• English
  • Business News
Friday, October 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hadin Kan Sin Da Afrika A Bangaren Kiwon Lafiya Zai Ci Gaba Da Samun Nasarori

by Sulaiman and CGTN Hausa
1 year ago
Sin

“Da na bude kofa da safe, sai na ga (maras lafiya)sun yi dogon layi suna jira, don neman samun tallafin kiwon lafiya daga wajenmu, abin da ya bayyana amincewarsu da ni da kuma tawagar likitoci da Sin ta tura musu.” Malama Zhang Youming mai shekaru 91 da haihuwa ce ta gaya min haka yayin da na ziyarce ta a birnin Changsha na tsakiyar kasar Sin a kwanan baya. Ta nuna min wani hoto, ta yi murmurshi ta waiwayi abubuwan da suka faru shekaru 60 da suka gabata, yayin da take ba da taimakon kiwon lafiya a Aljeriya.

 

A shekarar 1963, jim kadan bayan kasar Aljeriya ta samu ‘yancin kai bayan yake-yake na tsawon shekaru 10, tsarin kiwon lafiyarta ya fuskanci kalubale matuka, don haka gwamnatin kasar ta yi kira ga kasashen duniya da su ba ta taimako. Nan da nan kasar Sin ta tura wata tawagar likitocinta mai mambobi 13 zuwa kasar. A matsayin likita mai kula da mata da mata masu juna biyu Zhang Youming tana daya daga cikinsu. To, daga wannan lokaci, a karon farko tawagar likitocin kasar Sin ta fara gudanar da aiki a Afrika. A cikin wa’adin aikinta na tsawon shekaru 2 da rabi, Zhang Youming ta yi tiyata fiye da sau dubu. Zhang ta tuna da cewa, akwai wata mace mai juna biyu da ta shiga mawuyancin hali yayin haihuwa, daga bisani ta haifi jaririnta lami lafiya karkashin kulawarta, lamarin da ya sa wannan mace ta radawa danta suna “Basine”, saboda tana ganin cewa, likitar Sin ce ta ceci rayuwarta da ta danta.

  • Shugaban Kasar Sin Ya Bukaci A Daukaka Ra’ayin Gurguzu Mai Sigar Kasar Sin Yayin Da Deng Xiaoping Ke Cika Shekaru 120 Da Zuwa Duniya
  • Huawei Ya Kaddamar Da Horo Game Da Tsaron Yanar Gizo Ga Jami’an Zimbabwe

Tun daga shekarar 1963, likitoci masu dimbin yawa kamar Zhang Youming sun taba ko suna aiki a kasashen Afrika, sun yi kokarin samar da gudummawar jinya har wasunsu sun sadaukar da rayukansu.

 

LABARAI MASU NASABA

Harkokin Ciniki Da Zuba Jari Tsakanin Sin Da Afirka Sun Samu Ci Gaba Mafi Girma a Shekaru 5 Da Suka Gabata

Sanarwar Bayan Taron Jks: Mene Ne Sirrin Kwarin Gwiwar Kasar Sin?

Bangaren kiwo lafiya wani muhimmin bangare ne na hadin gwiwar Sin da Afrika. Kuma turawa kasashen Afrika tawagogin ba da tallafin kiwon lafiya, wani sashi ne na hadin gwiwar Sin da Afrika a bangaren kiwon lafiya. Ban da wannan kuma, Sin ta taimaka wajen aiwatar da shirye-shiryen kiwon lafiya 25 a Afirka, ciki hadda hedkwatar cibiyar magance cututuka masu yaduwa ta Afrika ta AU, da asibitin Bobo-Dioulasso na Burkina Faso da dai sauransu. Kazalika ta samarwa kasashen Afrika tallafin alluran rigakafi kimanin miliyan 240, matakin da ya taimakawa kasashen dake da bukata wajen samun isassun alluran.

 

Bisa kokarin da likitocin Sin suke ta yi, ba shakka, zumunci a tsakanin Sin da kasashen Afirka na ta karfafa. Hadin gwiwar bangarorin biyu ta fuskar kiwon lafiya zai ci gaba da samun nasarori a nan gaba, duba da cewa suna kokarin kafa kyakkyawar makomarsu ta bai daya a wannan bangare. (Mai zane da rubutu: MINA)

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Harkokin Ciniki Da Zuba Jari Tsakanin Sin Da Afirka Sun Samu Ci Gaba Mafi Girma a Shekaru 5 Da Suka Gabata
Ra'ayi Riga

Harkokin Ciniki Da Zuba Jari Tsakanin Sin Da Afirka Sun Samu Ci Gaba Mafi Girma a Shekaru 5 Da Suka Gabata

October 23, 2025
Sanarwar Bayan Taron Jks: Mene Ne Sirrin Kwarin Gwiwar Kasar Sin?
Ra'ayi Riga

Sanarwar Bayan Taron Jks: Mene Ne Sirrin Kwarin Gwiwar Kasar Sin?

October 23, 2025
Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Kasar Sin Na Saurin Bunkasa
Ra'ayi Riga

Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Kasar Sin Na Saurin Bunkasa

October 21, 2025
Next Post
Binciken LEADERSHIP Hausa… Asalin Abin Da Ya Faru Da Iyalan Da Suka Mutu Sanadin Gurbataccen Abinci

Binciken LEADERSHIP Hausa… Asalin Abin Da Ya Faru Da Iyalan Da Suka Mutu Sanadin Gurbataccen Abinci

LABARAI MASU NASABA

Nnamdi Kanu Ya Sake Bayyana A Kotu Ba Tare Da Lauya Ba, Zai Kare Kansa Da Kansa

Nnamdi Kanu Ya Sake Bayyana A Kotu Ba Tare Da Lauya Ba, Zai Kare Kansa Da Kansa

October 24, 2025
Uba Sani Ya Amince Da Biyan Naira Biliyan ₦2.3 Ga Tsofaffin Ma’aikata Da Iyalansu

Ƙungiyoyin Ma’aikatan Jihar Kaduna Sun Yabawa Gwamna Sani Kan Amincewa Da Sabon Albashin  Ma’aikata

October 24, 2025
Ƙarfin Niyyar Manzon Allah (SAW) Da Matakinsa Na Aƙlul A’ala

Ƙarfin Niyyar Manzon Allah (SAW) Da Matakinsa Na Aƙlul A’ala

October 24, 2025
Gobara Ta Tafka Ɓarna A Kasuwar Shuwaki, Ta Ƙona Fiye da Rumfuna 500 A Kano

Gobara Ta Tafka Ɓarna A Kasuwar Shuwaki, Ta Ƙona Fiye da Rumfuna 500 A Kano

October 24, 2025
Gwarzuwar Shekarar 2025 Sanata Oluremi Tinubu

Gwarzuwar Shekarar 2025 Sanata Oluremi Tinubu

October 24, 2025
Dauda Lawal Gwarzon Gwamnan 2025: Ceto Zamfara Domin Ci Gaba

Dauda Lawal Gwarzon Gwamnan 2025: Ceto Zamfara Domin Ci Gaba

October 24, 2025
Buƙatar Daƙile Badaƙalar Amfani Da Takardun Karatun Bogi A Nijeriya

Buƙatar Daƙile Badaƙalar Amfani Da Takardun Karatun Bogi A Nijeriya

October 24, 2025
Fahimtar Sabon Tunani: Samar Da Wadata Ga Dukkan Jama’a Ta Daidaita Gibin Dake Tsakanin Hamshakai Da Matalauta

Fahimtar Sabon Tunani: Samar Da Wadata Ga Dukkan Jama’a Ta Daidaita Gibin Dake Tsakanin Hamshakai Da Matalauta

October 23, 2025
Shugaban Senegal: Kasar Sin Ta Zama Abin Koyi Ga Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Senegal: Kasar Sin Ta Zama Abin Koyi Ga Kasashe Masu Tasowa

October 23, 2025
Sojoji Sun Kashe Mayakan Boko Haram 6, Sun Kama Wasu A Borno

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 50, Sun Daƙile Hare-Hare A Borno

October 23, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.