ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hadin Kan Sin Da Afrika A Bangaren Kiwon Lafiya Zai Ci Gaba Da Samun Nasarori

by Sulaiman and CGTN Hausa
2 years ago
Sin

“Da na bude kofa da safe, sai na ga (maras lafiya)sun yi dogon layi suna jira, don neman samun tallafin kiwon lafiya daga wajenmu, abin da ya bayyana amincewarsu da ni da kuma tawagar likitoci da Sin ta tura musu.” Malama Zhang Youming mai shekaru 91 da haihuwa ce ta gaya min haka yayin da na ziyarce ta a birnin Changsha na tsakiyar kasar Sin a kwanan baya. Ta nuna min wani hoto, ta yi murmurshi ta waiwayi abubuwan da suka faru shekaru 60 da suka gabata, yayin da take ba da taimakon kiwon lafiya a Aljeriya.

 

A shekarar 1963, jim kadan bayan kasar Aljeriya ta samu ‘yancin kai bayan yake-yake na tsawon shekaru 10, tsarin kiwon lafiyarta ya fuskanci kalubale matuka, don haka gwamnatin kasar ta yi kira ga kasashen duniya da su ba ta taimako. Nan da nan kasar Sin ta tura wata tawagar likitocinta mai mambobi 13 zuwa kasar. A matsayin likita mai kula da mata da mata masu juna biyu Zhang Youming tana daya daga cikinsu. To, daga wannan lokaci, a karon farko tawagar likitocin kasar Sin ta fara gudanar da aiki a Afrika. A cikin wa’adin aikinta na tsawon shekaru 2 da rabi, Zhang Youming ta yi tiyata fiye da sau dubu. Zhang ta tuna da cewa, akwai wata mace mai juna biyu da ta shiga mawuyancin hali yayin haihuwa, daga bisani ta haifi jaririnta lami lafiya karkashin kulawarta, lamarin da ya sa wannan mace ta radawa danta suna “Basine”, saboda tana ganin cewa, likitar Sin ce ta ceci rayuwarta da ta danta.

ADVERTISEMENT
  • Shugaban Kasar Sin Ya Bukaci A Daukaka Ra’ayin Gurguzu Mai Sigar Kasar Sin Yayin Da Deng Xiaoping Ke Cika Shekaru 120 Da Zuwa Duniya
  • Huawei Ya Kaddamar Da Horo Game Da Tsaron Yanar Gizo Ga Jami’an Zimbabwe

Tun daga shekarar 1963, likitoci masu dimbin yawa kamar Zhang Youming sun taba ko suna aiki a kasashen Afrika, sun yi kokarin samar da gudummawar jinya har wasunsu sun sadaukar da rayukansu.

 

LABARAI MASU NASABA

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

Bangaren kiwo lafiya wani muhimmin bangare ne na hadin gwiwar Sin da Afrika. Kuma turawa kasashen Afrika tawagogin ba da tallafin kiwon lafiya, wani sashi ne na hadin gwiwar Sin da Afrika a bangaren kiwon lafiya. Ban da wannan kuma, Sin ta taimaka wajen aiwatar da shirye-shiryen kiwon lafiya 25 a Afirka, ciki hadda hedkwatar cibiyar magance cututuka masu yaduwa ta Afrika ta AU, da asibitin Bobo-Dioulasso na Burkina Faso da dai sauransu. Kazalika ta samarwa kasashen Afrika tallafin alluran rigakafi kimanin miliyan 240, matakin da ya taimakawa kasashen dake da bukata wajen samun isassun alluran.

 

Bisa kokarin da likitocin Sin suke ta yi, ba shakka, zumunci a tsakanin Sin da kasashen Afirka na ta karfafa. Hadin gwiwar bangarorin biyu ta fuskar kiwon lafiya zai ci gaba da samun nasarori a nan gaba, duba da cewa suna kokarin kafa kyakkyawar makomarsu ta bai daya a wannan bangare. (Mai zane da rubutu: MINA)

 

Sin
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta
  • Sulaiman
    Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
  • Sulaiman
    Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa
Sin
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

MASU ALAKA

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka
Ra'ayi Riga

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

July 10, 2026
Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?

July 9, 2026
Next Post
Binciken LEADERSHIP Hausa… Asalin Abin Da Ya Faru Da Iyalan Da Suka Mutu Sanadin Gurbataccen Abinci

Binciken LEADERSHIP Hausa… Asalin Abin Da Ya Faru Da Iyalan Da Suka Mutu Sanadin Gurbataccen Abinci

LABARAI MASU NASABA

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.