• English
  • Business News
Saturday, August 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hadurran Jirgin Sama 10 Da Suka Girgiza Nijeriya (I)

by Idris Aliyu Daudawa
2 years ago
in Tarihi
0
Hadurran Jirgin Sama 10 Da Suka Girgiza Nijeriya (I)
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Haruddan jirgin sama sun sha faruwa a Nijeriya inda suka yi sanadiyar mutuwar mutane da yawa, a cikinsu ga goma wadanda suka fi muni.

  1. Ranar 20 ga Nuwamba 1969 mutane 87 suka rasa rayukansu a hadarin jirgin sama na Bickers BC-10 wanda ya fadi a Legas Nijeriya.BC-10 ya taso ne daga Landan zuwa Legas inda ya yada zango Rome da Kano.Lokacin da ya kusa isowa Legas sai jirgin ya yi kasa sosai ba kamar yadda aka saba ba ya bugi itace wanda hakan ya sa ya fadi ya kama da wuta.
  2. Ranar 22 ga Janairu 1973 jirgin sama mai kirar Boeing 707 wanda hukumar jiragen sama ta Nijeriya ta ba shi aiki domin ya maido da Alhazai daga Jidda zuwa Legas ya fadi a Kano ya kashe mutane 176.

Saboda rashi kyawon yanayi a Legas sai aka juya akalar jirgin zuwa Kano.Ya yi yunkurin sauka a titin da jirage ke bi domin sauka amma sai aka samu matsala sai an yi sa’ar ceto ma’aikata biyu da fasinjoji 23 da ransu.

3.11 ga watan Yuli 1991 mutane 261 sun rasa rayukansu lokacin da jirgin sama na McDonnell-Douglas DC-8 da yake dawowa da Alhazan Sakkwato da aikin Hajji a madadin tsohuwar hukumar kula da jiragen sama ta kasa ya fadi a Jeddah, Saudi Arebiya,shine hadari mafi muni  a tarihin hadarin jirgin sama a Nijeriya.

Jirgin saman Nijeriya ya taso daga Jedda amma bayan tasowar tsakanin kafa 2000-3000, sai aka samu matsala wadda ma’aikata suka bayyana.

An dauki mataki ba tare da bata lokaci ba sai dai bai hana abin da zai faru ya auku ba domin kuwa an samu matsalar birki wadda ta sa jirgin ya rasa irin halin da yake ciki sai ya fadi ya kama da wuta lokacin da yake kokarin dawowa.Shine hadarin jirgi mafi muni wanda ya shafi jirgin sama mai kirar DC-8 shine kuma hadari na biyu da ya faru a Saudi Arebiya a wancan lokacin.Matsalar da tasa hadarin an dora ta akan kuskure na mutum a hukumar kula da harkokin jiragen sama.

Labarai Masu Nasaba

Dalilan Da Suka Sa Cinikin Bayi Bai Yi Nasara A Arewacin Nijeriya Ba

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (6)

  1. Ranar 26 ga Satumba 1992 mutane 158 suka mutu wadanda suke cikin jirgin Lockheed C-130H Hercules wanda sojojin saman a kasa ke amfani da shi ya fadi kusa da Legas.

Bayan jirgin ya tashi sai inji na farko ya lalace daganan sai na biyu shi ma ya biyo sahu bada dadewa ba.Ma’aikatan jirgin sun yi kokari su maida akalar jirgin zuwa Ejigbo amma sai inji na uku shi ma ya daina aiki.

Daga karshe dai jirgin ya fada a wurin da ruwa yake mai tabo ba a san ko mutane nawa bane suka mutu.Akwai ‘yan Nijeriya a kalla 150, ‘yan kasar Ghana 5,dan kasar Tanzaniya 1, dan Zimbabwean 1, da kuma dan  Uganda 1 a cikin hadarin.

  1. Ranar 7 ga Nuwamba 1996 jimillar mutane 144 sun mutu bayan jirgin sama na Boeing 727 da kamfanin jirgin sama na ADC ke amfani da shi ya taso daga Fatakwal zukka Legas ya fadi a Ejirin a inda duk mutanen da ke cikin jirgin suka mutu.

Za mu ci gaba a mako mai zuwa


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Gasasshen Nama Mai Dankali

Next Post

Sada Zumunci Da Abubuwan Da Ke Yanke Shi A Zamanin Nan

Related

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (6)
Tarihi

Dalilan Da Suka Sa Cinikin Bayi Bai Yi Nasara A Arewacin Nijeriya Ba

4 weeks ago
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (6)
Tarihi

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (6)

1 month ago
Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (1)
Tarihi

Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (1)

2 months ago
Tarihin Shugaannin Kasar Mali Na Farko A Daular Songhai (8)
Tarihi

Tarihin Shugaannin Kasar Mali Na Farko A Daular Songhai (8)

5 months ago
Tarihin Shugaban Ƙasar Mali Na Farko Sundiata Keita (2)
Tarihi

Tarihin Shugabannin Ƙasar Mali Na Farko A Daular Songhai (7)

5 months ago
A-Ula: Dadadden Birni Mai Cike Da Dinbin Tarihi Da Al’adu
Tarihi

A-Ula: Dadadden Birni Mai Cike Da Dinbin Tarihi Da Al’adu

10 months ago
Next Post
Sada Zumunci Da Abubuwan Da Ke Yanke Shi A Zamanin Nan

Sada Zumunci Da Abubuwan Da Ke Yanke Shi A Zamanin Nan

LABARAI MASU NASABA

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

August 22, 2025
UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

August 22, 2025
Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

August 22, 2025
Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

August 22, 2025
JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

August 22, 2025
Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

August 22, 2025
Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

August 22, 2025
Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

August 22, 2025
Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025

Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025

August 22, 2025
Ruben Dias Ya Rattaba Hannu Kan Sabon Kwantiragi A Manchester City

Ruben Dias Ya Rattaba Hannu Kan Sabon Kwantiragi A Manchester City

August 22, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.