ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hadin Kan Sin Da Afrika A Bangaren Kiwon Lafiya Zai Ci Gaba Da Samun Nasarori

by Sulaiman and CGTN Hausa
2 years ago
Sin

“Da na bude kofa da safe, sai na ga (maras lafiya)sun yi dogon layi suna jira, don neman samun tallafin kiwon lafiya daga wajenmu, abin da ya bayyana amincewarsu da ni da kuma tawagar likitoci da Sin ta tura musu.” Malama Zhang Youming mai shekaru 91 da haihuwa ce ta gaya min haka yayin da na ziyarce ta a birnin Changsha na tsakiyar kasar Sin a kwanan baya. Ta nuna min wani hoto, ta yi murmurshi ta waiwayi abubuwan da suka faru shekaru 60 da suka gabata, yayin da take ba da taimakon kiwon lafiya a Aljeriya.

 

A shekarar 1963, jim kadan bayan kasar Aljeriya ta samu ‘yancin kai bayan yake-yake na tsawon shekaru 10, tsarin kiwon lafiyarta ya fuskanci kalubale matuka, don haka gwamnatin kasar ta yi kira ga kasashen duniya da su ba ta taimako. Nan da nan kasar Sin ta tura wata tawagar likitocinta mai mambobi 13 zuwa kasar. A matsayin likita mai kula da mata da mata masu juna biyu Zhang Youming tana daya daga cikinsu. To, daga wannan lokaci, a karon farko tawagar likitocin kasar Sin ta fara gudanar da aiki a Afrika. A cikin wa’adin aikinta na tsawon shekaru 2 da rabi, Zhang Youming ta yi tiyata fiye da sau dubu. Zhang ta tuna da cewa, akwai wata mace mai juna biyu da ta shiga mawuyancin hali yayin haihuwa, daga bisani ta haifi jaririnta lami lafiya karkashin kulawarta, lamarin da ya sa wannan mace ta radawa danta suna “Basine”, saboda tana ganin cewa, likitar Sin ce ta ceci rayuwarta da ta danta.

ADVERTISEMENT
  • Shugaban Kasar Sin Ya Bukaci A Daukaka Ra’ayin Gurguzu Mai Sigar Kasar Sin Yayin Da Deng Xiaoping Ke Cika Shekaru 120 Da Zuwa Duniya
  • Huawei Ya Kaddamar Da Horo Game Da Tsaron Yanar Gizo Ga Jami’an Zimbabwe

Tun daga shekarar 1963, likitoci masu dimbin yawa kamar Zhang Youming sun taba ko suna aiki a kasashen Afrika, sun yi kokarin samar da gudummawar jinya har wasunsu sun sadaukar da rayukansu.

 

LABARAI MASU NASABA

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta

Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin

Bangaren kiwo lafiya wani muhimmin bangare ne na hadin gwiwar Sin da Afrika. Kuma turawa kasashen Afrika tawagogin ba da tallafin kiwon lafiya, wani sashi ne na hadin gwiwar Sin da Afrika a bangaren kiwon lafiya. Ban da wannan kuma, Sin ta taimaka wajen aiwatar da shirye-shiryen kiwon lafiya 25 a Afirka, ciki hadda hedkwatar cibiyar magance cututuka masu yaduwa ta Afrika ta AU, da asibitin Bobo-Dioulasso na Burkina Faso da dai sauransu. Kazalika ta samarwa kasashen Afrika tallafin alluran rigakafi kimanin miliyan 240, matakin da ya taimakawa kasashen dake da bukata wajen samun isassun alluran.

 

Bisa kokarin da likitocin Sin suke ta yi, ba shakka, zumunci a tsakanin Sin da kasashen Afirka na ta karfafa. Hadin gwiwar bangarorin biyu ta fuskar kiwon lafiya zai ci gaba da samun nasarori a nan gaba, duba da cewa suna kokarin kafa kyakkyawar makomarsu ta bai daya a wannan bangare. (Mai zane da rubutu: MINA)

 

Sin
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • Sulaiman
    ‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna
Sin
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

MASU ALAKA

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta
Ra'ayi Riga

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta

September 8, 2026
Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin

September 4, 2026
Samun Rarar Kudin Ciniki Ba “Laifi” Ba Ne, Hadin Gwiwa Da Cin Moriya Tare Ita Ce Mafita Ga Kowa
Ra'ayi Riga

Samun Rarar Kudin Ciniki Ba “Laifi” Ba Ne, Hadin Gwiwa Da Cin Moriya Tare Ita Ce Mafita Ga Kowa

September 2, 2026
Next Post
Binciken LEADERSHIP Hausa… Asalin Abin Da Ya Faru Da Iyalan Da Suka Mutu Sanadin Gurbataccen Abinci

Binciken LEADERSHIP Hausa… Asalin Abin Da Ya Faru Da Iyalan Da Suka Mutu Sanadin Gurbataccen Abinci

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.