (Mai zane da rubutu: MINA)

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Ta Zama Zakaran Gwajin Dafi A Fannin Goyon Bayan Zaman Lafiya Da Adalci Tsakanin Kasashen Duniya

Next Post

Binciken LEADERSHIP Hausa… Asalin Abin Da Ya Faru Da Iyalan Da Suka Mutu Sanadin Gurbataccen Abinci

Related

A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka
Ra'ayi Riga

A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

14 hours ago
Bil’Adama Zai Iya Tabbatar Da Kyakkyawar Makoma Ne Kadai Idan Ya Rike Tarihi A Zuci
Ra'ayi Riga

Bil’Adama Zai Iya Tabbatar Da Kyakkyawar Makoma Ne Kadai Idan Ya Rike Tarihi A Zuci

4 days ago
Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta
Ra'ayi Riga

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

6 days ago
Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?

6 days ago
Tattalin Arzikin Sin Tamkar Teku Ne Ba Karamin Tabki Ba
Ra'ayi Riga

Tattalin Arzikin Sin Tamkar Teku Ne Ba Karamin Tabki Ba

1 week ago
Karin Wata Kasa Da Bai San Ta Ba A Doron Duniya
Ra'ayi Riga

Karin Wata Kasa Da Bai San Ta Ba A Doron Duniya

2 weeks ago
Next Post
Binciken LEADERSHIP Hausa… Asalin Abin Da Ya Faru Da Iyalan Da Suka Mutu Sanadin Gurbataccen Abinci

Binciken LEADERSHIP Hausa… Asalin Abin Da Ya Faru Da Iyalan Da Suka Mutu Sanadin Gurbataccen Abinci

LABARAI MASU NASABA

UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.